KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KURUCIYAR MINAL COMPLETE HAUSA NOVEL

Ina matukar kaunarku! Daga taku KARAMARSU BABBARSU

Miss Untichlobanty ?

5th April, 2020.

[4/10, 20:39] Miss untichlobanty Writer: ??KURUCIYAR MINAL??

?by miss Untichlobanty ?

INSTAGRAM : miss_untichlobanty
WATTPAD : miss_untichlobanty
TWITTER :miss_untichlobanty
TIKTOK: Untichlobanty

?CHAPTER 80?

RECAP

Yace tofah, ummu ai baki sanar dani cewa amina taki batada kunya ba ashe uwar tsiwa ce. Wani kallo minal ta aika masa ta ajiye kosan a gefe ta dafa kasa ta Mike. Wato za’ayi cakwakiya kenan, daidata tsayuwarta tayi ta dun?ule hannu wata Mata dake keken abinda ke faruwa ta window tace tooo, ashe aminar ba ta arziki bace wannan aminatun yar jagwal ce.
Atake kan minal ya Sara ‘aminatu yar jagwal’ ke Mata yawo akai kamin ta yanki jiki ta fadi.

CONTINUATION

Mikewa ummu amina tayi tana rafka salati tace na shiga uku aminatu lafiya? Fallawa saurayin Mari tayi tace kai ilu me kayi Mata? Uwani ta Kira ta taimaka Mata suka shiga da minal cikin gida.

Sabi yana karyo kwana yaga taron mutane, baya baya suka fara ja lokacin da suka lura yana tunkaro su. Ashar ga danna yace kai me kukeyi anan wajen? Yaran ne suka ruga da gudu yayinda samarin suka watse suna gunguni? su kuwa Mata yan tasha yan gulma suka dinga Watso magana ta batanci. Matar nan dake leke ta window tace kai sabi’u bamason iskancin banza, kai da uwarja bakuda aiki sai hada tarzoma. Yatsa ya nuna Mata yace ke talatu billahillazi la ilaha illa huwa idan kika kuma kirana sabi’u zanci… tam.

Kofar gidan su ya bankade da kafa har sanda ta karye ya shiga tun daga zaure yake dannawa mahaifiyar sa kira. Ummu! Ummu! Ummu! Tace kai wai lafiya kake Kira na haka sai kace kana bina bashi dalla ka fice kaje ka tuya mini kosai banson shirman banza.
Yace ummu ba nace kar na dawo na samu yarinyar nan a cikin gidannan ba? Tace tunda kai ka haiho ba. Wallahi sabi idan baka fice ka toya kosan nan ba zan fito daga dakinnan in ci maka mutunci. Uwani tace waikai sabi bakada tarbiyya ne? Mahaifiyar ka tana magana kana mayar Mata yace ke uwani babu ruwanki, kuma idan rashin tarbiyyar ne ai gara akan danki.

Juyawa yayi ya fice yana fadin mutane sai shisshigin masifa ko uban me ya kawota gidan oho. Kuma wallahi idan ba’a cire wannan yarinyar a gidannan ba zan muku hauka zan muku bari.

Koda ya fito zama yayi a kujeran yana suya yana banbami wai tsabar an rainashi za’a hadashi da suya. Wallahi babu abinda zai hanashi ketawa minal rashin mutunci.

??

Safina! Safina!! Safina karki fita a gidannan nace ko. Wacce aka Kira da safina ne ta ja tsaki tare da kada kai tayi ficewar ta.
Motar kawarta dake jiranta a bakin kofa tayi shigewarta tare da cewa babe yau? Sheraton zamu je. Kawarta me suna rafisa tace kamar kinsan zuciya ta Dan naji ance this week akwai guests sosai. Figar Motan sukayi bayan sun sake kida kamar a club.

Suna cikin tafiya rafisa ke cewa gaskiya babe mum dinki bata kyauta miki ace big girl kamarki bazata iya using mota ba? Haba this is not right. Tsaki safina taja tace kede bari ai wata rana saina gaurawa wannan matar Mari.

Reception suka Shiga lokacin da suka iso hotel din nan suka tambaya kuma aka sanar dasu cewa yau akwai baki sannan ma ana party.
Nan suka tafa tare da biyan kudin daki saboda kar a hanasu shiga.
Daki Dali suka fara bi suna kafa kunne idan sunji alamun namiji ne kadai a dakin sai suyi knocking idan an bude sai sugani, idan Dan hannu ne shi da kansa zai musu tayi idan ko ba Dan hannu bane sai su basa hakuri suce batan kai sukayi.

Saide fa yau da matsala Dan basu samu customer ba gashi anfara complain cewa wasu Mata na damun baki.
Shawara suka Yanke idan suka duba room dinnan ba customer toh zasu nufi wajen party ne.
Knocking sukayi ba’a bude ba har suna shirin wucewa sukaji alamun motsi hakan yasa suka gyara tsayuwa tare da sake budo wasu bangare na jikinsu. Ana budewa suka saki murmushi amma me zasu gani ayush ce ta bude kofar. Wani kallo take binsu dashi da yake itama safina tanaji da kanta harara ta mayar Mata. Aiko babu bata lokaci ayush taci kwalarta tare da wulla ta chiki daki. Sauri rafisa tayi itama ta fada tana kokarin ceto kawarta yayinda itama safina ta ci kwalar ayush nan fa dambe ya kaure tsakaninsu suna zagin juna uwa da uba.
? Ganin abin yaki karewa yasa goje shiga tsakani tare da fadin wai sweetheart me ya hadaku fada ne tsawa ta daka mishi tare da cewa banza munafuki wato abinda? kakeyi a bayan idona kenan ko? Wato kanada wasu yan? Mata ko? Safina tace ke munyi miki kama da kananun karuwai irinki ne? Wani kallo ayush ta Mata kamin yace ke shegiya ki iya bakinki wannan din miji nane. Kai kuma…. ta juyo tare da sake kallon goje saide kamin taci gaba yayi saurin cewa haba wifey hotel dinnan fa ke kika kama kuma nasan zakizo toh meyasa zan kirawo yan Mata? Sannan da banida gaskiya bazan bari ki bude kofa ba saide ni in bude ince musu su jirani ko wani Abu. Tace ehhh kuma fa hakane amma ya akayi cikin duk dakunan hotel dinnan sukazo dakinnan? Yace tayaya zanyi na sani? Kallon Safinan tayi tare da cewa karamar ka….. safina ce tayi saurin cewa wallahi kina karashe wa saina tsinka miki Mari. Karuwa tana bin maza ne dan kudi Niko ina binsu ne Dan biyan bukatata. Ni safina Usman nadabo nafi karfin kudi wallahi.

Ayush tace what ke yar gidan Alhaji Usman nadabo ne? Safina tace kwarai kuwa. Murmushi mai sauti ayush ta fara tare da fadin yar uwa ai bakiyi bayani bane da wuri, toh amma me yasa kika zabi wannan harka bayan dukiyan da babanki yakeda shi? Tabe baki safina tayi tace wannan harka ta ce babu ruwanki.? Ayush tace hmm malama safina kenan ai yanzu? batun rigima ta kare a tsakanimu ai mun zama yan uwa dariya rafisa dake kefe tayi tace kai jama’a duniya juyi juyi anayi inajin dadi kamar ba yanzu kuka gama fada ba. Ayush tace kinga babu ruwanki ehe, kawai kina nema ki shiga tsakanin yan uwa.

Safina tace malama ya da sauri haka yaushe na zama yar uwar ki? Ayush tace kede bar wannan sanar dani ansar tambayan ki. Tabe baki tayi tace saboda kawai in biya bukatata. Ayush tace toh kiyi aure mana. Safina tace lokacin da nakeson ayimin AI ba’ayi ba yanzu ko ban bukata Dan na Saba da maza dayawa guda daya bazai isheni ba.

Dan tunani ayush ta shiga yanda zata rike safina Dan idonta akan kudin mahaifinta ne. Aikuwa sai ta tuno lokacin da zakiyya ke raki akan jarabar yazeed hakan yasa tayi saurin cewa idan kuma na samo miki Wanda yakeda komai har wannan fa? Safina tace ai babu bata lokaci zan bar bin maza.
Ayush tace rest your case hajiya ta kin samu bani numbarki kawai. Sharing number dinsu sukayi suna ta jin dadi kowa bukatarsa zai biya sannan suja rabu.

Koda safina ta koma gida carko carko ta Sami iyayenta. Baban ta na ganinta ya daka Mata tsawa ke me sunan mama daga ina kike? Nace cabdi,wannan shine ihu bayan hari. Turo baki tayi tace daddy wai kaima irin momy zaka zama ne? Yace shashashan yarinya ayimin shiru. Wallahi idan baki fito da miji nanda 3 months ba babu ni babu ke. Bubbuga kafa ta fara tare ta haye sama tana fadin lokacin da nace ayimin cewa akayi banida kunya yanzu kuma za’a dameni. Mum dinta ne tace idan kika bari na sameki wallahi zan ballaki.

Kallon Alhajin tayi tace Alhaji kaga abinda nake fada ko lokacin da kake bata ta, tazo tace tanason aure kace Sam sai tayi karatu saboda tayi taking over business dinka. Toh gashi yanzu ita auren ma baya gabanta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button