BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

    Raudha dai batasan mike faruwa ba. Dan koda Ramadhan ya dawo sukuku baice mata komai ba ita kuma bata tambayesa ba saboda ba daɗin jikin takejiba sam. Ko lokacin da aka kawo su Bilkisu har falonsa suyi sallama a taƙaice ya musu nasiha ya sallamesu. Bilkisu kuwa ta rungume Raudha suna kuka har abin ya bama wasu mamaki dan da’alama akwai shaƙuwa sosai a tattare da su. Ganin abun nasu bana wasa bane Ramadhan ya rabasu da ƙyar ya rungume matarsa duk da mutane dake wajen bai nuna ya san da su ba. Bayan wucewarsu ya jima yana lallashinta, daga ƙarshe ma yasata sukai kwanciyarsu.

      Dan hatta da Aynah ta tare nata gidan bisa tursasawar mai-martaba. Hasalima shi da kansa yay mata rakkiya har gidan mijin nata ya kuma tabbatar ma mijin ko da wasa yaji a ransa zai iya rabuwa da Aynah duk abinda zatai, to lallai sai ya hukuntashi shima bawai ita kaɗaiba.
    To Alhmdllh, mai-martaba ma dan bai san wanene Aminu ba, idan hatsabibanci Aynah takeji ya taketa ya shanye. Idan iskanci ne gidan ta taras.

__________
 
        Har biki ya tashi lafiya kowa ya kama gabansa babu wanda ya sake tada maganar. Sai dai gimbiya Su’adah da jikinta keta sake tsanani duk da kulawar da take samu. Hakama Raudha ciwo ta kwanta sosai hakan sai ya raba hankalin Ramadhan biyu. Ga kwanakin hutunsu ya ƙare dama sati ɗaya ne kacal. Yanda jikin Maah ɗin keta ƙara tsanani ya saka Pa yanke shawarar tafiya taga likitan ta, dan haka randa su Ramadhan zasu koma government house aranar suma sukai shirin wucewa duk da Anne da taƙi yarda Raudha ta koma can gidan sai da Bappi ya lallaɓata. Aka kuma haɗata da su Basma.
     Tasha kuka duk da ita shaidace a yanzu mijin nata ya dawo dai-dai, sai damuwar da take hange cikin idanunsa da bata san ta micece ba. Ba kuma ta matsa da tambayaba tanata masa addu’ar dacewa dai da warwarewar matsalar tasa…
        
          Abubuwa sun lafa sai dai bazamuce duka ba. Gimbiya Su’adah na can likita ya ɗorata a magani, yayinda anan NAYA Addah Asmah keta faman shigi da fici na son ganin an hakala mata rayuwar Ramadhan dama Gimbiya Su’adah kanta duk da ƴar uwartace uwa ɗaya uba ɗaya. Sai kuma auren Aynah da take son rabawa wadda kullum cikin kiranta take tana kuka da roƙon taimakonta tazo Aminu zai kasheta. Dan bashi da aiki sai na mata fyaɗe safe da yamma. Idan taƙi yarda ya naɗa mata ɗan karen duka yayi yanda yakeso kuma. Baijin nauyin shigowa gidan da ƴammata da abokansa susha giyarsu da cocaine. Ya kuma dinga basu labarin abinda tai a America a club, hasalima anan ya fara ganinta har yaji yana buƙatar kasancewa da ita amma ta maresa. Shine dalilinsa na ƙudira aurenta. Ya kuma ɗau alwashin sai ya gama morarta ya saki videon wa duniya.
      Jin wannan zance Aynah tayi kuka tayi roƙo amma sam yaƙi saurarenta. Ta tabbatar masa komi yake so zatai masa akan karya tona mata asiri. Kota kanta bayayi saima ya zauna yayta kwasar dariya shi da abokansa.

      GOVERNMENT HOUSE

      Sukam matsalolin nasu da sauƙi Alhmdllhi, dan Raudha ma ta ɗanji ƙarfi harta koma zuwa makaranta ma. Idan akwai abinda ke damunsu a yanzu bai wuce ciwon gimbiya Su’adah ba. Sai dai kullum Pa na kwantar musu da hankali akan da sauƙi sosai. Hakan naɗan saka musu nutsuwa, har ma yake bama Ramadhan damar shan sharafin soyayyarsa. Duk da kuwa randa ya nuna buƙatar kasancewa da Ustazah ɗin nasa ansha daru. Kuka ta dinga masa da tsalle-tsalle dan ta kasa manta azabar data sha ta ƙarshe. Tunda suka dawo gidan daya tunkareta sai tace wajen bai warke ba ai. Ranar dai ya gaji da yawo da hankalin da take masa ganin zai cutu ya matseta ta ƙarfi ya duba.
    Tuni ta warke abinta zaren ɗinkin ma ya warware da kansa saboda kulawar data dinga samu wajen Anne. Azabar data sha ne kawai yasa take gudunsa. To ranar dai kam duk kukanta bai saurareta ba sai da ya sauke nauyi. Sai dai ya bita a hankali matuƙa yanda har taji nutsuwa tsoronsa ya ragu a ranta bakamar kwanakin baya ba.
     Daga ranar kuma suka sake dunƙulewa waje guda. Dan takai ma ita da kanta tana nuna so saboda cikinta yazo mata da wannan yanayin sosai. Cikin ƙanƙanin lokaci ta sake kara buɗewa tai ƙiba sosai da haske. Shi kansa har baya gajiya da kallonta da kiranta ƴar lukutarsa.
     Da yace ƴar lukuta zata fara masa kukan shagwaɓa ita bata yardaba. Shiko yayta dariya da tsokanarta. Sukanyi waya da Bilkisu kullum, tana kuma cigaba da sake ɗorata akan abubuwa na musamman har gashi yanzu Raudha ta ɗauka sabbin ma’aikata. Mai mata kwalliya da kula da duk wani ado da zatayi musamman idan hakan ta kama akan wata fita ta musamman duk da har yanzu Ramadhan bai taɓa yarda yaje da ita wani taro ba. Sai mai mata gyaran jiki itama. Ramadhan bai hanaba tunda ya san duk abinda zai ƙaru da sune shima ai, to shinema mai ƙaruwar tun school dai kawai Raudha ke zuwa, sannan koda yaushe komanta a rufe.

         Zuwa yanzu cikin Raudha ya shiga watanni na huɗu, ya fito mata ɗan duk da bawani ƙato can ba, wanda ma baida fahimta zai ɗauka tumbi ta fara ajiyewa saboda ƙibar da tayi. A kuma lokacinne gimbiya Su’adah ta dawo NAYA dan likitan riketa yay ta huta sosai acan.
      Ita da shi sukaje mata sannu da zuwa a wani dare cikin fitar sirri. Har yanzu bazamuce Gimbiya Su’adah na ra’ayin Raudha ba. Sai dai akwai sassauci matuƙa a yanayin data amsheta. Harda tambayarta tana lafiya kuwa wannan ƙiba tata lokaci guda haka?. Ita dai Raudha komai batace ba sai ɗan murmushi kanta a kasa. Hakama Ramadhan bai saka musu bakiba dan a ganinsa bai kamata yacema Maah ɗin Raudha nada ciki ba taga rashin kunyarsa a fili. Sai bilkisu ce ta sanar mata Raudha nada ciki ai. Duk da gimbiya Su’adah ta danne yanayin data shiga na farin ciki ƴaƴanta sai da suka fahimta har shi Ramadhan ɗin da Pa, sai dai babu wanda yace mata komai akan hakan.
      Raudha taji daɗin haɗuwa da Bilkisu da itama mijinta ya kawota duba Maah ɗin. Dan tanata son zuwa ma taga gidajen amaren laulayi ya hanata, Ramadhan kuma yace bazatajeba sai taji ƙarfi sosai. Makaranta ma yana barintane dan kar tai asarar abubuwa.
     Sosai Anne ta bata dabarun rainon ciki da shawarwari, tare da mata addu’ar fatan sauka lafiya. Basu baro gidan ba sai kusan ɗaya na dare………✍

Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹????‍♀️⛹????‍♀️????

ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA????????????????????

1~ KUFAN WUTA????
Safiyya Huguma

1~ BAQAR INUWA????
Billyn Abdul

1~ RAYUWAR MACE????
Hafsat Rano

1~ MASARAUTA????
Miss Xoxo

1~ NOOR ALBI❤‍????
Mamuhgee

Guda 1????300
Guda 2????400
Guda 3????500
Guda 4????700
Guda 5????1k

ZAKU BIYA KUDINKU ANAN????????

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN????????

09166221261


JAMA’AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan????????

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button