KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVEL

motansa yahau ya Shiga gari kawai ya samu wani ice cream palace ya zaun plan kawai yake nema yanda zaici ub*n minal Ba tare da mom ta gane ba. Lokacin rufewa ne yayi masu wurin suka masa magana kamin ya fita.

Daidai ya tsaida motansa a cikin gida idea ta fado masa murmushi yayi tareda danna kai cikin gidan.

Minal kam sanda ya fita aranta tace kai wannan oga sir din Anyi masifaffe ni inyazo ma wulakanci zan kafta mai. Wani zuciyan yace dubeki saikace zaki iya tuno kallon daya mata kamin ya fita tayi atake ta tsure ta kidime yanxu ya zatayi gashi mom zata tafi ta barta waiyo Allah.

Kwanciya tayi abinta sanye da kayan jikinta gyalenta kawai ta cire kamin tayi baje baje atsakiyar gado tana yaba laushin katifar. Allah sarki har tayi missing din tsohuwar gadonta da yar karama da katifarta.

Around 1 yazeed din ya dawo so direct ya shigo dakin minal domin aiwatar da aniyarsa kallonta ya tsayayi yana yaba kyanta.
Aranshi yace mutum ga kyau amma Ba hali money monger

Concentrate yazeed Karka bari kyanta ya rude ka idan Ba haka Ba bazaka iya cin ub*nta Ba 

Alokacin minal ta Dade da Shiga duniyar mafarki Wai tana baccinnan yazeed yazo ya caka mata wuka sannan ya binne gawanta a bayan gidan.

Wani wawan juyi minal tayi acikin baccin dama ita A ne wajen style din bacci ta iyasu kala kala dankwalinta ne ya zame gashinta ya bude dama ta cire ribbon din sanda zatayi alwala

Tsaki yayi aransa yace mata halinsu daya ka Duba iyayenta basuda karfi sosai amma sanda tasa wig mai tsada. Ko ina ta sami kudin? Wata zuciyarsa ce tace masa ka manta barauniya ce ko yar 419?

Bubbuga gadon yayi fiskansa babu alamun wasa domin ya daura aniya kuma sai yayi…….

Toh fa ko menene aniyan yazeed? Fans me kuke gani yazeed zaiyi?don’t forget to vote and comment your ra’ayoyi.

Miss untichlobanty💕
23rd September, 2019.
[1/11, 1:54 AM] Mzz_Untichlobanty💞: 🏆🏆KURUCIYAR MINAL🏆🏆

🌹@mzz_untichlobanty🌹

CHAPTER 27

Juyi minal tayi tace inna bacci,Wai har asuban yayi ne?

Haushi abin yabawa yazeed hakan yasa ya wantsalar da pillow din da take kai,aiki babu shiri ta mike ganin shine yasa taji wani faduwar gaba yazo mata

Tunda take arayuwarta bata tana jin faduwar gaba irin wannan Ba kuma bata taba jin tsoran wani Kamar yadda tsoron yazeed ya shigeta a yanxu Ba.

Wani irin kwarjini yayi Wanda tayi nadamar kallon idanunsa domin kuwa ko lokacin da suka fara haduwa bata kallesa da kyau Ba

Wani kirma jikinta ya fara ta fara karkarwa Kamar mejin sanyi.

A hankali muryatta Kamar zatayi kuka tace sannu da zuwa.
Wani kallo yazeed ya mata Wanda yasa hanjin cinkinta kadawa kamin yace uban Waye yabaki izinin kwanciya akan gadonnan? Wato anzo ansami banza ko shine kikayi yi relaxing kina bacci ?

Da izinin wa kikayi bacci? Tayi shiru…
Bakida kunnene ko yaya?muryanta na rawa idanunta ya cicciko da hawaye tace kayi hakuri yace will get down zaki sauko ko saina taka ruwan cikinki?

Babu bata lokaci ta diro saga kan gadon yayinda tayi kneel down run kafin a bata umarni yazeed ko Ba tare da ya kalli inda take  Ba ya taka ahankali cikin takunsa na kasaita da isa amma cikin kuzari Wanda zai nuna maka Cewa shidin wani jarumi ne kuma namijin duniya

Har izuwa bakin gadon ya isa sannan ya zauna ya cire hularsa me mugun kyau da tsada sannan ya ajiyeta a gefe

Dago kansa yayi yanaso ya karewa minal kallo amma hakan ya gagara sabida kirjinsa dake bugamasa da Sauri da Sauri amma dai baikai na minal Ba sai ya dauki hakan amatsayin baccin rai  

Dan haka sai ya jingina Kansas da allon gadon yana mai lumshe idanu Kamar yadda yayi scan baya sanda ya fara haduwa da ita a gidansa.

Minal ko gabadaya jikinta yayi sanyi,ta sadakar Dan ita a ganinta Allah ne yake ramawa mutane irin tsiyar data musu sanda take gida.
Tayi tsuru tsuru da ido Kamar Mara Gaskiya,gabadaya jikinta ya jike da gumi ga wani fitsari ga zazzabi ya sauko mata tsabar rudewa.
Dukkanin shikashikan tashin hankali ta cikashi a halin domin ko hawaye sun Dade da fara safa da marwa a kumatunta bakinta ko yayi mata nawi ko hakurin ma takasa badawa sai tsilla ido take tana kallon kafafunsa Wanda Duke dake da Zara zaran yatsu da kuma gashi kwance luf luf akai.

Sanda suka dauki kusan minti goma a haka kamin yazeed yace sannuki da zuwa cikin masifa da bala’i hade da tashin hankali.

Minal Kam ta kasa dabbaka Komai Dan ita ko a film bata tana ganin irin yanayin  da tashiga Ba ganin take ko yaushe ma ziciyarta zai iya bugawa ta mutu zaboda yadda yake bugawa har cikin dodan kunnenta takeji

Abubuwa dayawa ke yawo azuciyar yazeed Wanda yana fahimtar wasu,Wasu kuma baya fahimtar su

Ba tare da buds idanunsa Ba yace kinsan ni soja ne jarumi kuma naga alamun kinason zama dani,kuma kinsan jarumi sai jaruma,Dan haka kamin infara considering dinki a matsayin matata sai kin cika wa dannan sharudan

Shiru ne ya biyo baya kamin yazeed yace ;
Na farko daga yau ke zakinayin dukkanin shara,moping,dusting, wanke-wanke,inkika saba wadannan to zan hada mini da wankin mota da safe sukuma masu aikin zasuyi girki da sauransu da yamma kuma zakiyi sharan bangarena sannan zaki dafa abinci kuma ni Vance ki kawomin jagwalgwalonki Ba.

Na biyu karki sake koda wasa ki na ganki a Inda nake domin ganin fuskarki kadai nakanji Kamar zanyi amai

Na uku abinda nace kiyi agidannan su kadai zakiyi idan kina neman izinin yin wani abu to ki rubuta a paper ki ajiyemin ka kibi duk umarnin da matata zata baki saboda marabarki da yar aiki shine darajar mom

Na hudu karki sake mahaifiyata tasan da wannan maganar idan Ba haka Ba to kin kusa ki bakunci barzahu

Hope kin gane ta gyada masa kai yace bakida bakine
Tace na gane

Yace good idan kinbi wannan dokokinn to zaki zauna lafiya amma idan kika saba to kema kinsan sauran.

Sannan ban yarda ki kwanta akan gadonnan Ba harsai naga how serious are

Itade taji bazata kwanta a gadon Ba sauran kuwa to kunde San sauran .

A hankali ta bude bakinta tace oga sir Dan Allah idan na cika sharudanka zaka sakeni yayi shiru kamin yace hakan ya ta allaka da yanayin biyayyarki may be in sakeki
Yana gama fadan haka ya tashi ya fice wani nauyayyan ajiyar zuciya ta sauke tare da sakin numfashinta Wanda bata masan ta rikeshi Ba sannan ta goge hawayenta sannan tadau bargo ta Komai kan kujera ta kwanta tare da rufe kafafunta

Yazeed kuwa yana komawa dakinshi yayi wanka tare da brush sannan ya fito dressing room dinshi ya Shiga ya dauko pyjama dinshi blue tare da Rigan ya saka sannan ya haye gadonsa ya kwanta yana mai lissafi yanda rayuwa ta kasance masa

Hakadai bashi yayi bacci Ba sai wuraren asuba koda ya tashin sallahn asuba Kansa yayi masa mugun nauyi hakadai ya daddafa yayi sallh yayi azkar yau ko karatun Qur’ani bai samu yayi Ba ya koma bacci. Dama Ba kullum yakeyi saboda yanayin life.

Minal ko tunda tayi asuba taje kitchen ta nemi kayan aiki aiko batasha wahala Ba ta samu ta kama aikintakarfe 8 cif saiga su atine da su larai sun shigo sukaga babu kayan aikinsu parlour suka leko jin motsin mutum aciki aiko  da gudu gudu Sauri Sauri suka karaso

Atine tace Allah sarki yar uwa yaushe Rabin da mu ganki ziyara kika kawo manane ko wajen hajiya kikazo kika bage da aiki saide kash hajiya ma jiya da daddare tabar kasan itada danginta kinsan fa mai gidan ya karo aure
Duka atinen ta fada a numfashi daya zuwa biyu Asabe ta kara da ya karo wulakanci Ba larai tace baza’aji mutuwar sarki abakina Ba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button