ABDUL JALAL PART 2

Tofa!
Masoya kaunar da nake kumu tasa nai muku dogon page gashi nan, senaji Comments dinku love you all
????????????????❤️❤️❤️????????????????
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680.
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????
(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P.W.A✍️
PART 2
_PAGE 4️⃣3️⃣96
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Juyawa tayi ta fice da sauri tana goge hawaye, Ilham dataga duk abunda yafaru tayi wani tsallen farinciki, amma da tuna irin tonon sililin da Jalal yayi mata dazu se taji jikinta yayi sanyi ta juya da sauri ta koma gida.
Jalal bashida zabi da ya wuce ya bar gurin shima kamar wanda kwai ya fashewa a ciki yakoma part dinsa, zuciyarsa kaman an kunna masa wuta saboda bacin rai, side bed dinsa ya kalla yaga Alqur’anin nan da kuma teddyn Jalila a gurin, a hankali yace
“do she really mean what she said, zata barni gaba daya, bani ba ita? Jalila why? karkimin haka mana, nasan ba’a kyauta miki ba, Amma kar laifin Mummy ya shafeni”
ya zauna a gefen gadon sa ya rintse ido, ya dinga tuno moments dinsu tare, da fitar da sukayi dazu, ji yayi kansa yana juyawa zuciyarsa ta masa nauyi, ya kunna sigari yafara sha, ya sha takai kara biyar amma beji yadda yakeso ba seda ya dakko merlot red wine ya sha ya fita daga hayyacinsa sannan ya yada kwalbar a gurin shima ya zube.
Ita kuwa Jalila seda ta samu guri a cikin flowers tayi kukanta ta gode Allah sannan ta nufi palourn gidan, tunda ta shiga ita dai taji Abba yana bayani yayinda Yaya mairo keta haya gaga, sam Jalila bata gane me suke fada danji take kaman zata fadi ta wucesu ta shige daki ba tareda ta kula kowa ba, tana zuwa ta haye gado ta ja blanket ta cigaba da kuka da kuma tunani, shikenan yanzu kuma kallon mazinaciya mahaifiyar Jalal take mata? Gaskiya tsakanin ta da Ilham se Allah yasaka mata, amma ba komai zata rama ne, zatayi wa Ilham daurin da bata isa ta kwance ba”
Jawwad ya farka daga baccin dayake cike da farinciki ya tashi yayi salla, sannan ya nufi cikin gida dan ganin Maama dakuma ‘yan kannensa dan yasan zuwa yanzu sun dawo daga school. Yana fitowa manu direba ya shigo harabar gidan da mota, ya jira manu yayi parking Nana ta fito daga motar kallo daya zakayi mata kasan a gajiye take, se jefa kafa take kawai tana ganin Yaya Jawwad ta yalwata murmushinta tareda fadin “Oyoyo mutan Bauchi, Ashe kun dawo?”
“Mun dawo Nana, ya school din? Naganki ke kadai ina Jalila?”
“Yaya Jawwad kasan Jalila manyan kwarine, yau bataje school ba, amma ancemin angan ta dazu ta shiga zasuyi test”
“Shikenan mukarasa ciki, yau Akwai Albishir masu dadin gaske, muje in gaida Maama tukuna” suka jero tare zuwa cikin gida.
Abba yace “Hajiya mairo ban yanke wannan hukuncin dan cin mutuncin ki kona zuriyarki ba, sedai dan hakan shine masalaha ga yarona, idan baki saniba yaka mata kikara sa ido da bincike akan yaranki, Amma dana san haka abun yake, da tunda fari ban yadda da batun hada Auren nan ba, nasamawa Jawwad wata yarinyar itama Naja, taje Allah ya hadata da rabonta dan binciken danayi akanta gaskiya bazan iya bari Jawwad ya aureta ba”
Yaya mairo tace “dama dai can ka shirya cin mutuncina nida yarinya ta, amma inda arziki da mutuci ita daudar gora ai a ciki ake shanyeta, koma me take aikatawa silar Auren ai sekaga ta shiryu”
“Hajiya Mairo, da abunda ze yuwu ne da na hakura anyi auren nan amma baze yuwu ba, kuyi hakuri, sannan Naja ta koma gidan mahaifinta ta zauna”
Maama da tun dazu batayi magana ba tace
“Dan girman Allah kayi hakuri mun yadda ya auresu su biyu ma bakomai, amma idan akayi haka kaman amci mutuncin gidanmune”
Abba yace
“Ni ban Janye batun Auren nan dan cin mutuncin wani ba, amma da abunda ze yuwu ne dana hakura anyi, zanje in samu mahaifinta muyi maganar, dan ba dake ma yakamata muyi wannan zancen ba”
Naja kam se rusa uban kuka takeyi
“Dan Allah ku kyale masa dansu, sekace shi kadaine namiji, kokuma mijin gold ne? Banda kaddara me zatayi da wani Jawwad mutum sam be waye ba waishi Ustaz, dalla kidena kuka kiyi rayuwar ki kamar kowa, ki manta dashi”
Sa’adah ce ke wannan maganar cikin fitsara da rashin kunya, Abba ya mike yana kokarin bar musu palourn su Jawwad suka shigo jin hayaniya yasa
Jawwad yace “Abba lafiya kuwa?”
“Rufe mana baki kasurgumin munafiki daga kai har ubannaka da waccan makirar jarababbiyar, kun shiga kunfita kafasa Auren yarinyata dan ku kunya tamu a duniya to ta Allah ba taku ba, Matsiyatan banza dana wofi hadda wai tabar gidan nan dadinta tanada gidan uba ba’a titi take kwana ba”
Yaya mairoce ta wangale makogaro taketa zazzaga rashin mutunci san ranta, ta kalli Naja tace
“Jeki kwasomin kayanki mu tafi, Nina gayamiki sekin samu wanda ya fishi, Azzalumai kawai”
Maama ke kokarin kwantarwa da Yaya mairo hankali ta hanyar cewa
“Yaya dan girman Allah kiyi hakuri, zan shawo kan matsalar nan, dan Allah”
Naja tace “ba wani shawo kan matsala, ni bana son karya irin wadda kika saba yi, an kaimin kudi kin lallaba kun hada kai ze auri wata, kuma ana kokarin yimin sharri wallahi Allah ya isa ban yafe ba aikin banza kawai”
A harzuke Jawwad yace
“Wallahi kika kuma zagarmin uwa sena wanka miki mari, baza’a Aureki dinba, waze Auri mace irinki ace itace uwar yaransa, Kika kuma zagarmin iyaye sena bata miki rai”
Aikuwa Yaya mairo tayi kansa ta hanyar cewa
“Rufemin baki mara mutunci, har kanada bakin magana, iyayennaka ba kananan mutane bane, masu baki biyu, matsiyacin ubannaka dan Allah ya bashi Arziki ze wulakanta munida yarana”
A fusace Nana tace “A’a kinga Yaya mairo dakata, ubanmu fa ba sa’anki baneba, Maama ce ‘yar uwakki dan haka kuje kiyi keda ita, da kike kiran ubanmu matsiyaci ya gama muku komai, dawainiyar ku ba wadda baya dauka yayi muku rana, da tsiyar tasa da kike fada ya muku rana ya maganta muku abubuwa dayawa, meye ba’ ayi muku a gidan nan, wani abunma ku sata sann………
“Ke Nana rufemin baki, Yaya mairon Sa’ar kice? Maama ta katse ta,
Jawwad juyawa yayi ya fice, dan a rayuwarsa baya son tashin hankali sam,
Nana tace “Allah sarki Jalila baiwar Allah, dukda abubuwan dakike mata Maama nasan Jalila bazata taba kallon tsabar idonki takira ki da makaryaciya ba, yau sega wanda kikeso din suna zagin ki, dama Allah ai ba Azzalumin sarki bane, musamman Naja tazo gidan nan danta kori Jalila, ga reshe ya juye da mujiya ai, bata kori Jalila ba, bata auri Jawwad ba kuma ita an koreta”
Nana tai wucewarta zuwa daki ta barsu a tsaye cirko2 suna cigaba da masifa.
Nana na shiga dakin ta tarar da Jalila ta kima bargo akanta tanata bacci duk hayaniyar nan baccinta take, Nana ta tatttaro kayan Naja ta fito mata dasu palour ta ajiye,
Tace “ga kayanki nan, daga nan bama bukatar ki a dakinmu”
Ta juya takoma daki tasa key, ta barsu da Maama a gurin.