BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

BAKAR INUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

________________

        A kwana a tashi babu wuya wajen UBANGIJI. Raudha ta cigaba da rainon cikinta cikin kulawar ALLAH da Ramadhan, duk da nauyin Al’umma dake a kansa yana iyakar ƙoƙarinsa gareta itama. Ga gimbiya Su’adah kadaran kadahan tsakaninsu, ba gallazawa babu nuna damuwa. Dan ko Taura House taje zata gaisheta ta amsa ba kamar da ba sai dai iyakar gaisuwarce. Bazata kulataba bazata kuma hantareta ba. Hakama tsakaninta da Aunty Hannah, takan leƙo gidan lokaci-lokaci su gaisa, wani lokacin da mutanenta ƴan siyasa, wani lokacin ita kaɗai sai guards nata. Sau uku tana zuwa gidan Mummynta Asabe. Hakama gidan su Bilkisu dake nan Bingo duk taje. Su Fatisa ne dai har yanzu bata leƙaba saboda ba’anan Bingo suke ba.
      A haka cikinta ya shiga watan haihuwa raki da shagwaɓa ya ƙaru, dole kuma Aunty Zuhrah ɗiyar Yafendo ta dawo nan government House da zama dan Anne dai taƙi hakan duk da kuwa Ramadhan jikane. Tunda watan ya shiga kwanakin haihuwa ta daina zuwa makaranta, sai ta dai su Basma suzo su mata bayanin abinda akayi. Randa takejinta da lafiya ta fahimta, saɓanin hakan tace su barta karatunma baza’ayiba. Sukan mata dariya da tausayinta. Dan hatta uban gayyar idan ta birkice masa da rikici dariyarsa yake kwasa kafin ya koma lallashinta a shirya da ƙyar.
        Tun dai ana saka ran haihuwar har kwanakin da aka bata a sibiti suka gota, koda Ramadhan ya nuna damuwarsa Dr Hauwa tace karya damu ana samun irin hakan ai ba komai bane. Adai cigaba da mata addu’ar sauka lafiya ……….✍

Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹????‍♀️⛹????‍♀️????

ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA????????????????????

1~ KUFAN WUTA????
Safiyya Huguma

1~ BAQAR INUWA????
Billyn Abdul

1~ RAYUWAR MACE????
Hafsat Rano

1~ MASARAUTA????
Miss Xoxo

1~ NOOR ALBI❤‍????
Mamuhgee

Guda 1????300
Guda 2????400
Guda 3????500
Guda 4????700
Guda 5????1k

ZAKU BIYA KUDINKU ANAN????????

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN????????

09166221261


JAMA’AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan????????

Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F

ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA????????

+227 95 16 61 77

TEAM ZAFAFABIYAR????????????????


BAƘAR INUWA…????????

Da ɗumi-ɗuminsa????????????????????????????????

Please
Follow me
Share
Comments akan abinda ya shige maka duhu.

     _AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar????????????????????????_

YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za’a cike Form ɗin kamar haka: –

Enter your name: (Cikakken sunanki)

Enter your mail: (Email ɗinki)

Enter an username (Sunanki)

Enter your password: ( misali 12341234)

Confirm password: (misali 12341234)

Sai a taɓa Sign Up shikenan an buɗe account a ArewaBooks????????????.

Continue with Google – Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za’a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

Register – Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.

AREWABOOKS LINK kai tsaye

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3

Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App… Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine.

MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER

+234 903 177 4742

Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan????????????????????????.

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
     Typing????

Episode 75

………..Alhmdllhi a wani dare na juma’a da yay dai-dai da cikarta watanni goma cif ta farka da gigitacciyar naƙuda. Rikicewa Ramadhan yayi, da ƙyar ya iya control ɗin kansa ya saka jallabiya sannan ya fito kiran Aunty Zuhrah. Da taimakonta suka ɗauki Raudha zuwa clinic ɗin gidan, yayinda tuni su Basma sun sanar ma Anne. Babu bata lokaci a daren Anne da Dr Hauwa suka nufo gidan, inda suka samu har wata Dr ta shiga da ita ɗakin haihuwar. Babu ɓata lokaci Momyn Jafar ta rufa musu baya itama, aiko ta tarar Dr Ingoze na niyyar halaka yaro dama uwar. wata irin muguwar bangaza takai mata tare da sauke mata tagwayen maruka, daga haka ta hankaɗota waje ta koma kan Raudha.
    Kowa yayi mamakin yanda aka hankaɗo Dr Ingoze waje. Gashi Dr Hauwa tace security su rike mata ita har saita fito. Hakan kuwa akai zuciyar su Anne fal wasuwasi. Dama shi Ramadhan suna kawota ya koma ciki kamar yanda Aunty Zuhrah ta bashi umarni. Maimakon zama sai yay alwala ya fara nafilfili da nemawa matarsa sauƙin naƙuda da fatan sauka lafiya.
     Tabbas Dr ingoze tama Raudha lahani, sai dai cikin amincin ALLAH an samu damar ciro jaririn ta hanyar theatre kamar yanda Dr Hauwa ta yanke shawara. Dan ƙarfin Raudha ya nema karewa saboda yanda Dr ingoze ta dinga danna kan yaron yana ƙoƙarin fitowa kafin zuwa Momyn Jafar.
      Sai gabanin asuba suka fito, anci nasarar ciro santalelen yaro gashi ƙato alamar uwarsa taci ta ƙoshi. Sai dai babu damar ganin Raudha har sai ta samu isashen hutu kamar yanda Dr Hauwa tace. Atake murna ta gauraye gidan na gwamnati, kowa kuma nama Raudha fatan samun lafiya. Lokacin da jariri yaje hanun uban gayya Ramadhan hawaye yaji sun cika masa ido. Ya sumbacesa tare da rungume abinsa yana maijin kaunarsa na ratsashi. Wannan shine karo na biyu da ALLAH yay masa ƙyautar da kuɗi basa badata, hakama mulki da ɗaukaka. Ya bukaci ganin Raudha duk da Dr Hauwa taso dakatar dashi ya bata haƙuri, dole aka ƙyalesa ya shiga shi kaɗai ya dubata. Tausayinta ya kamashi, ya dinga jera mata tagwayen kiss’s da addu’oi.

     Zuwa wayewar gari labari ya karaɗe lungu da sako na ƙasar NAYA akan shugaban ƙasa ya samu ƙaruwa. Ga hoton Baby nata yawo saboda su Basma da sukaita turawa ƴan uwa da abokan arziki. Sai yazam kowa ƙoƙarin ɗorawa yake a shafinsa, wasu idan sun gani suma sai su ɗauka daga haka ya karaɗe wayoyin mutane. Yaro yasha addu’oi yayinda ƴammata da yawa suka koka dajin kishin inama daga jikinsu ya fita. Sultana dake ƙasar America kam harda kwanciya ciwo dan har yanzu ciwon son Ramadhan na zagaye da ita. Kawai dai babu yanda zatai ne tunda ya faɗa mata iya gaskiyarsa shi baya ra’ayinta tayi haƙuri ta samu mai sonta..
     Karo na farko, lokaci kuma na farko da Gimbiya Su’adah ta kira waya tasa aka haɗata da Raudha data farka a washe gari da rana. Yajiki tai mata da fatan samun lafiya. Ita dai Raudha abun ma har hawaye ya sakata. Ramadhan dake gefenta yasa hannu yana share mata fuskarsa ɗauke da murmushi.
     Ɗansa dake hanunsa yanata barci ya kalla. Ya shafi lips yaron jajaye yana faɗin, “Ba kuka zakiyi ba Partner. ALLAH zaki godemawa a wannan gabar, ni shaida ne Maah ta jima dayin nadamar abinda tai miki, ta shanye a cikintane kawai saboda nauyin tunkararki. A yanzu kam koda abinda ke faruwa da Lubnah a gidan miji ya isa sake tsoratata”.
     Da mamaki Raudha ta dubesa. “Aunty Lubnah kuma?”.
     Kai ya jinjina mata batare da ya kalletaba ya cigaba da wasa da sumar yaron. “Eh Lubnah. Tun satin da aka kai Lubnah gidan aure bata sake farin ciki ba. Kuskure kaɗan miji zai lakaɗa mata duka tare da ƙanensa. Ke hatta da uwar mijinma ba ƙyaleta taiba itama dukan nata take. Duk da dukiya irin ta gidan su Mansur ƙiri-ƙiri suka sallami kaso ɗaya bisa biyun ƴan aikinsu aikin ya koma kan Lubnah. Cikin ƙanƙanin lokaci ta fita hayyacinta saboda azaba. Ameenatu, tun sanda Lubnah ta kawo Mansur garemu matsayin miji na nuna ƙin amincewata, saboda na jima dajin labarin mahaifiyarsa bata zama da sutukai. Hakama kanensa basu da isashen tarbiya. Amma sai Maah taƙi saurarena saboda Lubnah tace tana son sa akace ai nima wadda nake aure bata dace dani amma suka amsa. Dan haka Lubnah zata auresa ko ina so ko banaso. To ga sakamakonan sun gani, dan yanzu a dalilin dukan da surukar mijinne tai mata tai ɓarin cikin jikinta, maimakon Mansur ɗin yaji tausayinta sai ya maidota gida da takardar saki har uku wai yana zarginta da tarayya da drivernsu kiji sharri. Koda nai bincike uwarsace duk ta tsara hakan kamar yanda take koran matan ƴaƴan itama tai sanadin da za’a korota”.
        Sosai abun ya taɓa zuciyar Raudha duk da zaluncin da su Lubnah suka dinga mata a baya. Ta jingina kanta da kafaɗar Ramadhan tana kallon babynsu hawaye na zubo mata. Shima rungumita yay da hanunsa cikin son kore mata damuwarta yace,
        “Ustazah dawa yaron nan ke kama?”.
      “Dani mana”
Ta bashi amsa tana share hawaye. Ƙeyarta ya ɗan tallara kaɗan. “Son kanki yayi yawa madam. Kowa yaga Abdull-Hameed Ramadhan Taura yasan gida ya ɗakko, mufa jininmu ƙarfine da shi yarinya”.
     Murmushi tayi mai ƙayatarwa da cewa, “Uhm nidai basan cika baki. Dama da Pa kace yana kama ko Bappi sai na yarda”.
     Dariya yay yana mai sumbatar kumatunta. Hakama babyn ya sumbaci goshinsa. “Bakice komai akan sunan dana kirashi da shi ba”.
    Murmushi tayi mai kyatarwa da shafa kumatunsa. “Saboda shine ra’ayina shiyyasa nima”.
      “Woow sweetheart inajin daɗi idan muka kasance bisa tarayyar abu guda”.
     “Noorullah! Idan duk yarana zasu kasance da sunan Bappi ko Pa ko Anne ko Maah ko kai bazan taɓa baƙinciki ba. Fatana dai ALLAH ya bani ikon sauke nauyinka dake kaina ka kuma zamemin miji har a gidan aljanna. ALLAH ya raya Abdull-Hameed Ramadhan Taura ya albarkaci rayuwarsa. Yasa yay gadon ƙyawawan halayen Bappin da Pa da kai kanka”.
      “AMin ya rabbi sweetheart. ALLAH yay miki albarka ya ƙara miki lafiya. Yasa nan da wata shekarar mu sake dawowa labour room…..”
      Da sauri ta rufe masa baki ƙwalla na ciko mata ido. “Wannan ai fatan tsiyane”.
     Dariya ya kyaƙyale da ita yana ture hanunta. Miye na wani fatan tsiya anan ai nasan zaki iya Mrs Taura.
    Haka suka kasance cikin nishaɗi har saida Aunty Zuhrah tazo ta korashi ɗakinsa sannan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button