TAGWAYE COMPLETE HAUSA NOVEL

TAGWAYE COMPLETE HAUSA NOVEL

Ruqayyah ta zabi kuɗi…..ko cikin gidan Baba bai barta ta shiga ba….ko Sumayya bata samu ta gani ba…..

Tun a mota ta fara kuka, kuncin zuciyarta yana karuwa. Tana som family dinta tabbas kuma zata iya zabensu akan kudi idan da ace bata samu nakasa ba, amm yanzu she can’t even imagine herself a matsayin kurma, gurguwa, bazawara kuma talaka. In tana cikin wannan nakasar kuma tana cikin kudi ai da sauki ko? Sai ta samu kanta da questioning choices dinta, shin me yasa ma tayi abinda tayi ne? Me yasa kuma ta tona asirin ta ga Hassan har ta kai shi ga sakinta har kuma ta kai iyayenta suka sallama ta? Yes, tana son kudi, kuma koda yaushe tana yin dogon tunani akan hanyar da zata sami kudin amma yanzu me yasaya zamana kamar kanta ya toshe ne?

A haka ta koma gida ta cigaba da rayuwa, ta tashi ta jawo jiki zuwa palo tayi kallo taci abinci ta koma daki ta kwanta ta kasa bacci ta kuma dawowa palo ta zauna. Sai in ta gaji ta kira kawayenta suzo suyi ta mata hir ta dauki kudi ta basu du tafi. Shikenan. Hatta wayarta takan wuni batayi kara ba. A cikin wata daya sai da loneliness din ya zamanto kamar zai kasheta da ranta. Ta rame tayi duhu kuma ita kanta tasan rashin bacci ne. Tsoro da fargaba dan ko kofa aka taba sai taji kamar zuwa za’a yi ace mata ga Fatima nan ta dawo.

Ta koma gidan su har sau biyu amma ko tsakar gida bata taka ba, kamar Baba yanzu ya daina gadin kamfani ya koma gadin kofar gidan sa. Sai a lokacin ta tuno da malamin duban Minal, sai a lokacin ta samo amsar tambayar da take yiwa kanta na dalilin da yasa ta aikata abinda ta aikata din, abinda malamin duban nan ya gaya mata shine dalili, wannan kudin daya kwadaita mata shine tabi ta kuma dauki zabin da take ganin shi zai kaita ga kudin, kuma ya kaita din. Amm kumaa cikin duban nasa bai gaya mata cewa zata zama musaka ba, ko bai ga wannan ba? Ko kuma ya gani bai fada mata ba?

Sai ta ya ke shawarar komawa gurinsa.

Bata manta gidan ba, ta kwatantawa drivern kuma ya kaita har kofar gidan sannan t fita tana jan kafa ta shiga ta aika aka gaya masa yayi bakuwa kamar yadda taga Minal tayi ranar nan. Akayi mata iso ta shiga har palon da suka zauna ranar nan, kamar babu abinda ya chanja amma komai ya chanja, babu Minal, babu kunnuwan ta babu kafarta guda daya.

Tana zaune ya fito fuskarsa da murmushi ya zauna yana kallon ta “Hajiya Ruqayyah barka da zuwa. Har na fara tunanin ko kin manta da alkawarin mu ne” ta bata fuska tace “alkawari kuma? Wanne alkawari muka yi da kai?” Yace “alkawarin idan aikina ya tabbata zaki zo ki biya ni kudin aikina” tace “ni babu aikin dana saka ka ballantana in biya ka. Ni sanda nazo gidan nan bansan kai malamin duba bane ba da ba zanzo ba ma. Sanda ka yar da charbin ka bansan duba zakayi min ba shi yasa na dauka, da na sani da……” Yace “and yet, you believed what I said” ta tsaya ta saki baki tana kallon sa, ya daga kafada yace “eh, mana. Idan har Abinda kika fada har cikin zuciyarki ne me yasa da na gaya miki maganar kika yarda da ita har kuma kika yi amfani da ita? ” Tayi shiru ta kasa magana, a lokacin ta fahimci cewa wannan shine kuskuren ta a wannan bangaren, yarda da abinda malamin duba ya gaya mata, da bata yarda ba da ba lallai ta kawo idea din yarda jaririn a ranta ba, da bata yarda ba da ba zata yi tunanin wasu options guda biyu ba har ta zabi daya, da bata yarda yaron ba kuma da ba zata hadu da wadannan masifu da suke ta samun ta a jere ba, da bata hadu da masifun ba kuma da ba zata zama frustrated da har zata gaya wa Hassan maganganun da zasu saka ya sake ta iyayenta kuma su sallamawa duniya ita ba.

It all starts here………duk da dai ya tarar da hali.

Ta mike tana jan kafa zata bar gurin yace “baki sallame ni ba har yanzu” ta juyo a fusace “me zan baka ne wai ni? Ka barni da masifun da nake ciki mana kar ka kara min da naka masifar kuma. Wallahi kwandala ba zan baka ba kuma babu abinda zance maka sai Allah ya isa tsakani na da kai” ta sake juyawa sai yace “ina kawarki Amina? Har yanzu ba’a tono gawarta ba ko?” Ta juyo da sauri ta zube idanuwan ta akansa, yayi murmushi yace “yar uwarta tazo nan gurina akan in duba musu ko zanga inda Amina take, na duba kuma na gani, naga mutuwarta, na kuma ga inda aka binne ta” Ruqayyah ta dauke numfashin ta tana jiran mai zai ce sai kuma yace “amma ban gaya musu ba, ina jiran sai kinzo tukunna” tace “abinda ka gani karya ne, in da gaskiya kana ganin badini me yasa baka gayawa Minal cewa ga abinda zai faru da ita ba? Me yasa baka gaya min cewa ga masifun da zasu same ni idan nabi kudi ba?” Yace “ba komai nake gani ba sai abinda Allah Ya banj ikon gani, in kuma na gani din ba komai nake fada ba, ina fadar abinda zai saka mutum ya sake dawowa gurina ne ba wai abinda zai saka mutum ya daina zuwa ba. Idan da ace na gaya miki zaki zama kurma kuma gurguwa ai da ba lallai ki bi hanyar da nake so kibi ba, kinga kuma da ba zaki dawo yanzu ba” ta dafe kanta tana jin hawaye yana cika idonta, sai yace “wannan da jaririn yana nan lafiya kalau, mahaifiyar sa ma kuma tana da rai” ta bude idon tana kallon sa, bakin ta ya kasa budewa balle har tayi masa magana, sai ya dauko wata takarda ya ajiye a gabanta yace “account number dina ce, da kuma adadin kudin da nake so kike turo min duk wata a cikin account din, in ba haka ba zan gayawa yan uwan Amina exactly a inda gawarta take zan kuma gayawa Hassan a inda dan danuwansa yake in kuma bashi labarin yadda akayi yaje gurin. Wannan karon in ya shake ki sai ya kai ki lahira. Sannan Inna da Baba su biki da tsinuwa har cikin kabarin ki. Zabi ya rage naki”.

Wannan littafin na siyarwa ne idan kika ganshi a wani guri na sata ne, in kina son ki sayi halaliyar ki ki yi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020

Ina masu bukatar hadadu kuma ingantatun turarukan wuta da khumra masu dadin kamshi kuma a farashi me sauki to ga dama tazo muku Awwaba scent nada turarukan wuta humra burners kasko shisa coal dorot stool dilka body milk dadai sauransu masu bukatar na iya nemansu a whats app ko kuma kira ta wannan lambar 08034236800
bugu da kari duk wanda ya sayi humra ko turaren wuta a cikin wannan watan akwai kyautar dilka me kyau tafiyaya daga kasar chad wadda zata gyara jiki tay expoliating skin acikin minti 20 kawai ku garzayo dan kwasar garabasa
Adress kundila zoo road kano muna tura sako ko ina da iznin Allah????Her New Life

Ta fara girgiza kanta hawaye yana zuba tana cewa “karya kake walllahi, kai baka isa kayi blackmailing dina ba karya kake wallahi, babu abinda ka sani, kawai kame kame kake yi dan ka mayar dani saniyar tatsar ka amma karya kake babu abinda zaka iya yi min” yace “da gaske? To ki gwada ki gani mana. Nan zuwa karshen wata kar inji alert a waya ta kin ga a lokacin zaki tabbatar da gaske nake ko karya nake yi, zaki tabbatar na sani din ko kuma kame kame nake yi” ta zauna a hannun kujera saboda yadda taji tana neman faduwa tace “azzalumi, mugu, in Allah ya yarda ba zaka gama da duniya lafiya ba” yace “ni wanne zalunci nayi? Ni ban dauki jariri daga jikin uwarsa na jefar dashi ba, kuma ban boye mutuwar aminina ba, dan haka tsakanin ni da ke za’a warware waye azzalumi. Ni sana’a nake yi, wannan aikin duban shine sana’a ta dashi nake samun kudi kuma dashi zan cigaba da samun kudi ta wajen ki, ban jawo kafarki na kawo ki gurina ba da kanki kika zo, da kanki kuma kika aikata abinda kika aikata ni ko shawara ban baki ba, sannan kuma da kanki zaki ke biya na kudi duk wata” bata ce komai ba har ya mike, yana kallonta yace “kar ki manta da takardar in zaki fita” sannan ya koma ta kofar daya shigo.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148Next page

Leave a Reply

Back to top button