KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVEL

Kara turo bakin tayi kamin ta fara aikinta.

Bayan ta gama aikin zata fita yace karki batamin lokaci ki Shirya yanxu tace Toh

Tana fita shima ya Shirya cikin shaddarsa sky blue sabuwa fil da ita,ya feshe jikinsa da turare sannan ya kafa hularsa dinkin buhariyya amma mai tsadace saide bana almubazzaranci ba.

Chas ya fito dashi Kamar shine angon sannan ya fito domin har 1 tayi kuma 2:30 za’a daura auren.

Koda ya fito bai ganta ba Dan haka ya nufi part dinta dai dai ta rufe kofar kenan juyowarta keda wuya sukayi karo kallon kallon su kayi for what seems like eternity kamin yazeed yace muje ko? Tace yo Toni ka sakeni kullum sai kana wani rirrikeni sai kace na maka kama da yar iska.

Dalle bakin yayi yace ba kace banson jin wannan Kalmar ba? Tace toni Toni…..sai tayi shiru yace toke me? Tace babu kayi hakuri sakinta yayi sannan ya kamo hannunta suka fito.

🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹

Lukman ne rike da takalminsa a Hannu yaji wani mummunar faduwar gaba.

Hazbiyallahu wa ni’imal wakil yace sannan ya goge black covered shoe dinshi ya fara sawa.

Sanye yaje cikin farar shadda kal harda babbar Riga wadda zubinsu kusan daya Dana yazeed ne. Kallon karshe ya karayiwa dakinsa daya banbanta Dana sauran kuratan sojojin yayi domin tabbatar da komai tsaf yake sannan ya fice domin shi da yazeed su halarci daurin auren Suleiman da zaliha. Sauri yayi ya rufe kofar dakinsa yana mai Cewa bari in hanzarta kafin uban complain dincan ya fara.

Koda ya Shiga motar da zasu tafi

Ya share kusan 30 mins amma shiru babu alamarsu Dan murmushi yayi yace sh*ge mutumi na yana can ya makalewa yar mutane in Anyi magana yace bayaso.

Nazarin irin kirkin abokin nashi ya fara tun Daga gidan daya canzawa parents din minal da gudun muwar kayan dakin daya yiwa zaliha da yadda ya hadawa sulaiman dinma lefe ya bashi dukda ko dakyar da sudin goshi Sulaiman din ya karba sannan ya Sanar da ahalinsa yazeed dinne yamai suko sai godiya suke Suna sa masa albarka.

Jin an bude motar yasa ya Dan firgita tare da Cewa sannu da fitowa amarya.
Yauwa sannu ina wuni ta fadi hakan Adan kunyace.

Yace lafiya ya gidan da maishi?
Bata amsa ba yazeed yayi knocking glass din window din lukman din. Lukman dinma ya fahimci matsala Dan haka ya fito ya bude masa kofar sannan ya Koma.

Koda suka Shiga yazeed yace shine Dan wulakanci zaka tsaya kana yiwa matata wannan surutun naka ko?lukman yace sorry sir! Yazeed yace kai ni karka wani cemin sir sai kace saniya.
Dariya minal keson yi amma ta cinyeshi.
Yazeed yace ke ta juyo yace kinsan wannan? ta gyada kai,yace wayeshi tace driver dinma ne yace Toh point of correction amini nane.

Zaro ido tayi zatayi magana yace rikewa kanki tambayoyinki Dan bazan iya a amsasu ba, kai luku muje dayan wajan.

Kunna motan yayi domin ya gane me yazeed ke nufi sannan ya figeta a guje minal bata shiryaba ta rungumo yazeed tana zazzare ido shiko wani sanyi gabobinsa sukayi Kamar ammasa wanka da ruwan sanyi.

Gaba daya abinda ya faru jiya ke tariyo masa tsab aiko yanayinsa kana daya ya sauya cikin kankanin lokaci. Lukman ko yana ganin duk abinda ke wakana Dan haka ya kara wuta yana mai kunshe dariyarsa.

Minal kam kunyace ta rufeta amma wallahi bilhakki da Gaskiya bata sakinsa dan gani take Suna raba jiki zata mutu saboda a 120 luku ke tafiya kuma dai kunsan motocin yanxu da shegen gudu.

What do you think of this chapter?

Inane yafi yi muku dadi?

Thank you and don’t forget to vote.

Miss untichlobanty💕

8 November, 2019.

5 – CHAPTER 41-50
[1/11, 2:22 AM] Mzz_Untichlobanty💞: 🏆🏆KURUCIYAR MINAL🏆🏆

🌹@mzz_untichlobanty🌹

CHAPTER 41

A haka har suka iso sabon gidan iyayen minal, itakam ta rufe idonta kyam sai laftawa lukman da yazeed din kwandon Allah ya isa take a zuciyarta Dan gani take hada baki sukayi domin suyi mata mugunta.

Yatsa yazeed yasa ya dungure mata kai yace ai saiki sakemin Riga ko? Duk kin yamutsa Min Riga sai kace na fito Daga filin kokuwa, ko jikin nawa ne bai isheki Ba?

Bude ido tayi da sauri tare da hade fiska ta zabga masa harara kasa kasa tace sai kace wani abin arzikin ne ajikinnasa.
Yazeed yace me kikace zaro ido tayi tace babu aranta ko Cewa tayi Wai wannan mutumin aljanine ?taya akayi yaji me nace?
Wani smiling yazeed yayi yace matar aljani muje ko?
Wani numfashi me karfi taja ta zaro ido tana kallonshi tama kasa motsi.

Tabe baki kawai yayi ya fice sannan ya miko mata hannu ganin kawai kallonsa take Kamar taga fatalwa yasa ya fincikota suka fara nufar cikin gidan hannu cikin hannu.

Kallonsan kawai ta cigaba dayi shikam gabansa yake kallo yana murmushi Wanda ya rasa dalili, Ashe luku ya Ciro wayarsa yana watsa musu photo dan Ba karamin kyau sukayi Ba Kamar sune Amarya da angon.

Juyowa yazeed din yayi Dan ganin kallon yaki ya kare aiko tayi saurin kauda kai tana kyafta idanu cikin jin kunya. Aiko lukman ya kara hasko su Wanda su duk abinda ke faruwa basusan anayi Ba.

Koda suka Shiga gidan dauke da sallamar su suka zauna. A lokacin minal ta lura gidan mai mugun kyau ne. Yaba kyawun gidan take taji wata murya wadda yayi mugun tsoratar da ita dan batayi tsammanin wannan muryar anan ba. Saurin kallon wajen data jiyo murya tayi aiko Ba karya kunnanta sukayi mata Ba tabbas innarta ce sanye da super mai kyau ta kashe daurin dankwali tayi haske sai murmushi take kamin tace wanake gani haka? babban bako dan albarka zuwa Ba sanarwa ? Allah ya taimaka akwai abin naka ba bari inkawo ma.
Ah ah kace min tare kake da malam lukumanu. Murmushi yayi yace wallahi inna tare Mike ina wuni?…… Nan suka gaggaisa inna tace malan lukumanu irin wannan babban Riga haka sai kace ango Sosa kai yayi yace wallahi daurin auren classmate dinmu zamu.
Inna tace ayya Allah ya Sanya alkhairi.

Ganin Kamar inna bata lura da minal dake sankare scan kuryan parlourn Ba yasa yazeed Cewa inna bakiga bakuwar ki bane sai lokacin inna ta juya aiko minal ta gani tayi kuri tana kallon ta.

Inna tace ja’irar ‘yarnan kina kallona bako gaisuwa?minal kam mikewa tayi ta fara takowa wajen innar ga mamakinsu sai ta rungumeta ta fashe da kuka haka aka lallasheta tace inna banganeba innan tace kwantar da hankalinki wato……………..

Nan tayi mata bayani duk yadda akayi sannan ta kallo yazeed din tace baka fada mata bane? Murmushi yazeed din yayi yana kallon kasa yadan gyara hularsa sannan yace wallahi dama surprising dinta nakeson yi.

Inna tace dakyau aiko ta sufarasu dayawa harda kuka.
Turo baki minal tace bafa safarsu bane suprisu ne. Hararar ta inna tayi tace o ni ‘yasu mai hali bata chanja halinsa, kice min bata chanza zani. To mike ki shige nan kofar ta bangaren hannun daman ki akwai  firji cikin akwai sobo ki dauko. Acikin drawer akwai tray saman canter kuma akwai cup ki dauko musu Toh tace sannan ta mike ta nufi kitchen din.
Koda ta kawo so’bon suna sha inna sai hira suke da yazeed da alama sun shaku, minal kam abubuwan da suka faru da ita ayau Nada wuyan shanyewa lokaci guda.

Mikewa su yazeed sukayi Suna Cewa zasu wuce lokaci na kurewa,minal din kuma sai su tafi gidan bikin tare da inna tunda itama innar zata Kamar yadda tace.

Wajen suka fita inna tace bazaki raka mijin naki bane? Tashi tayi akunyace tabi bayan su koda lukman yaga ta fito mota ya Shiga yana Cewa bari in bada guri kar adaga mini hankali da rana tsaka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button