BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

GOVERNMENT HOUSE

    Tarba ta musamman Alhaji Hameed Harith Taura ya samu shi da Ramadhan a fadar ta shugaban ƙasa, kasancewar tun a daren jiya Bappi ya sanarma mai-girma shugaban ƙasa zuwan Ramadhan ɗin NAYA ta hanyar text Message.
    Duk da tarin liyafar da aka shirya domin Ramadhan hakan bai wani birgesaba, dan tunda suka baro masarautar Bina zuciyarsa bata tare da gangar jikinsa duk da nasiha mai ratsa jiki da mai-martaba da Pa da Bappi sukai masa.
  Sai kuma Raudha dakan faɗo masa a rai. Sai yanzu yake ƙara yarda da hasashensa kan dalilin Raudha na bama Bappi kariya. Dan haka kawai bazata bada ranta akan wanda bata saniba ko rashin dalilin, zuciyarsa na sake tabbatar masa a yanzu abinda tayi nada alaƙa da wannan batun na fitowarsa takara, lallai akwai wani shiri a ƙasa da su Bappi basu fahimtaba. Sai dai wanene ke shiryawa? Akan mi? Akan wane dalili? Duk bai saniba shima. 
  A zuciyarsa yake ayyana. (Inko hakane dolene nabi dukkan hanyar daya dace dan na sani koda kuwa hakan na nufin zai iya rasa raina).
  Taro ne daya tara manyan jiga-jigan jam'iyyar tasu, sai dai gaba ɗayansu sunada masaniya akan son tsayar da Ramadhan takarar. Amma kowa yanada manufarsata ta amincewar kuma. Wani yanki a cikinsu kamar su Alhaji Yaro glass sune suka san ainahin manufar. Sauran kuma suke kallon hakan bisa ƙyaƙyƙyawar niyyar manyan jam'iyyar na kawo dai-daito akan rabuwar kawuna dake neman shiga tsakaninsu a dalilin yawan ƴan takara. Sai dai kuma duk da haka wasun su zukatansu a ƙuntace suke da rashin son Ramadhan ɗin musamman da suka gansa yaro ƙarami saboda mafi yawansu sun haura sittin su, kawai dai basu da ƙarfin faɗa ajine sai ya zam dole suka zuba ido wajen bin gangar yarima asha kiɗa.
  Bayan anci an sha da ga abinda aka tara wanda Ramadhan ko ruwa bai sha ba a wajen suka fara gudanar da abinda ya tarasun. Shugaban jam'iyya da sauran jiga-jigai sukayi bayanai da welcoming ɗin Ramadhan cikin su, tare da fatan zai basu haɗin kai wajen yin aiki tuƙuru da ƙara ɗaga darajar jam'iyya. 
 Ba wani fahimtarsu yake ba, dan sam hankalinsa baya a tare da su. Amma magana da ido da Bappi yay masa ta tilasta masa miƙewa yay bayani shima. Bayan godiya da jinjina a garesu ya tabbatar musu zasu sameshi fiyema da yanda suke buƙata.
 Jin kalmar (fiye da yanda suke buƙata) a bakinsa ya sasu ji a ransu zasu iya juya Ramadhan duk yanda sukeso domin biyan buƙatunsu.....

JIHAR ƊILLO. HUTAWA

        Tunda Asabe tabar gidan gaba ɗaya sai ya koma tamkar wani zararre. Duk masifarta da gantalin faɗansu da baya ƙarewa itaɗin ta daban ce a gareshi. Dan a gidan Asaben ce kawai zata samu abunta ta bashi batare da baƙin ciki ba. Amma ko baba Nafi duk haƙurinta akwaita da halin banza a wani fannin itama. Sai dai nata da sauƙi akan na Larai.
 Da farko Larai tata ƙoƙarin ganin neman auren da Alhaji Maude Dallatu Kema Raudha ya dawo kan ɗiyarta ne Zabba'u. Dan tata lallaɓa M. Dauda akan hakan tare da banka masa rubutu da magungunan malam. Ance tsafi gaskiyar mai shi, dan ta ɗan fara samun kansa harma da manta Asabe da ƴaƴanta da taso yayi, sai dai kuma ba'aje ko inaba aikin ya watse.
   Dan a ranar salla tunda labarin abinda ya faru da Raudha yazo kunnensa sai ya rikice harda kukansa. Ya dinga tsinema Alhaji Hameed Taura akan yaja an kashe masa ɗiyarsa saliha mai addini. Dan kuka rurus ya zauna yanayi a bakin masallaci. Mutane suka taru a kansa anata bashi haƙuri da lallashi amma M. Dauda sai sake ɓare baki yake yana fyatar majina.
  Daga ƙarshe yace inhar anaso yay shiru sai a haɗa masa kuɗin motar zuwa Bingo inba hakaba yata kuka kenan har sai Alhaji Hameed Taura yazo Hutawa. Mutane sun san halin M. Dauda ƙwallon ɗan is.... Ne shiyyasa basuyi ƙasa a gwiwa ba wajen fara haɗa masa wasu ƴan kuɗaɗe. Yai kwanaki biyu kenan kuwa ana haɗa kuɗin a masallaci. Ba wani kuɗin kirki bane suke badawa. Mai hamsin mai ɗari ne kawai, shiyyasa haɗa kuɗin yaɗan ja lokaci duk da sun san zuwa yanzu ya samu fiyema dana motar.
Ilai kuwa a daren jiya aka tattare kuɗin naira dubu bakwai aka bashi harda canji a sama. Daɗi ya sakashi fara godiya yana kuka, harda cewa baisan ana ƙaunarsa a anguwar tasu ba har irin haka. Sudai mutane dariya suka dinga gumtsewa kawai. Shi ko ko'a jikinsa, ana idar da sallar asuba ma ko wanka baiyiba yaje gida ya canja babbar riga kawai, rigar duk ta fita hayyacinta da tsufa da dauɗa amma bai damuba. Dan itace kawai rigarsa ta arziƙi ta ganin shugaban ƙasa. Ya dakwarra wata shegiyar hula da ko wanki babu tare da ita balle sitatin kirki.
 Duk jarabar da Larai taita masa da ƙirƙirar suyi rigima ta lalube kuɗin bai kulata ba, sai ma ɗakko bakko ɗin kayansa data gama shiga uku dan tsufa yay yayi fitowarsa. A ƙofar gida yaci karo da malam Gambo abokinsa. Yay wani gaba kamar zai kifa sai kuma ya dawo baya ya dafe bango yana hangame baki da haɗe fuska.
    “Kai kuma lafiya na ganka anan harda malum-malum?”.
Baki M. Gambo ya washe yana miƙewa tsaye da leda viva ɗinsa a hannu, shi kansa ba ƙaramin a harmutse yake ba, dan har gwarama m. Dauda ɗin ta wani fannin. “Kai abokina ya kake magana haka kamar ka manta ni abokinka ne na amana. Ai bai kamata na barka kaje kai kaɗai ba babu kara. Dole ne na bika muga halin da yarinyarmu ke ciki tare. Mu kuma san matakin da zamu ɗauka akan tsohon nan Taura”.
   Da farko ƙanƙance idanu M. Dauda yayi yana harar M. Gambo Ƙasa-ƙasa. Sai kuma tunawa da yay M. Gambo ya fisa tujara ƙila idan sun sami ganin Taura zaifi ƙwato musu ƴanci. Dan yayi alƙawarin idan Taura bai sauraresu ba gidan redio zai dawo ya masa terere duk da a yau yaji a labarai an sake cewa Taura da jikansa sunje sun sake duba Raudha a asabitin da aka ɓoyeta ana bata tsaro na musamman. Ciwon Raudha ya damesa, amma a ƙasan ransa gani yake silar arziƙinsa ce a wajen. Dan yasan dai baza'a nakasta masa ɗiya a dalilin Taura ba Taura yaƙi jiƙashi da kuɗaɗe. Wannan yanada ɗaya daga son zuwan nasa Bingo...
  “Abokina daina tunanin nan muje da-ALLAH kar rana tayi”.
“A'a ai ba tafiyar bace matsalata M. Gambo, ka sani duk fa abinda muka samo sammaka zanyi ba raba dai-dai zamuyiba. Dan nasan badan ALLAH kake son mini binbinin nan ba.”
  Kamar m. Gambo zaiyi magana sai kuma ya fasa, dan yasan halin buyagin M. Dauda. Lallamashi kawai ya shigayi harya haƙura suka tafi tasha neman motar Bingo.....

BINGO CITY (TAURA HOUSE)

     Komai ya ƙwace masa, babbar damuwarsa hanashi komawa da Pa da Anne sukayi America. Dan Bappi dai yaƙi yace masa komai tunda suka baro gidan gwamnati. Shima ɗin bai yarda ya zauna da kowa ba ya shige ɗakinsa dake a sashen na su Anne. Koda yake bazamuce ɗaki kawai ba. Dan shima tamkar wani part ne na musamman a wajen. Falone har guda biyu ƙarami da babba, ƙaramin an shiryasane kawai dan hutawa, inda glass ne kawai ya rabasa da babban sai labulaye. Sai bedrooms biyu, kitchen, store, dining, da ƙofar da zata sadaka da backyard inda akai wani haɗaɗɗen ƙaramin garden da yasha tsirrai masu ni'ima, ga madaidaicin swimming pool a gefe da akai masa wani style da ruwa ke fitowa ta wani dutsuna tamkar ƙorama. Daga can gefe keɓantaccen wajene da akayi da glass an cikashi da kayan motsa jiki ().
 Duk gidan bamai shigowa wajen sai idan aikosa akai, dan ko baya nan mai kula da shine kawai ke shigowa saiko Bappi idan yanason kaɗaice kansa. Idan kana hango wajen daga cikin falonsa saboda glass ne a bangon saika ɗauka bama cikin NAYA kake ba, dan daga falon kana jiyo ƙamshin furanni dana saukar ruwan dake fita a dutsen nan, ga grass carpet ta ko'ina lamarin ba'a cewa komai.
   A yanzu hakan ma dai a cikin garden ɗin yake kwance bisa kujera irin wadda akan ajiye gaban ruwan nan domin hutawa kawai, ƙafarsa ɗaya a ƙasa ɗaya tana kan kujerar, yayi kwanciyar rigingine ne fuskarsa na kallon sama, yay filo da hannunsa ɗaya yayinda ɗayan ke riƙe da gorar ruwa, ya ƙurama sama ido tamkar yana irgen gajimaren dake yawo ne a cikinta.
 Abu biyune sukafi komai masa kaikawo a yanzun. Maganar siyasa da su Bappi keson tsundumasa batare da shi ya taɓa ra'ayin hakan ba. Sai ɗunbin zargin Raudha da yake ganin tayi komai ne da wani dalilinta kona sakawar waninta. Na ƙarshe ma tana ɗan sukarsa sai dai ba sosai ba, wato maganar aure, babu zancen ƙara aure a budget ɗinsa, dan haka koma ƴar wacece ake son aura masan shi zai gargaɗeta ta bijire ma su Bappi. Dan haka baya ɗaukar wannan babbar matsala........✍

To Ramadhan B. Taura bara mugani koba babbar matsala bace kamar yanda ka ɗauka????????????.

   https://arewabooks.com/chapter?id=629a77b967809ad6daab2109

Chapter 13

BAƘAR INUWA…????????

Da ɗumi-ɗuminsa??????????????????????????????

Please
Follow me
Share
Comments akan abinda ya shige maka duhu.

     _AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar????????????????????????_

YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za’a cike Form ɗin kamar haka: –

Enter your name: (Cikakken sunanki)

Enter your mail: (Email ɗinki)

Enter an username (Sunanki)

Enter your password: ( misali 12341234)

Confirm password: (misali 12341234)

Sai a taɓa Sign Up shikenan an buɗe account a ArewaBooks????????????.

Continue with Google – Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za’a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

Register – Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.

AREWABOOKS LINK kai tsaye

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3

Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App… Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine.

MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER

+234 903 177 4742

Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan????????????????????????.

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
Typing????

Episode 16

……….Tunda mai-martaba ya sako zancen Ramadhan a cikin meeting da yakeyi da ƴaƴansa da matansa a duk irin wannan ranar hankalin Gimbiya Su’adah da Fulani da Adda Asmah yake a tashe. Ba komai ne ya tada hankalin nasu ba kuwa sai jin mai-martaba yace har Alhaji Hameed Taura yayima Ramadhan ɗin mata. A cikin satin nan ma zasu tuntuɓi iyayenta dan baya buƙatar abun yay nisa.
Duk yanda gimbiya Su’adah taso daurewa saboda ƴan uba dake a wajen kasawa tai. Ta ɗago a firgice tana kallon mahaifin nasu. Cike da ƙasaita yace, “Mamana kinada magana ne?”.
Kowa yasan irin son da yake mata saboda sunan wadda taci, dan haka suka shiga ɗan taɓe baki suna maida kawunansu gefe rayukansu fal hassadar jin Ramadhan zai fito takarar shugabancin ƙasar NAYA a dalilin kakansa.
“Abi maganar yimasa matar ne sai naga kamar anyi gaggawa, tunda kaga abinda ya faru a baya kamar ya kamata a bari ya nutsu kafin a sama masa wadda zata dace da shi da matsayin da muke fata zai hau”.
Mai-martaba da ke kallon television kamar bazai ce komai ba sai kuma ya ɗan murmusa. “Mamana banda abinki wace nutsuwa Ramadhan ke buƙata bayan wadda ya samu a shekaru biyar da faruwar rasa iyalinsa. Kece fa kike damuwa da rashin aurensa har kike damuna, yanzu kuma an sama masa kina jayayya?. Alhaji Hameed bazai taɓama Ramadhan zaɓen matar banza ba, sannan yanada iko akansa irin wanda ni bani da shi matsayina na kakansa ta ɓangaren mace. Inaga addu’a da fatan alkairi ya kamata mu masa, dan bazasu taɓa zaɓa masa matar da bazata dace da matsayin da kike kallon ba”.
“Amma Abie….”
Kansa ya girgiza mata. Kafin cikin ƙasaita ya ce, “Na gama magana Mamana”.
Dole tai shiru, sai dai zuciyarta tafasa take tamkar zata kama da wuta. Fulani da bataso Gimbiya Su’adah yin maganar anan ba ta ɗan harareta ta wutsiyar ido itama. Dole tai shiru har aka tashi taron kowa ya koma sashensa.

★★

  “Ammi wlhy bazan amince ba a wannan gaɓar, wai taya za'ace ni da Basheer dake mahaifin Ramadhan bamu isa yanke hukunci akan ƴaƴanmu ba musamman ma Ramadhan sai dai tsoffin nan dake matsayin kakanninsa.”
Gimbiya Su'adah daketa kaikawo a cikin falon hutawa na Fulani ta faɗa cikin tashin hankali. Kafin Fulani tace wani abu Adda Asmah ta amshe rai ɓace.
 “Maganar gaskiya wannan fin ƙargine Ammi. Amma ni ina ganin tun farko harda sakacinmu. Taya zaki sakar musu ragamar ɗanki bayan shi kaɗai ne tilon ɗa namiji a gidan. Daɗin daɗawa shine kuma babba.....”
 “To Adda ya kike so nayi?, bayan kinsan tun daga yayen Ramadhan suka riƙesa suka hanani, wane kalar abune banyiba amma sukai kunnen uwar shegu dani tsoffin nan”.
  “Amma ai basai ta wannan hanyar ne zaki dawo da Ramadhan jikinki ba. Tun a lokacin ya kamata kiyita jan ra'ayinsa cikin hikima shi da kansa zai dawo gareki batare da kin nuna musu koda a fuska ba. Amma ai wannan ƙarfa-ƙarfar tayi yawa. Dan wlhy yanda yakejin maganar waɗan nan tsoffin da mutuwa ke gab da su bayajin taki ma”.
    Tsaki Fulani tayi, hakan ya sasu kallonta su duka. Ta gyara zamanta na ƙasaita tana hararsu. 
   “Kunfa dameni da surutan banzarku. Ku miyasa a komai baƙwa nutsuwa kuyi abun hankali sai shirme. K Su'adah yanzu kamata yay ki lallaɓa musan wacece zasu aura masa. Ni yanzun zan tuntuɓi mai-martaba da batun ƙudirinmu na haɗa auren Aynah da Ramadhan ɗin naji mizaice, duk dai abinsa ai bazaiƙi jikarsa ba ko?. Indai Ramadhan ne a wannan gaɓar zai dawo garemu, dan bazamu amince ya samu mulki su Firdausi su cigaba da juya manashi yanda suke so ba. Shine babban jikana na farko, dan haka nima inason abina”.
   Sosai shawarar mahaifiyar tasu ta ɗan basu nutsuwa, dan haka gimbiya Su'adah ta zauna tana sauke numfashi da ajiyar zuciya....

TK SPECIAL HOSPITAL

     “Kai wlhy idan sama da ƙar zata haɗe yau sai na shiga naga halin da gudan jinina ke a ciki, kajimin mara mutunci. Bar ganin kasa waɗan nan kayan kai tunanin zanji tsoronka, kai fa ba komai bane sai mai gadin gate ɗin asibiti mun sani, ni da kake gani na anan ba ƙaramin tantiri bane, duk wani gidan shege da shegiya dake ƙasar NAYA da mu akai taron bikin buɗesa saboda gawurtarmu a iya shege. Idan kaji ƙarya cigaba da nunamin yatsa kaga idan ban karya shege ba naga miza'ayi min”.
M. Dauda ne ke zuba ruwan bala'i a gaban gate ɗin Tk special hospital. Dan security ɗin gate ya hanasu shiga ciki, shine suka tafi da kokawa akan sai fa sun shiga ɗin. Ganinfa da gaske suke security ɗin ya ɗaga waya ya kira ogansa. Jin hayaniyarsu ta cikin wayar ne ya tilastama Dr Shamsu fitowa da kansa dole har wajen gate ɗin.
     “Kaga matsa masa Daniel”.

Dr Shamsu dake ƙarasowa wajen gate ɗin ya faɗa cikin ɗagama security ɗin hannu ganin su M. Dauda na neman ɓalla masa kunkuru. Dan sun haɗu su biyu sun ƙadandanesa adole sai sun ɗagasa. Ga Daniel ɗin kuma yayi huɗunsu dan su taba duk ta gama ragaɗe naman jikin nasu.
Cikin bin umarni security ɗin ya janye jikinsa yana ƙwafa da hararsu. Suma harar tasa suke da cigaba da kumfar baki har sai da Dr Shamsu ya dakatar dasu.
“Kunga Baba ya isa haka dan ALLAH, mike tafe da ku?”.
Da farko M. Dauda shima kallon sama da ƙas ɗin yay masa zai yaɓa masa bagaƙar magana M. Gambo ya dakatar da shi ta hanyar zungurinsa, shi ya fara magana da sauri.
“Ranka ya daɗe dama munzo duba yarinyarmune da aka jima ciwo a dalilin Alhaji Hameed Taura. Wannan mahaifintane, ni kuma abokinsane kuma ɗan uwansa na ƙut-da-ƙut”.
Dr Shamsu ya ɗan rumtse ido dan shi surutun M. Gambo hawar masa kai yake, a ƙasan ransa yana auna Raudha da wanda aka kira mahaifin natane. Tabas M. Dauda ƙyaƙyƙyawa ne, sai dai taba duk ta gama cinyesa ta sake sakashi komawa baƙi. Idan mai nazari ya nutsu tsaf a kallonsa zai ɗanga yanayi na jini dake tsakaninsa da Raudha, sai kuma kamanin su Fatisa da shi tafi rinjaye duk da suma sun fisa ƙyan gani da ƙuruciya a yanzun.
“Maganar gaskiya bazai yuwu na yarda daku kai tsaye ba, saboda dalilai masu yawa. Yarinyar nan kowama zai iya basaja yanzu domin farautar ranta ko nuna dangantaka da ita domin idasa mugun nufinsa akan Taura. Dan haka kuyi haƙuri idan an sallameta zaku ganta. Dan a yanzu dai babu mai ganinta saboda tana ƙarƙashin kulawar ƴan sanda”.
“Kutt… Bantan uban can kayyasa. Kai awa da zakace bazanga ɗiyata ba. To wlhy yau an taɓo bala’i, ai dama nasan za’a rina shiyyasa na shirya tsaf dan yin kayayatu a gidan redion jaharmu. Zan tafi bazanƙi ba, amma Taura ya saurari saƙona, dama ba’ance mana anji ƙishin-ƙishin ɗin takarar shugaban ƙasa zai hito ba, to wlhy nine zan fara masa ƙafar angulu ni Dauda uban Raudha mijin Asabe baban Ɗanjuma da Garbebe………”
“Ya ALLAH”. Dr Shamsu ya faɗa yana ɗan ja da baya danjin kansa na sara masa bisa surutun M. Dauda. Su Malam Dauda na ganin haka suka faki idonsa suka kwasa da gudu zuwa cikin asibitin. Securitys ne suka rufa musu baya. A taƙaice dai cikin ƙanƙanin lokaci suka nema harmutsa asibitin, sai securitys sukai kama-kamar ɗakkosu zuwa waje. Ganin abun nasu bana masu hankali bane ga marasa lafiya da basa son hayaniya yasa Dr Shamsu ɗaga waya ya kira Bappi batare da tunanin zai ɗauka ba. Sai dai Alhmdllhi tana a ringin na uku aka ɗaga. Cikin girmamawa Dr Shamsu ya gaishe da Alhaji Hameed Taura, tare da jero masa bayanin abinda ke faruwa duk da shima daga can yana iya jiyo hayaniyar.
“Oh ALLAH waɗan nan wane irin mutanene haka? Doctor Please saka wani ya kawomin su gida yanzun nan”.
“Okay Ranka ya daɗe yanzu insha ALLAH ”.
Bayan ya yanke wayar ya dakatar da hayaniyar su Malam Dauda da ƙyar yay musu bayani, amma sai suka ƙi yarda a cewarsu raina musu wayo Dr Shamsu zaiyi dan su bar asibitin. Anyi-anyi amma sunface basu yardaba, babu inda zasuje. Idan gaskiyane shi Tauran yazo ya samesu a asibitin inyaso sai su bisa.
Sosai zancensu yasa mutane sake musu kallon mahaukata. Yo inba mahautaba taya zasuce Taura da kansa, mutum lamba na biyu a masu kuɗin africa, na ɗaya a NAYA yazo nan domin su kawai.
Shidai Doctor Shamsu rasama yanda zaiyi yay, sai dai cikin ikon ALLAH yana tunanin miye mafita sai ga Bappi ya kirashi. Cikin rawar jiki ya ɗauka, ya kora masa bayanin halin da ake ciki. Murmushi kawai yayi da cewa, “Karka damu ina zuwa”.
Idanu Dr Shamsu ya ɗan kwalalo da hangame baki na mamaki, sai dai kafinma yace wani abu Bappi ya yanke wayar.

  Bappi ya ajiye wayar yana duban Ramadhan dake gefensa yana shan furar da Bappin kesha shima, tun wayar farko da yayi Anne ta tambayi lafiya ya mata bayani, amma duk da Ramadhan ɗin na'a wajen ko tari baiyiba, furarsa kawai yake sha yana sarrafa lap-top ɗinsa kamarma baya a wajen.
      “Ramadhan!”.

Bappi ya kirashi a hankali.
Ɗago nutsatstsiyar fuskarsa yayi mai ƙarancin hayaniya yana kallon Bappin, kafin yace wani abu Bappi ya taresa da faɗin, “Tashi muje ka kaini TK hospital”.
Tuni ɗan sakewar fuskar tasa ya ɓace, sai dai kuma babu damar yin gardama, dan shima Bappin ya tsuke tasa fuskar. Cikin marairaicewa ya maida dubansa ga Anne tamkar zai fasa kuka.
“Ni miye nawa kake kallona. Koni nace ka kainin?”.
Ɓata fuska ya sakeyi da janye idanunsa, batare da yace komaiba ya kashe lap-top ɗin ya miƙe, jacket ɗinsa baƙa mai ƙyalli dake ajiye saman kujerar gefensa ya ɗauka ya ɗora saman baƙin wandonsa da baƙar t-shirt, yanda t-shirt ɗin ta kama jikinsane yasa ƙyawunsa da yanayinsa na mutum mai tu’ammali da motsa jiki ya bayyana. Sosai sumar nan tasha gyara yau sai ƙyalli takeyi. Ɗan corridor ɗin dake hanyar bedrooms ɗin Anne ya nufa, ya buɗe wani ƙaramar drawer na glass da aka saka domin ado kawai ya ciri key batare daya duba na wace mota ya ɗauka ba. Dan duk keys ɗin motocin da suke amfani dashi anan sashen nanne wajen ajiyarsu.
“Furar fa!?”.
Anne ta tambaya lokacin da Ramadhan ɗin ke ɗaukar p-cap ɗinsa zai ɗora saman kai, dan yasan Bappi sai yayi magana akan gashinsa.
Hular ya gyara ta rufe masa fuska sosai, ciki-ciki yace, “Na ƙoshi”.
A yanda yay maganar Anne tasan a ƙufule yake, dama yaya lafiyar giwa. Tunda akai masa zancen mulkin nan da aure ƴar sauran fara’ar fuskar tasa ta ɓace ɓat duk da shi ba mutumne miskili ba, maganarce dai sai ya zaɓa da wanda yay niyyar yi saboda jin kansa da yay gado gurin uwa. Gaba ɗaya a kwanaki biyun nan daga gaisuwa babu ruwansa da kowa a gidan. Gashi kuma Ramadhan yayi mugun tsanar driving a rayuwarsa, ita da Bappi ne kawai ke shigar masa hanci akan ya tuƙasu ko yanaso ko bayaso. Amma daya tuƙa mota ya gwammaci ma ya hau mashin, shiyyasa mashina ɗinsa kusan uku a gidan.
Duk da yanda yaga bayan motar daya ɗakkoma key tayi ƙura haushi ya hanashi komawa ya canjo key. Sai Alu ya ƙwalama kira akan yazo ya fidda masa ita daga runfa. Lokacin da Bappi ke fitowa cikin jallabiya dan bai canja kayaba hula kawai ya sanyo saboda yamma ce garin yayi luf da alamar hadari. Ramadhan dake amsar motar a hannun Alu ya miƙa hannu ya buɗema Bappin gefensa, dan yasan in har shine zai tuƙasa a mota baya zama baya.
Koda Bappi ya shigo komai baice masa ba ya ɗaura belt tamkar yanda Ramadhan ɗin ke ƙoƙarin saka nashi, dan shi ƙa’idarsa indai zaiyi tuƙi baya ƙin saka belt ɗin, dan mutum ne mai tsananin son bin doka koda ace sauran ƴan ƙasa na mata riƙon sakainar kashi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button