ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Abba yace

“Masha Allah, Alhaji Habib duk abunda nayiwa Jalal tamkar Jawwad nayi wa ne, ABDUL JALAL tun tasowarsu da Jawwad yake kaunar sa, kusan kaso mafi yawa na Rayuwarsa a gidana yayi ta, dan haka yiwa kaine Allah yabasu zaman lafiya”

Itama Hajiya Salma godiya takuma yi da nuna farincikinta akan wannan lamarin.

Jalila kam tana zuwa ta zube a jikin Hanan tana wani irin kuka me sauti, Hanan ta kalli Nana suka hada ido ta dan jinjina kai, sannan tace

“Wai Jalila lafiya kuwa? Meyafaru ne haka?”
Jalila ta dago idonta da tuni yayi Ja tace

“Hanan wai an daura min Aure nima”
Nana tace
“Aure, dawa aka daura?”
“Nana wai Jalal aka auramin, meyasa a kayimin haka? Takuma fashewa da kuka
Hanan tace

” kece baki sani ba, mu mun riga munsan za’a daura muku Aure”
Zumbur Jalila ta tashi zaune ta kalli Hanan
“Amma meyasa baku gayamin ba?”
“Saboda ana gudun wannan shirmen dazaki yi, aka gargade mu karmu sake mu gaya miki, kuma ni banga aibun abunda akayi ba, hakan shine dai2”

“Haba Hanan meyasa zakimin haka? Ko dan na tsaya tsayin daka kin samu wanda kikeso, shine ni zakimin haka?”
“Jalila abunda ya dace akayi, nasan abunda akayi miki babu dadi, Amma iyaye basa zabawa yaransu abunda ze cutar dasu, wallahi Jalila sekin fi kowa Alfahari da shi nan gaba, Yana sonki, kuma kema kina sonshi, sann……
” Dan Allah dakata Hanan “
Jalila ta katseta
” dan bake akayiwa ba ko? Ina da wanda nakeso amma an Auramin wani daban, shine ya gaya miki yana sona, babu wani abu makamancin soyayya a tsakanin mu, ta yaya zan fara rayuwar Aure da Jalal, bahagon mutum me wani irin murdaden hali,
Mahaifiyarsa bata kauna ta, ko kinsam tana zargina da ďanta, Mahaifiyarsa tana da wanda takeso ya Aura, ta yaya zanyi zaman Aure da wanda mahaifiyarsa bata sona, Hanan nasha wahalar Rayuwa, yakamata ace lokaci yayi da zan huta, wannnan Auren tamkar kara jefa Rayuwa ta cikin wata wahalar ne, nasha wuya Ina bukatar zuciyata ta huta Nashiga uku ni Jalila “

” Subhanallah ke Jalila meye hakane kikeyi? “

Muryar Mummyn Hanan ce take magana, da suka shigo ita da Maama, tace

“duk Nasihar da’akayi miki baki jiba kenan? Meyasa bazaki dauki kaddara ba, ko ba’ayi haka ba dama Allah ya rubuta shine mijinki”
Kuka Jalila takuna fashewa da shi maama tace

“Jalila kidena kukan nan haka, batun mahaifiyarsa bata sonki ze wuce, musamman idan ta gane mahinmancin ki ga danta, Jalila tunda kika iya jure rayuwar gidana duk taren kalubalen da kika fuskanta daga gareni da ‘yan uwana, bana tunanin akwai wani kalubale daze tsoratar dake, Anmiki ba dai2 ba tabbas, Amma kiyi hakuri ki rungumi kaddara ki riki mijinki, ki masa biyayya, idan kikayi hakuri kikayi biyayya se Allah yayi miki Rahama saboda hakan”

Mummy tace

“wannan gaskiyane, kuma shi Ahmad da kike magana, ai Daddy ne yace ya bashi da farko, yanzu kuma ya bashi hakuri, Jalila na tabattar nan gaba sekin fi kowa jin dadin zama da shi”

Jalila sam bataji nasiharsu na shigarta ba, ita kawai an gama da ita basu san waye Jalal bane shiyasa suke fadar hakan.
Maama tace
“Nana ki shirya kayanku, gobe in Allah ya kaimu hadda ita zaku tafi maiduguri”
Jalila na jin haka ta kuma rusheewa da kuka.
Yusuf ne ya shigo dakin shima a fusace yana fada

“haba Mummy, meyasa daddy zeyi haka dan Allah? Yaza’ayi a Aurawa yarinya wanda bata so, kuma bayan yasan ďan shaye2 ne, a family din nan ba wanda aka taba yiwa Auren dole meyasa za’a fara akanta?ga shi sam wannan yaron bashi da mutuci, ga gadara da girman kai”

Mummy tace

“Sannu jagoran marasa kunya, meyasa bakayiwa daddyn ba seni? Kafi su sanin abunda yakamata ne?”
Hanan Kallon yaya Yusuf kawai take yadda yake zakewa yana masifa

Jawwad nai yai sallama a dakin shima fuskarsa dauke da damuwa, ya hango Jalila ta takure a gefe idon nan kaman gaita saboda ja, ga fuskarta duk ta kumbura. Bebi takansu Maama ba gaje gabanta ya tsuguna yace
“Baby why? Meyasa kike kuka haka? Gashi baki da lafiya? “

“ba dole yarinya tayi kuka ba, an mata Auren dole, an Aura mata ďan shaye2 wanda bata so”

Jawwad yace

“Yusuf meye haka? Ana kokarin hankalin ta ya kwanta kana son ka kunna wata wutar, koma dai meye an riga an daura Auren nan, ayi musu Addu’a da fatan Alkhairi mana” Jawwad ya kalli Jalila yace

“We are sorry Baby, kaddara ta riga fata, dana san ba kya son Jalal bazan bari ayi Auren nan ba, saboda nasan Jalal baze ban kunya ba shiyasa na amince”

“Yaya Jawwad ni bana sonshi”

“Jalila kulawar da kike bashi da babu so bazaki yi ba, na miki Alkawarin Jalal baze bada kunya ba, kuma shi Alkhairi ne a rayuwarki, dan Allah Jalila ki kula da rayuwar Jalal kamar yadda kike yi abaya, Nabaki amanar ďan uwana please Jalila” ya karasa maganar kamar zeyi kuka.
Girgiza kai Jalila ta shiga yi
“Yaya Jawwad….
“Shhhh kiyi shiru, ki karbi Amana ta kidena wannan kukan”

Hanan tace

“Jalila son da Haidar yake miki baze bari a baki abunda ze cutar dake ba kiyi hakuri da kaddara Queen”
Jalila shiru ta musu ba tace komai ba, ita ka dai tasan me takeji a ranta.
Jawwad ya mike yace
“Mummy seda safenku” sukayi sallama.
Yusuf dai ya cigaba da banbami da mita.
Su Maama suka cigaba da rarrashin ta tareda Nasiha.
Hanan kuma ta shiga hadawa Jalila kayanta dukda tarin gajiyar biki dake tare da ita.

Jawwad yakoma masaukin Jalal, ya tarar Jalal yana shirin kwanciya, Jawwad yace
“Ango ka sha kamshi”
Jawwad ya lura kaman Jalal baya walwala
“Jalal Lafiya kuwa? Naga kaman baka walwala, ko baka son Auren”?

“Jawwad ba wai bana son Auren bane, idan inason Auren itafa?”

Jawwad ya dafa kafadarsa yace

“brother karka damu, nasan zataji babu dadi da farko, saboda an mata bazata ba tareda masaniyarta ba an daura mata Aure, Amma nasan tana sonka, kuma a hankali zaku daidaita cikin kankanin lokaci”

Jalal yace

“Hmm haka dai kake gani”

“Hakane ze kasance, ni dai gata nan Amana Jalal, kayi hakuri da ita”
Jalal bece komai ba ya danyi murmushi, daga nan suka shiga wata hirar.

Hatta Inna ba’a barta a baya ba gurin rarrashin Jalila da yi mata nasiha, dan ita Inna har cikin ranta Jalal yayi mata, dan seda ta zage Yusuf tsaf saboda masifar da yakeyi akan anyiwa Jalila auren dole.

Jalila dai yau tayi kwanan bakinciki, dan sam bacci ko na minti goma batayi ba, Ga Jalal ya kwace mata waya balle ta kira Ahmad, gaba daya tausayin Ahmad takeji, yasaka rai akan Aurenta, yana da matukar kirki ya nuna mata soyayya, shiko wannan Jalal din da magana se ya ga dama ta ina ze nuna mata wata soyayya. Har akayi kiran sallar Asubah batayi bacci ba se sakawa da kwancewa, bayan tayi salla ta koma ta kwanta tana jin yadda kanta ke sarawa, ga kirjinta da yayi mata nauyi, se karanto Addu’oi take daban2 ko zuciyarta tayi sanyi.
Wajejen karfe bakwai da rabi, Mummy tazo ta kira Jalila suka tafi cikin gida, dakin da’aka sauki hajiya Salma ta kaita, mutane sun ragu sosai duk an watse, se tsirarin mutane da zasu raka Hanan Abuja, sekuma ma’aikata da suke ta kokarin gyara gidan.
Bayan sun shiga Jalila kanta a sunkuye ta gaida Hajiya Salma da Antin Jalal, Suka Amsa mata Antyn Jalal tace
“Sannu Amaryar mu, Kin tashi lafiya?”
Take Jalila ta kuma jin wasu hawayen suna zubowa daga idon ta, Mummy tace
“Ikon Allah, har yanzu baki gaji da kukan nan ba?”
hajiya Salma tace
“haba Jalila, banyi zaton haka daga gareki ba, mun san an miki laifi amma kiyi hakuri, Jalila zakiyi Alfahari da mijinki, yana sonki fiye da yadda kike tunani, gaba daya hope dinmu yana gurin Allah kuma yana gurinki, dan Allah ki kwantar da hankalinki ku zauna lafiya, ki gode Allah, Jalal baya kule kulen mata, ke kadai ce macen dana san yana saurara, kiyi hakuri Jalila “

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button