ABDUL JALAL PART 2

“in baki ci ba, zan kwana da yunwa ne, kuma ni inajin yunwa sosai, tunda aka fara biki bana samun cin Abinci fa, se Ulcer ta kamani ko?”
Yai maganar a ďan shagwabe, dariya ya bata tace
“in Ulcer ta kamaka ba rabin zamce ai, Dama haka ka iya shagwaba, wallahi tayi maka kyau”
tai maganar tana dariya, cikin hikima yanayi ya namata hira ya dinga bata kazar tana ci, seda suka kammala, Jawwad ya jagorance su sukayi Sallar nafila, domin nuna godiyarsu ga Allah da kuma fatan zaman lafiya me dorewa a cikin Rayuwar Aurensu.
Se Hamma take tana lumshe ido, da alamun gajiya da kuma bacci a tareda ita, Jawwad ya kalleta yace
“Wannan hammar da kike karki hadiyeni mana”
Tayi dariya ta Mike, tana cewa “gara in hadiyaka in huta ai”
fita Jawwad yayi domin rufe kofofin gidan, da kuma tabattar da komai lafiya.
Hanan ta canza kaya, ta nemi guri ta kwanta, wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita.
Cikin baccin nata ne tana kokarin yin juyi ta jita a jikin mutum, a hankali ta bude ido tace “Haidar”
“My love” ya amsa mata
“bakayi bacci ba?”
“Banyi ba”
“meyasa?”
“ina tunani ne”
“Nasan me kake tunani, be wuce su Jalila ba, ni na gaya maka komai ze wuce, zasu koma normal, Jalila tana son Jalal, kawai dai kasan ta da taurin kai”
A jiyar zuciya yayi, ya kuma kwantar da kansa a jikin ta yace “Naikaina na san Jalal yana sonta sosai, daga baya na yadda da maganar ki soyayyar ‘yan uwatanka ne tsakanina da ita, hankalinta akan rayuwar Jalal take, a tunanin ta tausayinsa take ji, amma da haka sonshi yayi mata illa bata sani ba, kaman yadda ban fargaba naki son yakusa karasani”
Ya kai bakinsa kunnenta ya rada mata
“I Love you my Hanan”
Makalkale shi tayi tace “I love you too Haidar”
Daga nan hirar kuma ta canza salo zuwa wani abu na daban, tun Hanan tana daurewa tana biye masa, taji abun ya wuce tunanin ta, ta fara neman taimako, ‘yan gidan su ba wanda be sha kira ba dama an hadu da uwar shagwaba, A wanna daren Jawwad ya saukewa Hanan wannan rawan kan nata.
(nima me rahoto naga abun yafi karfina dan haka na dawo da baya, na fito ????????????????????)
Gaba daya Nana ta takurawa Jalila da waya, har sha biyun dare tana manne a waya seka ce wata mara aikinyi, haushi duk ya ishi Jalila tana ganin ta fiye zakewa, ji ta ke kaman suna karama ta takaicin da take ciki, ta ja bargo ta rufe har kanta dan ta dena jin abunda Nana take fada.
Washegari tunda safe Su Nana suka fara haramar tafiya.
Wayar Nana Jalila ta karba sukayi waya da Maama, har daki aka kawowa su Jalila breakfast, Nana kanta ba ta sake taci ba, saboda gaba daya ji take ba dadi, zata daga tabar kasarta ta haihuwa Aure kenan.
Karfe sha dayan safe su Nana suka gama shirinsu, suka shirya domin tafiya airport, nan ma seda aka sha daru Da Jalila saboda kuka, haka sukayi Sallama Nana da Mahmud suka tafi.
Hajiya Salma bata bisu ba ita seda ga baya zata koma.
Bayan tafiyar Nana Jalila dakin ta koma ta kwanta gaba daya ji take duniyar tayi mata fadi, ba abokin hira an kawota inda ba wanda ta sani. Ta lura nan gidan Antyn Jalal ne, tana da yara ‘yan mata guda biyu, daya zata girmi Jalila, Husnah da Amal, Amma sam basa san mutane basa shiga harkar mutane, dan haka ko sannu bata hadasu da Jalila, sedai sukan gaishe ta.
Hajiya Salma ta shigo ta samu Jalila a kwance tace “Jalila har yanzu jikin ne?”
Jalila tace “A’ a naji sauki kaina ne kawai be dena ciwon ba”
“ko dai likita za’a kira”
“A’a Anty naji sauki”
“to shikenan, Amma Jalila ki kwantar da hankalinki, ki cire duk wata damuwa a ranki, Kicigaba da raguwarki kaman yadda kike yi a da kinji”
Jinjina mata kai kawai Jalila tayi.
Koda Hajiya Salma ta fita dakin da Jalal yake taje, yana zaune yana kallon labarai a tashar CNN.
“Sannu Jalal kana nan kana kallo, kai ko tambaya matarka bakayi, ka sameta a sauki, dan haka baka damu da ita ba ko?”
“to me zance? Kokuma me zanyi? Nima ai bata nemana”
“Au hakama zakace ai shikenan, yaushe zaka koma?”
“gobe insha Allah”
“zakaje kano ne kokuwa?”
Jalal ya dan yamutsa fuska yace “daga nan gurin aiki zan koma, bazanje Mummy ta hargitsa min kai ba, lagos zan wuce”
“Shikenan Allah ya kaimu goben” Jalal yace “Ameen Amma, se yaushe Zaku bani ita mu koma kano”?
Hajiya Salma tace
“ita wa kenan?”
“Matata mana” ya bata amsa
Hajiya Salma tace “au ashe matarka ce, baka da kunya Jalal, se lokacin dana shirya yayi tukuna, ashe dai ka damu da ita”
Dan dage kafada yayi irin i don’t care din nan.
Jalal idan ya tuna yadda Jalila ta ce bata sonsa a gaban kowa da kowa, yana tunanin wani irin zaman Aure zasuyi? Tsawon lokacin nan dama bata taba sonsa ba kenan? To meze sa ya cigaba da bibiyar ta tunda tace bata sonsa.
Bayan Hanan tayi sallar Asuba komawa tayi kan gado, wani wahalallen bacci ya kuma dauketa. Koda Jawwad ya dawo ya tarar ta koma bacci, ya hau kan gadon ya ďan tsira mata ido, baccin ta take hankali kwance, tuno darun da tayi jiya yayi, ya danyi murmushi ya janyo ta jikinsa ya kwanta shima baccin ya dauke shi.
Wajen karfe tara Jawwad ya tashi, Amma Hanan bata farka ba, ya je ya dafa musu tea ya fita, ya fita ba dadewa Hanan ta tashi daga baccin, taje tai brush tai wanka ta saka wata doguwar riga mara nauyi, ta fito parlour amma bata ga Jawwad ba, ta nemi guri ta zauna a kan kujera, befi mintuna goma da fitowarta ba se gashi ya dawo hannunsa dauke da kaya, yayi sallama ta juyo ta amsa suna hada ido ya kashe mata ido, hakan yasata sunkuyar da kai tana murmushi, ya karaso ya ajiye kayan yace
“good morning dear, kin tashi lafiya?”
“lafiya kalau, kaima ka tashi lafiya?” tai maganar tana kokarin kaucewa hada ido da shi
“lafiya kalau na tashi lafiya, How was your night?” ya kuma jefo mata tambayar.
Pillow ta dauka ta rufe fuska tana murmushi haka Jawwad ya cigaba tsokanarta yana bata kunya.
Ya dakko cups yana kokarin hada musu tea tace “Haidar waye ya dafa tea din nan?”
“ni na dafa” ya bata amsa
“Allah yasa dai baka bari yayi kanzo ba, dan na san baka iya girki ba”
Dariya ta bashi sosai
“Ai nafi ki iya girki in gaya miki, zaki kuma gani”
“to ai shikenan hada min yunwa nakeji”
“Ai wannan tea din nawane ni kadai, bazaki sha ba ke kazarki zaki warming a oven ki cinye”
Zare ido tayi tace
“gaskiya bazan ciba na koshi”
Jawwad yayi dariya yace
“se kin cinye ta kuwa”
“aikuwa bazan ci ba, tsaya in baka a baki” ta dinga bawa Jawwad Abinci a baka, yana bata haka sukayi breakfast cike da kulawa da kaunar juna.
Wunin ranar yau Jalila ji tayi duniyar ta kara mata fadi, ga har yanzu Bata kuma sa Jalal a idonta ba balle ta sa ran karbar wayarta.
Bangaren Jalila ma tunanin ta yaza’ayi tayi zaman Aure da Jalal be damu da kansa ba balle ita, tana ganin shima an cusa masa ita ne kawai baya sonta, banda haka kwanan su nawa da zuwa be nemeta ba ga rashin lafiya tanayi amma ko keyarsa bata gani ba balle tasa ran ze mata sannu.
Ko parlour bata fita tana ďaki, Hajiya Salma da Antyn Jalal suna monitoring din Jalal da Jalila domin ganin actions dinsu, Amma abun mamaki kowannensu yana nuna be damu da ďan uwansa ba, tunda sukazo kwana uku ba wanda ya nemi wani a cikinsu.
Antyn Jalal tana zaune suna hira a parlour su Husnah suna cin Abinci Jalal ya shigo, su Amal suka gaisheshi a ciki ya amsa, dan sun fidda ran ze amsa musu, suka cigaba da cin Abincin su.
Anty tace “Jalal ina zuwa haka?”
“Zan koma lagos ne”
Anty sukayi ido hudu da Hajiya Salma.
Hajiya Salma tace “to wannaan tafiya haka kaman wanda ake kora? Ka gayawa matarka yau zaka koma?”
Cikin ko in kula yace “in kun ganta ku gaya mata”
Anty tace “dan kaniyarka mu zamu gaya mata ka tafi, Anya Jalal ka shirya rike yarinyar nan?”
A ransa yace “ita zaku tambaya in ta shirya zaman Aure dani?”