BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

______________

         Wannan waya itace sanadin hucewar Ramadhan tun a london. Yayinda ita Raudha kenan NAYA cikin damuwa da fargabar karya hanata makarantar daya kwaɗaita mata tunda ya mata gargaɗi tun farko. Gashi gobe idan ALLAH ya kaimu zata fara zuwa monday kenan. Shi kuma yau Lahadi zai dawo kamar yanda ya faɗa kuma aka sanar a labarai. Bilkisu har yanzu tana gidan duk da sanin halinsa ta gwammaci zama harya dawo ta wanke laifin Raudha dan tasan itace da laifi ba Raudha ba. Bata son zama silar haɗa rikicin ma’auratan duk da bata taɓa zama ƙarƙashin inuwar aure ba. Ballema wannan auren nasu na ɗora ɗafini da take ganin matsala kala-kala baibaye da shi, dan duk ƙulle-ƙullen su Maah ta sani bata nunawane kawai tana musu fatan shiriya da ganewa.
      Bilkisun ce ta ƙarfafa mata gwiwa suka shirya masa abinci mai ƙyau, ta kumaje ɗakinsa ta gyaro kamar yanda bily ta nusar da ita karta sake yarda wani yay mata gyaran ɗakin miji da ranta da lafiyarta. Sai kuma tai ƙoƙarin kwashe drinks ɗin da aka zuba masa a fridge duk da bata da tabbacin wannan ɗin akwai guba sakamakon har yanzu wancan kukun bai koma bakin aiki ba ana kan binciken ta yanda aka saka mata ƙwayar zubda ciki tasha kamar yanda taji a bakin Mama Ladi.
       Da taimakon mama Ladi suke wannan ƙoƙarin na canja drinks ɗin a duk sanda aka zuba shi, sai dai ita kanta mama ladi batasan dalilin Raudha nayin hakan ba. Ko data sanarma Anne zancen catai “Bana tunanin yarinyar nan zata cutar da shi Ladi, anya kuwa babu wani abu a ƙasa data sani? Dan akwai wani saƙo da ya zo mana ana gobe ɗaurin aurensu kuma bamu san waye ya aiko ba, da kuma muka bincika mun samo abinda aka nusar damu akansa. Shiyyasa gaba ɗaya gidan gwamnatin nan a tsorace nake zamansu a cikinsa. Amma karki damu, insha ALLAHU munama Ameenatu ƙyaƙyƙyawan zato bazata aikata wani abu na cutar da Ramadhan ba”. A lokacin kai mama ladi ta jinjina tana murmushi kamar tana a gabana, cikin jin sake ƙaunar tsohuwar tace, “Insha ALLAHU Anne”  Daga haka ta yanke wayar, bakuma ta sake maganar driks da Raudha ke ƙoƙarin canjawa ba a duk sanda aka zuba a frighe ɗin sama dana bedroom ɗin Ramadhan.
          Dan haka yanzu ma tare sukayi a sirrance tamkar koyaushe. Daga haka tai wanka ta shirya cikin doguwar rigar atamfa da tai mata ƙyau sosai. Light make up bilkisu ta mata badan taso ba. Sai zuga ƙyawun datai takeyi da ƙarfafa mata gwiwar ya kamata ta koya kwalliya kuma ta dingayi dan tana ƙara mata ƙyau. Ita dai murmushi tayi kawai amma batace komai ba, dan kunyar Bilkisu takeji sosai, bama ita ba ko su Fatisa bilkisu ta girma, amma ita Bilkisun ba ruwanta ta saki jiki da ita sosai tamkar ƙawarta ma. A ranta tana faɗin, (wa zanma kwalliyar? Wannan birkitaccen yayan naku da bai iya komai ba sai jin kai da azabar masifar tsiya yaushe ma na ishesa abin kallo? Yau ka gansa normal gobe bajimin zaki kamar ɗan aljanu).
      Har ɗauri sai da ta mata, ta kuma tilastata suka fito falo suka zauna dan su Lubnah tun randa ya suka fita basu dawo ba wai bikin ƙawar Aynah akeyi suna can gidan Adda Asmah.

     Ita dai zaune take kawai amma badan tana fahimtar abinda suke kallo a television ɗin ba har aka nuna saukar jirgin tawagar shugaban ƙasa Ramadhan da shi kansa. Shine ya fara fitowa lokacin da aka buɗe jirgin. Kamar yanda ya tafi cikin suit haka ya dawo cikinsu sai dai na yanzu sky blue ne, rigar ciki light yellow. Bai sa necktie ba dan maɓallan rigar cikin ma guda uku a buɗe suke.
          Fuskarsa ɗauke take da ɗan murmushi lokacin da yake gaisawa da masu tarbar tasu sai dai bamai tsawwalawa ba. A hankali Raudha ta sauke numfashi tana lumshe ido ganin fuskarsa da ɗan sakewa saɓanin yanda tai zaton gani, ita kanta ta yarda Shugaban Ramadhan ƙyaƙyƙyawa ne kuma ya iya ado, ba duk mace bace zata kallesa ta iya ɗauke kanta batare da taji wani abuba, ita kanta yana mata kwarjini da cika ido, badan ya ɗara sauran maza ko mutane ba. sai dai ita bata taɓa jin son sa ba.
      Sake buɗe idanun tai tana kallon television ɗin, sai dai ranta cike yake da fargaba lokacin da ake nuna ya shiga mota ɗan jaridar na sanar da tahowarsa gida kai tsaye domin hutawa……….✍
         

Idan zanci duka a Zafafa yau, kuyo saurin zuwa ku kwaceni ALLAH. tsabar na hango irin dakuwar da zanyi har ji nake kamar nai hijira zuwa NAYA????????????????‍????

Ku garzaya AREWABOOKS ta link ɗin dake sama farkon page, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp⛹????‍♀️⛹????‍♀️????

ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA????????????????????

1~ KUFAN WUTA????
Safiyya Huguma

1~ BAQAR INUWA????
Billyn Abdul

1~ RAYUWAR MACE????
Hafsat Rano

1~ MASARAUTA????
Miss Xoxo

1~ NOOR ALBI❤‍????
Mamuhgee

Guda 1????300
Guda 2????400
Guda 3????500
Guda 4????700
Guda 5????1k

ZAKU BIYA KUDINKU ANAN????????

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN????????

09166221261


JAMA’AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan????????

Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F

ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA????????

+227 95 16 61 77

TEAM ZAFAFABIYAR????????????????


BAƘAR INUWA…????????

Da ɗumi-ɗuminsa????????????????????????????????

Please
Follow me
Share
Comments akan abinda ya shige maka duhu.

     _AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar????????????????????????_

YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za’a cike Form ɗin kamar haka: –

Enter your name: (Cikakken sunanki)

Enter your mail: (Email ɗinki)

Enter an username (Sunanki)

Enter your password: ( misali 12341234)

Confirm password: (misali 12341234)

Sai a taɓa Sign Up shikenan an buɗe account a ArewaBooks????????????.

Continue with Google – Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za’a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

Register – Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.

AREWABOOKS LINK kai tsaye

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3

Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App… Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine.

MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER

+234 903 177 4742

Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan????????????????????????.

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
Menu
Dashboard
My Library
Create Story
Home
About us
FAQ’s
Privacy Policy
Terms of service
Logout

BAKAR INUWA…!!
Chapter: 43

Share:

Report

BAKAR INUWA…!!
View: 156

Words: 3.1K

Chapter 43
43

………Ta najin shigowar motocin da suka ɗakkosa gidan ta miƙe a ɗan zabure wai zatai fitsari. Bilkisu da tuni ta gama fahimtar a tsorace take tai saurin riƙota tana danne dariyarta.

   “Hi madam! sai fa Brother yaga kwalliyar nan ya shaƙi daddaɗan ƙamshin nan, dan haka babu inda zaki gudu”.

  Fuska sosai Raudha ta marairaice kamar zatai kuka. “Aunty Please, kuma fa da gaske nak…….”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button