KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVEL

Ke er lele dama kina jina kikai shiru to abincin ki zaki dauka she didn’t reply inna rather all she did was sip water from her tiny blue cup

Inna tace er nan Ba lafiya Dan a yadda nasanki ko bata maki rai akayi baki wasa da tuwo amma yau ko motsi bakiyi
Ta fadi hakanne ayayinda take taba goshin Amina Dan inna ji take Amina batada Lpy domin ita bata wasa da tuwo

Jin ko magana batayiba yasa inna ta fita ta samu baba ta labarta masa abinda ta gani baba ne yace rabu da ita zamu hadu atakaice de ranan Amina bataci abinci ba.

Washe gari koda Amina ta tashi tayi shara da wanke wanke ta gama koko,
Sai wajen karfe goma ta tuna da Cewa zata raka zahra anguwa tashi tayi tasa hijabi taje dakin inna tace inna ni zan tafi gidansu zahra tace zan rakata anguwa

wani kallo inna ta watsa mata kamin tace shine gaisuwan ki ?

Amina tace mantawa Nayi ina kwana
Inna tace rike abinki
Sannan a haka zaki rakata anguwan kai Innalillahi aminatu yaushe zaki canza yau kwana uku kenan bakiyi wanka kuma a haka kike tunanin zaki samu miji ki Duba kullum in zahra zatazo gidannan kwas da ita amma ke a birkice

Since bakin zaninta tayi ta miko mata Dari biyu ki siyo sabulu da tirare dan d’uri da sabulun gashi kinji

Bubbuga kafa Amina ta fara haba inna zan bata mata lokaci fa
inna tace to wallahi inbakiyi abinda na fada Ba babu Inda zaki mutum sai shegen kazanta Allah ma daya taimaka bakida karnin kashi ai da mun mutu

Turo baki tayi tana guna guni har ta siyo ta dawo
Inna tace maza Shiga wanka ki wanke kanki sai kizo in miki kitso saura kiyimin gardama ma babu inda zaki
Subul subul tayi Kamar yadda inna ta umarceta ta shiga ban dakin shiru shiru babu ita babu labarinta inna tace wai me kike yine har yanzu kinsan dai jiranki nakeyi ko?

Fitowa tayi gefen kanta duk kunfa inna tace ke haka ake wankar duk dadewannan nanki baki daurayu Ba? Bata ko kula innar Ba ta shigewarta daki ta goge kan sosai ya zama saura damshi sannan ta zauna aka mata kitson ta dauko kayanta mai Dan haske ta saka sannan ta Dan shafa man baki sai tayi dass da ita.

Tana fitowa inna tace ko kefa amma ace mutum bayason wanka minal tace inna kwana biyu ne fa inna tace kaji banziya ko kunya bakiji har kina daga murya gararin makota suji

Tace to Nide na tafi tana fitowa Zaure ta hadu da baba tace baba ina kwana yace Lpy a’a aminatu ce haka ko bake bafa amma ace mutum kullum……………

Tace to baba ya isa mana tunda Nayi wankan yace yauwa er gari kinga in kina Dan kwalliyan nanne zaki samu miji ko Ba haka ba
murmushi tayi ya miko mata naira Dari yace na sanki da awara watakilla shi zakije siyowa ko innan ki ce ta aike ki
tace a’a gidan su zaliha zani zan rakata anguwa Dan auntyn ta ya karye kuma zamu tayata gyaran gida dashi ke basu Dade da kaura wannan gidan Ba
Baba yace Toh sai kin dawo amma karkiyi dare tace Toh kamin ta fita tanayi masa godiyan kudin daya bata

Tana fita tace Kamar baba yasan banda kudi wlh

Abangaren YAZEED kuwa yau ana shiri da mitimiyar domin bataje office Ba,
Ya Shirya musu evening outing zaliha anci ado makeup kamar ya zubo daga fiskanta attachment dinnan ba’a magana sai harhada rai take wai ita adole batason raini(nace uhm shi baice zaki rainashiba sai ke?)

Taku daidai take har ta iso gaban wani Mercedes Benz sai yauki take alokacin YAZEED ya Dade yana jiranta domin yace shi da kanshi zai tuka su kuma bayason escort na soldiers ko daya.

How is the novel?is it good?any suggestions?

Ramadan Mubarak and happy sallah in advance

2nd June 2019

Show some love

Mzz untichlobanty💕
[1/11, 1:30 AM] Mzz_Untichlobanty💞:

🏆🏆KURUCIYAR MINAL🏆🏆

CHAPTER 8

Tana shigowa ya kunna mota domin yaji haushin bata masa time da tayi domin he values time so much. Tafiya suke a hankali babu Wanda ya kula kowa

🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹

Abangaren minal kuwa ta isa gidan su zally ta sameta tana kwalliya an rike mirror da bakin eye pencil sai zana girannan ake baki wuluk abin abin dariya

‘Daka mata duka tayi a cinya
Kinga abinda kika jawomin ko? kullum in zakije anguwa saboda iyayi sai kinyi kwalliya kinsa inna ta Mani kitson dole ta sani kwalliya.

Sai alokacin zally ta kalle ta tace kawai kice kinyi kwalliya kinaso ki nuna mini  shine zaki fake da guzuma ki harbi karsana!
To wallahi bashi dukannan.

Minal tace wannan ke ta shafa sannan ta zauna tace kinsan yau Dana hadu da baba a Zaure na dauka duka na zaiyi saboda tabarar danayi musu a gidan

Ga mamaki na bemin maganar Ba kuma harda bani kudi
zally tace iye lallai kwalliya ta biya kudin sabulu,wato haduwar taki har akan baba tayi tasiri, yo ina batun su babba?hararanta minal tayi taci gaba da cewa amma matsalata dake ko kwalliyan baki iya Ba kinsan mu yan boko kuma wayayyu anaso adinga yin make up mai kyau amma kin wani shafa powder da man baki

Minal tace iye sannu wayaiya yar boko.
Zaliha tace ke nifa zan cigaba da karatu domin suleiman yanason inyi karatu har kudin WAEC ya biya min a wata makarantar private kuma yace zai Nayi mini lesson in munyi aure.

Minal tace lallai ma yarinyarnan wato haka zamuyi dake? tafiya makarantar gaba zakiyi ki barni?

Zaliha tace a ah zama zanyi in jiraki harsai kin zama farfesiya

kallon zaliha minal takeyi yayinda zalihar taci gaba da kwalliyarta.

Can zaliha tace ni yanzu banida burin daya wuce in Tara kudin Indan siya man kara haske Dan ba’kina yayi yawa wallahi.

Minal tace man me?! Sauri zaliha tayi ta rufe mata baki tace toh sannu sarkin karadi so kike iya taji ko?

Tureta minal tayi tace to in tajin ma ai haka akeso ni ban taba Sanin bakida hankali bama sai yau,ke bakisan Cewa butulci wa Allah bane ace yayi ki baka kice Wai bakinki yayi yawa ? Kin FISA sanin daidai ne? Kuma ai koba Komai mayukan blitin dinnan yana ‘bata fata bara kij,i kuma iyada lahani sosai saima kinji ciwo in yaki warkewa zakiyi bayani.
Karkiga ke baka ce wallahi wani zai iya mutuwa akan bakar mace kuma wallahi sai kiga fara ko a kafa aka daura masa sai ya kunceta.
Kima godewa Allah kinada kyau farare nawa ne munana?mtswww!

Ajiyan zuciya zaliha ta sauke kamin tace kuma fa maganar ki Gaskiya ne waje daya kika kwafsa Ba man blitin akace Ba bleaching ake Cewa. minal tace Koma menene Nide tashi mu tafi.

Zaliha tace Gaskiya kizo na Dan miki kwalliya minal tace Wanda Nayi ma ya isa.

Tace shiyasa bazaki taba samun saurayi Ba ki Duba ki gani kafin a tsaida lokacin aurena samarina dayawa

Amma ke wa ya taba miki kallon birgewa ma

Shiru minal tayi kamin tace kuma fa hakane wato shine sirrin baki taba fadamin Bako,Allah ya isa

Zaliha tace ai shiyasa kullum inna ke miki fada akan wanka baki gane Ba

Minal tace to me mike jira zana mini ado Yan mata

zama tayi zaliha ta shafa mata Jan powder aka zana girannan akayi mata Layin baki da green

Yadda Kasan er tashe

Fitowa sukayi zasu tafi sukayiwa iya sallama tanata kodasu Wai en matanta zasu haska titi

Koda suka fita zaliha ta ballawa Amina harara tace er uwa matsalata dake baza’a taba iya gyaraki Ba kaf duniya Ba Wanda zai iya in aka gyara nan sai asamo wani matsalan

wannan wani irin tafiyane?
Minal tace me matsalar tafiyannawa ?

zally tace kinga yanda ake tafiya yanga ta soma Kamar talotalo (lol karfa kuce ina kushe characters dina zasu Waye, just for entertainment ne 😂😂)

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button