ABDUL JALAL PART 2

Jawwad sam ransa ba dadi, bangare daya yana cikin farinciki, bangare daya kuma ransa a bace yake ya tafi dakin Jalal domin suyi hira, yagaya masa halinda ake ciki, Amma abun haushin yana zuwa ya tarar da gogan yayi mankas baccin sa kawai yakeyi, dan dafe kai Jawwad yai ya zauna ya tattare kayan shaye2n gefe daya, ya zauna a gefen gadon Jalal, yana kallonsa garin da dan sanyi sanyi ga fanka ga A. C Amma Jalal gaban goshinsa se zufa yake, Jawwad ya dan girgiza kai, tareda fadin
“Allah ya shirye ka dan uwa” sannan yasa hannu ya daddaki pillow da Jalal yake kai, a hankali Jalal ya bude ido ya saukesu akan Jawwad ya mayar ya lumshe idonsa, Jawwad yace
“Jalal ka tashi kai salla” dan karamin tsaki Jalal yayi yace “nika kyaleni please”
“haba Jalal bakayi salla ba, ka daure ka tashi mana”
Juyawa Jawwad baya yayi ya rungume pillow se ya tuna maganar Jalila
“Inkaana Ibada, kana Addu’a Rage wasu Abubuwan”
Sekuma ya danyi juyi ya mike da kyar yaje yai wanka da Alwala yazo ya gabatar da sallar Azahar da la’asar, fuskar nan tasa murtuk kaman be taba dariya ba.
Jawwad ya dinga masa hira yana bashi labarin abubuwan da suka faru a Bauchi, da dramar da aka gama yi a gidansu yanzu, Amma se ya lura sam hankalin Jalal baya kansa yayi zurfafa a tunani ne, lokaci zuwa lokaci ya kanyi tsaki.
Jawwad yace “Jalal wai me yake damunka ne? Ina ta magana hankalin ka baya kaina, se faman tsaki kake, menene?”
Ajiyar zuciya Jalal yayi sannnan yace “Bakomai don’t mind me”
“ban yadda bakomai ba, ka gayamin please”
“Am serious bakomai, kawai yanayin ne bayamun dadi”
“to Allah ya sawwake, Amma Jalal kwana biyu ina ta murna ka dena zuwa club, shaye shayen ma kaman ka dena amma nazo na tarar kasha giya, haba Jalal why”
Dan shiru Jalal yayi dan yanajin muddin baze rabu da wannan damuwar ba akwai yuwuwar yakoma ruwa tsundum, dan maganganun Jalila sunyi matukar tasiri a zuciyarsa, a fili yace
“Am sorry Jawwad, ina bakin kokarina, kasan wani lokacin halinda nake shiga idan ban shaba, Amma Insha Allah very soon zan dena gaba daya”
“to Allah ya amince”
Daga nan Jawwad ya lallaba Jalal ya jashi suka fita zaga gari da nufin ya debe masa kewa.
Seda aka gama wannan tarzomar aka gama su Yaya mairo suka tafi sannan Allah ya nufi Jalila da tashi daga baccin da take, ta kalli Nana tace “Nana meyasa baki tasheni ba? Gaskiya na sha bacci tunda na dawo na kwanta se yanzu na tashi”
Nana tace “Mhmm ke kinta bacci bakisan drama da’akayi ba yau”
“Tame fa?” Jalila ta tambayi Nana irin bata san meyafaru ba,
Nana ta labarta mata komai, Jalila ta jinjina kai ita babban abunda ya bata mata rai be wuce yadda Nana ta gaya mata irin cin mutuncin da suka dingayi wa Abba ba, hatta zagin da sukayi wa Maama yabata mamaki, bata taba zaton zasu yiwa Maama hakaba saboda yadda take kyautata musu.
Nana ta gayawa Jalila cewar tunda Abba ya shige daki da wannan abun yafaru ko Abinci be ciba, ba karamin tausayin Abba ne yakamata ba takara tabattar da Yaya mairo daga ita har Yaranta basuda tarbiyya dan haka Jalila salla kawai tayi ta shiga kitchen ta dora Abincin dare saboda Abba ya samu yaci.
Sunkuma waya da Ahmad ya gaya mata yauma tayi hakuri abubuwa ne sukayi masa yawa shiyasa baze samu zuwa ba, Jalila ta karbi uzurinsa saboda yanayin aikin nasa.
Jalila ta shirya Abinci me rai da lafiya, bayan sallar magariba ta kaiwa Abba nasa har daki, Amma da mamakin ta ta same shi cikin fara’a, yace “‘yar gidan Abba Girki akayi min haka ne?”
“Eh Abba, gashi nan kaci ka koshi sannan inzo inji Albishir din da zakayi min”
Yai murmushi yace “Ai Albishir din bana kine ke kadai ba, ki kira womin sauran’ yan uwanki muci Abincin tare”
“to shikenan Abba yadda kace haka za’ayi”
Haka kuwa akayi taje ta kira Nana, ta wuce dakin Jawwad dan kiransa, Amma Jawwad yanata rubuce2 shikuma Jalal yanata babbakawa cikinsa hayaki.
Dauke kanta tayi kaman bata ganshi ba tace “Mutanen Bauchi, Yaya Jawwad ko kanemeni ko?”
Haka nan jin muryar ta yasa gaban Jalal faduwa har yake kokarin boye sigarin hannunsa
Jawwad yace “nina isa, dazu na shiga cikin gidan amma na tarar ana fitina shiyasa na tafi”
“to shikenan, Abba yace in kiraka duk tare zamuci Abinci saboda Akwai Albishir daze mana”
Jawwad yace “Allah Auta, wane Albishir zeyi mana?”
“Ahh kajika ai kai yakamata in tambaya, tunda tare kuka dawo”
“to shikenan gani nan zuwa” Jalila ta mike ta fice, Sam Jalal beji dadin wannan dauke kan da tayi masa ba, Jawwad yace “Jalal zo muje”
“A’a jeka seka dawo” Jalal ya bashi amsa, Jawwad yace
“Wallahi baka isaba, tashi muje, Abban bakonka ne? Yakamata muje tare”
Jawwad ya takurawa Jalal, badan yaso ba ya bishi, suna shiga palourn Abba Idon Jalal akan Jalila yafara sauka, tana sanye da riga da skirt na Atamfa, kaman ajikinta aka dinkasu cif dasu, tayi parking din gashin ta, ta kashe dauri ba kwalliya a fuskar ta amma tayi kyau matuka, bata kalli inda Jalal yake ba suka cigaba dayiwa Abba surutu ita da Nana, Su Jalal suka Zauna, Jalal suka gaisa da Abba, Abba yace Jalila zubawa su Jalal Abincin mana”
Ba tace komai ba ta fara zuzzuba musu Abinci, dakin yayi shiru suna Cin Abinci se surutun Nana dake tashi, gaba daya Jalila takasa sakewa taci Abinci saboda tsabar kallon da Jalal yake mata, bakowa ze gane ita yake kallo ba amma ita tasan ita yake kallo, shi kansa ba iya cin Abincin yake ba jujjuya cokali kawai yakeyi, Jalila tace “Abba ka gayamana Albishir din naka, nifa duk na kagu inji”
Abba yayi murmushi ya kalli Jawwad yace
“Jawwad gaya musu mana” sunkuyar da kai Jawwad yayi yana murmushi, Abba na yayi murmushi sannan yace “Na canza maganar Auren Naja da Jawwad, zuwa Jawwad da Hanan, nan da wata hudu Insha Allah”
Wata irin Ajiyar zuciya Jalila tayi, Nana tace “dama ni zuciya ta tabani, Masha Allah, Allah yasanya Alkhairi ya nuna mana lokacin”
Jalila tace
“Abba ni na rasa abunda zance gaba daya, mungode Allah daya sa ka gano abunda nake ta maka nuni, Abba Allah yasaka da alkhairi wannan aini akayiwa ga Yayana Kuma ‘yar uwa ta, Amma shine Yaya Jawwad baka gaya mana ba, itama Hanan bata gayamin ba”
Abba yace “Itama Hanan din bata sani ba ai, daddynta be gaya mata ba, sannan babban Albishir na biyu shine; Kakar Hanan itace yayar mahaifiyar mu, Inna Asma” au”
Da Sauri Jalila ta waiwaya gurin Jalal dan in bata manta ba sunyi zancen da shi, amma kawai ta basar tace “Abba tunda naje tabani Labari nayu tunanin hakan, Amma nayi shiru ban fada ba saboda bani da tabbas, godiya ta tabatta ga Allah”
Jalal yai karfin halin cewa “Abba kaga yadda Allah ke juya lamarin sa, a baya kayi ta bulayin neman danginka, ashe suna tare da kai baka sani ba, ina tayaku farinciki Abba, Allah yakara hada kan iyalanka”
“Ameen Ya Allah ABDUL JALAL, Amma naji dadin wannan Addu’ar taka, kuma zance ka gaskiya ne, na dade ina bulayin nemansu amma ba zato ba tsammani na samesu ta silar ‘yar Auta ta”
Sukayi murmushi gaaba daya. Abba ya dora da cewa ” munyi magana da daddynka, Jalal ranar Asabar Insha Allah zasu kawowa Mahmud kudin Aure, suma tareda na Jawwad za’ a hada, gaskiya zanso a hada da naka, yadda kuka taso tare ga aiki ya samu kamata yayi a hada da kai gaskiya”
Dan guntun murmushi Jalal yayi wanda iyakarsa lebensa yace
“Abba Jawwad dai yayi, nikam se yadda Allah yayi, babu uba nagari da ze bawa ďan shaye2 auren ‘yarsa, koda za’ a bani saboda dukiya ta ne”
Gaba daya tausayinsa seda yakama su
Abba yace
“karka damu kaji Jalal, babu wanda ze hanaka ‘ya, kai mutumin kirki ne, wanda ya zauna da kai ne ze gane hakan, Insha Allah komai ze wuce, ka cigaba da Addu’a sannan ka dinga kokarin ka dena shaye2, babu abunda ze hana abaka’ ya Aure” jinjina kai Jalal yayi yace
“to shikenan nagode Abba”
Nana ta dan zumbura baki tace
“Abba wai meyasa baza’a hada dana Jalila bane?”
Abba yace “Saboda ban gaji da ganinta ba”
“Auni ka gaji da ganina kenan?” Nana tai maganar kaman zatayi kuka.
Abba yace “A’a Munyi maganar da Babanta, yace; Abari ta kammala karatu tukuna saboda yanayin Aikin Ahmad din, nan da shekara daya ne zata kammala in Allah yasa zamu gani itama zan Aurar da ita ga Ahmad”
Gaba daya kunya ta kama Jalila ta mike tace
“nikam seda safenku Abba” ta mike da sauri ta bar palourn, gaba daya Jalal ji yayi kaman Abba ya masa yayyafin wuta a kirjinsa, shima ya mike yai musu seda safe.
Haka suka watse daga palourn Abba, babu wanda yabi takan Maama balle susan halin da take ciki, ta kule a daki ta rasa abunda yake mata dadi, bata taba zaton yaran yaya mairo zasu iya zaginta ba, gashi mijinta da yaranta ma sundena shiga harkar ta suna fushi da ita.