ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Cikin kuka Jalila tace

“Mummynsa fa bata sona, tace in rabu da shi, kuma ba irin maganganun da ban gayawa Ilham akan sa ba, na kirashi da sunaye marasa dadi, kuma kawai ace shi na aura”

Hajiya Salma tace

“to shine me? Mahaifiyarsa bata sonki ni ba’a gaya miki abunda tayi min ba, ita da Saudat, gidan mijina abun kaunata seda ta rabani da gidan hankalin ta ya kwanta, ko kin fison a ya auri Ilham din ne? Jalila kece zakisa zaman gidan Aurenki yayi dadi in kin so, ki manta da abunda ya riga ya wuce kinji yarinya ta, Allah ya Albarkaci rayuwar Aurenku, kije ki shirya anjima kadan zamu tafi”

“wai a maidugurin zanta zama? Makaranta fa?”

Antyn Jalal tace “A’a ba’acan zaki zauna ba, Se a inda yakeso zaku zauna, amma akwai dalilin zuwanki can ďin”
Jalila dai ba tace komai ba suka cigaba da rarrashin ta. Haka Maama tazo ta ja hannunta domin fara shirin tafiya.

Daddy ya samu Hajiya Salma a masaukinta, shar da ita bakace ita haifi Mahmud ba, sekace kaninta, har yanzu tana tare da Gayunta,
Daddy yace “To Salma kinga abun Allah ko ba zato ba tsammani danki ya samu matar Aure, kodayake na dade ina burin Jalal ya Auri yarinyar nan”
Hajiya Salma tace
“Hakane, yarinyar tana da nutsuwa da kirki, dangin yarinyar nan sun gama yimana komai, Amma daddy wai ya’akayi abun nan ya kasance”
“hmm ai shekaranjiya dana zo, yazo ya ganni muna tare da iyayen Jalila, shine suke tambayarsa ya aikinsa? yace bayason zaman lagos, nake ce musu yanayin sabanin Addini da al’adun mutanen garin ne yasa baya son zaman garin, bayan ya tafi ne, kawai Captain Abdurrasheed yace ; inyana da wadda yake so ai masa Aure ya tafi da matar can lagos, se nake ce musu bana tunanin yana da budurwa, saboda yace yasan babu me bashi ‘yarsa yana wannan halin, se captain Rasheed yace; indai yana son Jalila ya bashi ita, shine aka kira Jawwad da yaron daza’ a bawa ita da, aka tambayi Jawwad yana ganin in aka Aurawa Jalal ita ze zauna da ita? Jawwad yace “ai Jalal yana sonta, dan haka suka kira shi wancan yaron suka bashi hakuri, shikansa Jalal be saniba se jiya a gurin daurin Auren”

Hajiya Salma tayi ajiyar zuciya tace

“Allah me yadda yaso, kaga Al’amarin ubangiji, ba zato babu tsammani my Son yasamu mace ta gari”

“Hakane amma yaushe zaku bashi ita? Naji kince da ita zaku tafi maiduguri”

Tai murmushi tace

“Daddy kenan, yadda aka daura aure a bagas ba tareda ya sha wata wahala ba, bazan bashi yarinyar nan a bagas ba, bazamu bashi ita ba se mun tabattar da irin Son da yake mata, dagaske yana sonta kokuwa? Zata zauna damu tasanmu, sannan muyi mata shiri irin namu na ‘yan barno”
Daddy yai murmushi yace “haba Salma, a takaice dai ta wani bangaren kuna son ku wahalar min da yarone kawai”
Tayi murmushi tace

“Zamu temake shi dai, yawwa sannan Jalila tana kukan matarka Khadija bata sonta har tana zarginta da Jalal, wannan karon bazan lamunci duk wani nau’i na rashin mutunci daga gareta ba, idan baka dau mataki akan wannan lamarin ba, Zeyi wuya mu bawa Jalal matarsa anan kusa, saboda nafi kowa sanin khadija nasan abunda zata iyayi, a wannan karon bazan bari ta cutar da ‘yar mutane ba kamar yadda ni tayimin ba”
Ta mike tsaye tace

“daddy bari inje in karasa shiryawa, da wuri zamu tafi”

Ta wuce cikin dakin, Daddy yabi bayanta da kallo, har yanzu Salma tana nan da gayunta da iya kwalliya, nan ya dinga tuna abubuwa da dama da suka wuce a baya.

Wanda zasu yiwa Hanan rakiya tuni sun shirya dan yiwa Hanan rakiya can gidan Jawwad dake babban birnin tarayya, Hanan tasha kuka, da kyar aka banbare Hanan daga jikin Mummyn ta, daddy yayi mata nasiha Sosai, suka hau motoci sukayi gaba.

Da kyar Maama ta takura Jalila ta ci Abinci aka bata magani, Karfe dayan rana Aka gama kintsa Jalila da Nana, suka fito domin tafiya, Jalila ko ganin gabanta batayi saboda kuka.
Tunda su Jalila suka fito Jalal ya sauke idonsa akanta ta rame sosai ga idanuwanta sunyi Jawur, gaba daya tausayinta ya kama shi, ko ya takeji a ranta oho? Sosai yake jin tausayinta a ransa.

Yadda Jalila da Nana suke kukane yasa jikin Maama yayi sanyi, shikenan Nana zata bar kasar se lokaci2 zata dinga ganinta, duk kiyayyar da tayiwa Jalila a baya, bata taba zaton zataji babu dadi haka ba, Zatayi missing din yarinya me kara da kawaici, ga Jawwad shima ze tafi, zasu bar mata gidan se ita kadai, yadda Jalila ta rirrike Maama tana kuka kamar mahaifiyarta yasa Maama ta kamu da matsananciyar kunyar muzgunawaa Jalila data dinga yi, ba tayi aune ba taji itama Hawaye na bin idonta ta kuma rungume Jalila a hankali tace “ki yafemin Jalila” . Jalila ta kankame Mama tana cigaba da kuka

Abba yace

“haba in kina kuka zaki karya musu gwiwa ne, kiyi hakuri, ki gode Allah da ya nuna miki Aurensu kuka rabu lafiya”

Antyn Jalal tace

“Ai dole tayi kuka, kowace uwa haka takeji a lokacin da take bankwana da ‘ya’ yanta, yaranta uku zasu tafi su batta lokaci daya, maman Hanan ma tana can ta nayi”
Daddy yace

“ya za’ayi se hakuri”
Haka aka sa su Jalila a mota, ana musu fatan Alkhairi.

Mota daya Jalila, Nana da hajiya Salma suka hau, kanin Mahmud ne ze jasu, sekuma tawagar Angwaye da sauran ‘yan uwansu dazasu biyo bayansu, Hajiya Salma tace Jalal ya biyosu a tasa motar, Jalila naji na gani suka ďaga suka nufi borno.

Tunda aka kira Ahmad aka bashi hakuri akam Aurensa yarasa ina zesa ransa yana matukar kaunar Jalila, sannan duk yadda zeyi yaga Jalila be samu damar yin hakan ba har suka tafi.
Yusuf kam ko sallama beyi musu ba saboda bacin ran abunda akayiwa Aminin nasa, haka kurum an hana mutumin kirki an bawa wannaan sakaran.

Daddy ma ya shirya kayansa tsaf, yayi musu Sallama ya koma kano, yayinda Abdallah ma da tawagar abokansa suka tafi yi masa rakiya kaduna kasancewar a can ze zauna.

Tuni Labari yafara karade unguwar su Nana cewar an ďaura Auren Jalal da Jalila, da yake Akwai wanda sukayiwa Maama kara sukaje mata biki ‘yan anguwarsu, Labari ya zaga unguwa inda wasu suke ganin an kwari Jalila da aka Aura mata wannan mara tarbiyar dan shaye2, bayan ita kamila ce, me kirki da faran faran ga kowa, Amma duk abun nan ba wanda yaje ya Tari Mummy ya gaya mata.

Bayan la’ asar Daddy ya je gida, da ya koma gida be gaya mata ba, seda yaci Abinci yayi wanka yai salla.
Suna zaune da Mummy tana ce masa “ya hanya? Ya kabaro su?
” lafiya kalau Alhamdilillah, Jawwad da iyayensa suna godiya “
Ya mike ya debo goro da alawowi dayawa ya zube a gabanta.
Ta kalleshi tace
“wannan kuma na menene? “
” Na Auren ďanki ne”
“ďana kuma? Wanne ďan nawa, daza’a abani wannan kayan haka?”
“Aike yaran naki ukune, ga Jawwad, ga Mahmud, ABDUL JALAL”
“Jawwad din dai, Mahmud ba ďana bane, sannan ba wanda ya isa yayiwa Jalal Aure ba da izinina ba, idan ma anyi ko ‘yar uban waye se an fasa shi, kodayake wace mace ce zata yadda ta Auri wannan ďan naka?”
Daddy yace “to shikenan tunda baki yarda ba”
Ya dau remote ya kunna tv abunsa. Ta shi tayi tabar masa palourn ta koma dakinta, tunani ta fara yi, tasan daddy da zolaya wani lokacin, Amma kamar in serious tone yayi maganar, tana cikin tunanin ne wayarta ta fara ringing, seda ta kusa tsinkewa hankalin Mummy ya kai kan wayar taje ta ďaga
“Salamu Alaikum”
Mummy tace “wa’alaikum salam, hajiya Rahama barka da yamma”
“yawwa Mummy ya gida ya taro?”
“taro kuma?”
“Au tambayata ma kikeyi? Baban su yacemin ;yaje ďaurin Auren ďan gidan Alhaji Usman a bauchi, ashe bayan na Mahmud har dana Jalal amma baki gaya mana ba, na miki magana ta what’s App bakiyi responding ba”
Ai Mummy bata jira me zata karasa cewa ba ta kashe wayar ta kunna data aikuwa messages suka dinga shigowa ana mata Allah ya sanya Alkhairi, wasu na mata mitar bata gayyacesu ba, jifa tayi da wayar kan gado ta nufi part din daddy
“dama dagaske kayiwa Jalal Aure ba da izinina ba? Akan me? Saboda me?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button