ABDUL JALAL PART 2

“Ni na manta da ke a doron kasa, in ban manta ba haduwar mu ta karshe yafi shekara, katsam jiya kika fadomin a rai, da irin abubuwan da kike aikatawa, haka nan naji kasa sakewa, zuciya ta tanata bani wani abu zw faru, katsam akan hanyata naga motarki na kokarin shigowa layinmu, shiyasa na biyoki dan duk inda kikaje babu Alkhairi Hannah “
Gaba daya kan Hannah ya kwance bata taba tunanin zata hadu da Jalila a wannan lokacin da take shirin hurawa Jalal wutar da babu me iya kashe masa ba.
Jalila ta kalli daddy tace
“Wallahi daddy karya take yiwa Jalal, ba wani abu dayake tsakanin ta dashi, sema ita da take kokarin cutar da shi”
With full confidence Hannah tace
“Karya kike inyiwa Jalal karya, ina dauke da cikinsa ne, kuma wallahi wannan karon bazan zubar ba, kamar yadda yasaba sani ina zubarwa”
Cikin tashin hankali daddy yace “Jalal din nawa ne yai miki ciki? Kiji tsoron Allah, bana tunanin hakan ze faru, wancan karon akan wannan maganar yayi fushi har ya nemi ya bar kasar nan, narasa waye me gaskiya a tsakaninku”
Jalila tace “Daddy ka kyale ta taje ta kai duk inda zata kai, Kai ka haifi Jalal kasan abunda ze iya da wanda baze iya ba, kasan baya shakkar kowa, idan ya aikata baze ji tsoron gaya maka ba, Daddy karya takeyi wallahi, I dan ba haka ba, taje ta shigar da karar”
Sosai Jalila take kokarin kare Jalal, abunda yabawa daddy mamaki, dan agabansa ya sha ganin irin artabun da sukeyi da Jalal, amma wani tabbaci take da shi akan Jalal haka, kuma y’a kayi tasan Hannah?
Ilham kam harar Jalila kawai takeyi ji take tamkar taje ta maketa a gurin, sekace Jalal din ubanta ne, ita so take tayi amfani da wannan damar, a tirsasawa Jalal yin Aure, amma Jalila nata karewa.
Mummy tace “Waike meye haka? Ban hanaki shiga duk wani shirgi daya shafi dana ba, banda munafunci da son jin kwakwaf hada biyo ta kizo kiji me ze faru, kina…….
“Rufe min baki khadija, Kinsan meyasa take kokarin kareshi, meye da dannaki da kike wani kumfar bakin adena shiga harkarsa”?
Daddy ya kalli Jalila yace “Jalila a ina kika san wannan yarinyar?”
Jalila ta kalli Hannah tace “daddy nasanta a gurin birthday din Jalal ne, Kuma sannan”
Sekuma tayi shiru, “Sannan kuma me?”
Daddy ya tambayeta, Jalila tace “bakomai daddy, amma makaryaciya ce”
Hannah ta fashe da kuka tace “Shikenan tunda ba ‘yar kuce niba kun zabi zubewar mutuncina, wallahi mutuncina baze zube ni kadai ba, ku saurari sammaci, wallahi karar Jalal zanyi”
“Karki fasa sekin dawo, Amma idan har karya kike abunda ya faru da iyayen gidanki ze faru dake, idan har kin iya makirci za’ a nuna miki ranar dukiya, ki fice kibar gidan nan da kafafuwanki kafin insa akama min ke”
Hannah ta tsorata da gadar zaren da Jalila tayiwa su Jeje suka rufta, dan haka ba kunya ta juya zata fice, daddy yace “Amma ta tafi ba’a gano bakin zaren ba”
Jalila tace “daddy ka rabu da ita, ko ta kai kara, kota bari ya dawo ayi maganar amma babu dalilin da zesa ta dinga maka karya tana bata maka rai akan danka”
Ta juya ta kalli Mummy tace “Mummy Allah ya huci zuciyarki, ban biyo Hannah dan shiga cikin lamarin iyalinki ba, sedan sanin hatsarin Hannah ga rayuwar Jalal, Amma Insha Allah kome ze faru bazan kuma shiga lamarin ba, in dai ya shafi gidan nan”
Ta juya zata fice, daddy yace “Jalila ita wannan yarinyar wacece? Sannan meye hatsarin ta ga Jalal? Menen alakarsu?”
Jalila tace “Daddy ba a bakina yakamata kaji ba, amma dai nasan babu wata alaka ta kusa dake tsakaninsu, na tafi se an jima” ta juya ta fice zuciyarta cike da bacin rai.
Maama ta dubi Yaya mairo tace “Yaya wannan jinin kuwa na lafiya ne?”
“Al’adace haka yake zuwar mata”
“haba Yaya, kalli guda gudan dayake zuba kice min Al’adace, yakama tunda nazo da mota mu kaita Asibiti”
“ba wani Asibiti da zamu kaita” yaya mairo ta bata amsa tana kokarin temakawa Naja ta mike zaune, amma tana tabata taga bata motsi, numfashinta da kyar yake fita, ga jini se cigaba da fita yake daga jikin Naja, ba shiri Yaya mairo ta mike, Maama ta temaka mata suka gyara Naja, suka sata a mota se Asibiti,
Sunkai awa biyu suna jira, Yaya mairo takira Naja a waya, tazo suka hadu a Asibiti, likita ya fito ya tambayesu alakarsu da Naja, sukayi masa bayani, yace su bishi office dinsa, haka suka bishi sukaje suka zazzauna suka zubawa likita ido, ya danyi gyaran murya sannan ya kallesu yace
“To kun san duk abunda yasamu bawa mu kaddarine daga Allah, kuma Allah yana jarrabar bayinsa ta ko ina, kuma dukkan musulmi se yayu Imani da kaddara sannan Imaninsa ze cika, Hakikanin gaskiya mara lafiyar ku tana dauke da ciki karami, kuma tayi Amfani da miyagun kwayoyi wanda hakan yayi sanadiyar zubewar cikin jikinta da kuma lalacewar mahaifarta”
“Innalillahi wa inna ilaihi raji un” shine abunda suka dinga nanatawa, gaba daya Maama taji jikinta yafara rawa, Yaya mairo ta dora hannu aka tafara ihu, likita yace “Haba baiwar Allah kamar ba yanzu nagama yi miki nasiha ba, ba wannan bama, yarinyar nan ta zubar da jini da yawa, Akwai bukatar a sama ta jini, kuma a bincike da mukayi tana da cutar Hepatitis B, (ciwon Hanta), dan haka ku gaggauta nemo Jini, a duba a ‘yan uwa wanda jininsu yayi dai2 se a samata”
Haka suka fiti office din nan suna salallami, jiki a sanyaye Yaya mairo tace “bari a kira yayanta a waya, Zainab kira Jawwad suzo a duba in jininsu zeyi a samata”
Da sauri Maama tace “Wane Jawwad din? Jawwad yana Abuja ya samu Aiki ai, nikam Yaya mairo ga wannan” tasa hannu a Aljihu ta dakko kudi tabata sannan tace “ga wannan ku sai magani, zan koma gida magariba tayi, se na dawo dubiya, Amma yakamata kunemo wanda yake da alhakin cikin nan, yazo ya dauki nauyin ta, se anjimanku”
Maama ta juya ta fito daga ward din, tana ta tunani tareda mamaki, da kyar Maama ta kai kanta gida, saboda tunani da Mamaki, da tuno marin da tayiwa Jawwad saboda Naja se taji gaba daya jikinta yayi sanyi.
Haka ta koma gida jiki a sanyaye, tunda ta koma take tunani, Nana ta lura da Yadda Maama jikinta yake a sanyaye dan haka taje ta sameta a daki take tambayar ta “Maama wai me yake damunki ne? Tukuna ma ina kikaje?”
Dan shiruu Maama tayi, sannan tace “Nana naso inyi ganganci da rayuwar dana”
“gangancin menene?”
Nan ta kwashe komai ta gayawa Nana, Nana tayi murmushi tace
“Allah sarki Rayuwa, Maama kinga wannan abun to izina ne a gareki, Allah yasa kar alhakin marainiyar Allah ya kamaku, kunsaka Jalila kuka ta zubda hawaye ba a dadi, ku zageta ku mata cin mutunci, ku mata gori amma se gashi su sunyi Abun kunyar da ‘yar arnan ba tayi ba, Maama lokaci yayi da yakamata ki gane su waye ke kaunar ki, Yaya mairo’ yar uwakki ce amma abun hannun ki takeso, ki duba irin biyayya da Jalila tayi miki tsawon lokaci, duk fitsararta da kuke fada, ke dai bata taba yimiki ba, se dai Yaya mairo, Maama a ci zarafin iyayen mutum dacin abun ya wuce yadda kike tunani, kun cutar da ita gaskiya, fatan Allah ya yafe muku, yanzu seki gane, Ummi da take ba musulma ba da farko, tayiwa ‘yarta tarbiyar da wanda aka haifa a musulinci bata yiwa’ yatta ba, Allah yasa hakan ya zama izina a gareku”
Maama kasa cewa komai tayi, se jujjuya maganganun Nana da takeyi, tabbas Maganganun Nana gaskiya ne,
Nana tace “Maama bari inje daki inada Assignment da zanyi”
Gyada mata kai kawai Maama tayi, Nana kuma ta fice, koda taje dakinsu Jalila tana kwance idonta a rufe, kaman me bacci, amma ba baccin take ba, tunanin abubuwa da dama ne ke zagayawa a cikin kwakwalwarta.