ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Shikan sa daddyn sa rabon da ya ganshi wata hudun kenan, ya sha manyan kaya yayi kyau, babban abunda ya daurewa daddyn sa kai be wuce yadda yayi sallama ba kuma ya risina yana gaishesu, suka amsa
Daddyn Hanan yace “ABDUL JALAL ashe kazo, Amma ban ganka ba, bamu hadu ba sam”
Jalal yayi murmushi yace “banfiye fitowa ba shiyasa baka ganni ba”
“Masha Allah, Yaya gurin Aikin na ka?
” Lafiya kalau, ina jin dadin Aikin, Amma nafison zama na a kano, gashi sunce sena kara watanni, bana son zaman lagos din nan”

Daddyn Hanan yace “Nayi farinciki ganinka ABDUL, kayi kalau da kai, me yasa baka son zaman lagos din?”
Daddyn sa yayi murmushi yace “baya son sabga da Mata, kasan kuma lagos babu ruwansu da Addini ko Al’ada, in munyi waya yana gayamin ;shi baya son Abunda matan kabilun nan sukeyi” suka kwashe da dariya, Abba yace “Karka damu Kaji Jalal, kana da gaskiya”
Daddyn Hanan ya kalli baban Yusuf yace

“Kaga yaron dana ce ka samarwa Aiki, Ansamu improvement kwarai a tattare da shi, gaskiya ‘yar Baba tana da kai sosai, ita tayi wannan tunanin a samo masa aiki, tace min in aka samo masa aikinyi hakan ze dauke masa hankali da ga barna da yake kuma ya rage masa damuwa da kadaici, a haka gata kaman bata iya komai ba se shagwaba da tsokana amma tafi Hanan kai”

Baban Yusuf yace “ABDUL JALAL karka damu kaji, haka sha’ anin Aiki yake, ba inda baya kai mutum, kai dai kayi gaskiya ka rike Addininka kuma kaji tsoron Allah”
Sukace hakane, daddyn Hanan yace

“Karka damu Jalal, za’a san abunyi, babban farincikin danayi, daga can lagos din sun kirani suna yaba maka, naji dadi sosai wallahi, Abunda yake kara shashi shaye2 da wannan phobia din na rashin son mutane, hadda psychological issues, yana bukatar me jansa a jiki, be kamata saboda halin da yake ciki na shaye2 ayi watsi da shi da lamarin sa ba, kokuma a dinga yi masa mummunan furuci ba, ko mutane su kyamace shi gaba daya ba, kuma wannan yana daya daga cikin matsalar society dinmu, wallahi wanima ko masallaci yaje baza’a hada sahun salla da shi ba, daga haka suke fara janye jikinsu daga mutanen kirki, se na banza su janye su, maimakon a jasu a jiki da nasiha da rarrashi”

Daddyn Jalal ya dan girgiza kai yace

“Wallahi you said it all sir, Jalal gaba daya gudun mutane yake se tsirari, musamman mata, saboda yarasa wani babban jigo a rayuwarsa da duk wanda yarasa dole yayi kuka, shiyasa da Wannan ‘yar tawa Jalila da Jawwad banida abunda zan biya su da shi, ko iya haka aka tsaya sun kawo gagarumin sauyi ga rayuwar ďana, bani da bakin godiya, ban taba tsammanin za’ a samu sauyi kwatankwacin haka akansa ba”

ya karasa maganar yana kokarin hadiye kwalla da ta taru a idonsa, gaba daya sukayi tsit cike da tausayin Jalal da mahifinsa, Jalal ya sunkuyar da kai, yana tuna Abubuwan da suka shude na rayuwarsa, Ya fuskanci kaddara daban2, gaba daya tausayin kansa dana daddy ya lullube shi.

Jalila kam cikin sanyi jiki, tace
“Haba Daddy, ni me nayiwa rayuwarsa dana cancanci wannan godiyar da kuke tayimin, wallahi banga abunda nayi masa dana cancanci hakaba, ni yakamata in baku hakurin cin zarafin sa dana dingayi a gabanku, nake kiransa da kalamai marasa dadi Amma….
Sekuma maganar ta kasa fitowa saboda kuka, dan Haka ta mike, da sauri tabar dakin.
Shikam baban Yusuf mamaki ne ya cika shi, ace kamar wannan yarinyar ta sauya akalar Rayuwar matashi da ya riga ya dilmiya a gurbatacciyar rayuwa, itakuwa wace irin baiwa ce da ita, ko dayake ance mata ‘yan baiwa ne, sedai kowacce akwai sigar da take Amfani da tata.
Jalal yace “daddy seda safenku, zanje in kwanta”
Abba yayi karfin halin cewa “to shikenan Allah ya tashemu lafiya”
Ya amsa da “Ameen” ya mike ya fito kaman wanda kwai ya fashewa a ciki.

Jalila takoma part dinsu ta canza kaya, tayi wanka, har tayi ta fito tausayin Jalal da daddy ne fal a ranta, se goge Hawaye take lokaci zuwa lokaci.
su Hanan suka dawo, suna zuwa suka tarar har tayi bacci.
Nana tasa hannu tasheta, Jalila ta mike zaune tana kallonsu tace “meye kuma na tashi na?”
Nana tace
“ya akayi kika taho ne? Tun a can Maama take nemanki, Ahmad se kiranki yake a waya baki daga ba”
Se yanzu ta tuna wayar tana gurin Jalal.
“Su Abba ne sukazo shiyasa na dawo gida” ta basu amsa
Hanan tace “keda wa kuka dawo, dan nasan baki san hanya ba”

“ban sani ba, uwar kwakwakwafi a isak na dawo”
Hanan tace “daga tambaya? Allah yabaki hakuri”
Siyama tace “Jalila wallahi Jalal ya hadu, kinata masa wulakanci, wani kallo da yake miki kamar ze cinye ki”

Sukasa Jalila a gaba da tsokana tayi musu banza ta kyalesu.

Jalal yana zaune yana ta tunanin abubuwan da suka faru dashi a baya, shi kansa yana sarawa namijin kokarin Jalila, ta iya lissafi gata da himma da kokari, duk rashin kunyarta da taurin kai, akwai kawaici da tausayi, duk zamansa da Jeje besan Cutar shi yake ba, Amma ita a ranar da suka fara haduwa ta gane hakan, ta saka rayuwarta a hatsari da dama saboda shi, besan mezeyi ya saka mata ba” kallon wayarta data ke faman ringing yayi, sunan My yana yawo akan screen din wayar, har wayar ta gaji ta katse, hotonta ne akan screen lock dinta tana murmushi, ya kurawa hoton idon na dan lokaci, ya sa hannu ya shara screen din, wayar ta babu key a kai, wallpaper dinma hotonta ne da Nana, kanta babu dan kwali, ta dan turo baki Nana kuma tana dariya, ya dade yana kallon wallpaper, yayinda kiran Ahmad ya shigo ba’a dadi, ya gaji sa wayar a silent ya ajiyeta ya cigaba da tunani,
Yana cikin tunanin ne, Angwaye suka dawo.
Jawwad beyi mamakin ganin Jalal a gida ba, dan ba karamin aikinsa ne gurin dinner din ma yaki zuwa gaba daya ba.
Gaba daya Ahmad ransa a bace yake yana ta tunanin ina Jalila ta shiga haka? Ya kira har ya gaji amma bata dagawa, kuma ya duba hall din nan be ganta ba, sukayo wa Angwaye rakiya yana shirin fita daga dakin yace
“Jawwad zan tafi seda safe, Dan Allah ko Jalila ta dawo ne ? Nakirata har nagaji bata dagawa”
Jawwad yace
“Aini tunda ta sauka akan stage din nan ban kuma ganinta ba, Amma ka kira wayarta mana”
“Aina kira wayarta ta bata dagawa”
Jawwad yace
“Idan ma ta dawo yanzu nasan tayi bacci, Amma bari in kira wayar ta ta”
Jalal yana jinsu amma be tanka musu ba, Jawwad na kiran wayar Jalila yaji ringing dinta a dakin, da yake yasan tone din wayarta, Jawwad ya kalli inda ringing din wayar ke tashi, tana kan teburin dake gaban Jalal tareda wayoyinsa,
Jawwad ya tafi gaban tebur din, yaga tabbas wayar Jalila ce, Jawwad ya kai hannu ze dau wayar, yace “ya akayi kuma wayarta tazo nan?”
Jalal ya sa hannu ya dauke wayar ya kashe wayar gaba daya yace
“wayar tana gurina, tare muka taho”
A fusace Ahmad yace

“Amma dan wulakanci kanaji ana maganar kayi banza? Meyasa zaka dakko ta? Na lura tunda kazo kake wani jin kai da nunawa mutane gadara, ubanwa kafi? Zaka dinga nunawa mutane jin kai, meye naka na shiga sabgarta? Waye dinta kai? Dama ana fadin kana shaye2 wallahi kamin hauka kurata zansa sumaka duka”
Jawwad da sauri yace

“yi hakuri Ahmad, baka fahimci Jalal bane, shima yayanta ne yana da iko akanta, Bekamata ka dinga wannan maganganun ba, an riga an zama daya”
Zuciyar Jalal wata irin tafasa take, ba dan Dalilin Jawwad ba wannan banzan ya isa ya tsaya gabansa yana zaginsa, dan takamarsa yanada kaki, idan takamar Ahmad kakin soja, shikuma yana da abunda ze siye shi da kakin nasa yasa Aljihunsa
Kawai Jalal ya jingina da kujera ya zaro karan sigarinsa ya kunna yana kada kafa.
Karshen kuluwa Ahmad yayi, wai uban me Jalal ya taka yake wannan gadarar.
Abdallah ne ya shigo dakin da sauri yana fadin “Jawwad ana nemanku a part din daddy, kaida Ahmad”
Jawwad yace “Allah yasa ba wani abun mukayi ba?”
“ba abunda kukayi ance dai in kiraku”
Jawwad yace “Amma a daren nan haka?
” kuzo dai muje, ko menene kwaji a can”
Seda Ahmad yayiwa Jalal wani banzan kallo, yayinda shikuma Jalal yakara yawan hayakin da yake fesarwa a iska, yana lumshe ido Ahmad ji yake da da bindiga se ya harbe Jalal, haka suka fita suka tafi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button