TAGWAYE COMPLETE HAUSA NOVEL

TAGWAYE COMPLETE HAUSA NOVEL

A lokacin ne aka turo Ruqayyah daga labor room zuwa dakin hutu, idanunta a rufe aka wuce da ita, sai kuma duk hankulan su ya koma kanta suka bita a baya sai Aunty ta dakatar dasu tace “anyi mata allurar bacci ne saboda ta huta sosai, kar ku shiga kuma ku dame ta” Hassan ya dan shafa kansa yana kara leka inda aka shiga da ita sai aunty ta karbi babyn hannunsa tace “shiga ka ganta, kar ka tashe ta amma ka barta ta hutawar ta Please, yarinyar nan ta sha wahala wallahi” ba musu ya mika mata shi da sauri ya shiga ya rufo kofa su kuma suka zauna a kujerun gurin Sumayya tana shafawa babies din dabinon data tauna suna ta lashewa tana dariya, sai kuma ta dan basu zam zam kadan, Aunty kuma ta dauko waya ta fara kiran yin albishir, Inna Ade ta fara kira ta gayawa, daga inda Sumayya take zaune tana jiyo muryar Inna tana hamdala sai tayi murmushi, Allah sarki uwa. Ko dazu da rana sai data kirawo su ta tambayi lafiyar Ruqayyah. Daga nan kuma sai Aunty ta kira Hussain, bata sami wayarsa ba sai ta kira ta Fatima ta gaya mata tace ta gaya masa. Ita ma tayi ta murna kamar ita aka ce ta haihu, sauran kuma Aunty tace sai gari ya waye tukunna tunda yanzu dare ne. Sumayya kuwa bata bari sai gari ya waye ba tuni ta dauki hoton babies din ta saka a social media. A lokacin nurses suka zo suka karbe su aka tafi dasu aka yi musu duk gwaje gwajen da za’a yi musu sannan aka yi musu wanka aka shirya su cikin kayan da aka taho dasu daga gida.

Hassan yana shiga dakin ya ja kujera kusa da Ruqayyah ta zauna ya zuba mata ido, da ace zai iya hadiye ta dan kauna to kuwa da tabbas ya hadiye tan, ya rike hannunta a cikin nasa, yayi kissing hannun, still yaji hakan bai yi masa ba sai ya sunkuya yayi kissing goshinta, ta dan bude ido kadan tana kallonsa dusu dusu sai yayi mata murmushi yace “sannu Hassana. Allah ya baki lafiya kinji” cikin magagin bacci tace “bana so” yace “menene ba kya so? Gaya min menene ba kya so?” Tace “suna Hassana, bana so” sai ta koma baccin ta. Yayi shiru yana kallonta ammaya kasa judging komai a cikin maganar ta, maybe abinda yake ranta kenan, maybe kuma magagin allura ne.

Bata tashi ba sai da gari ya waye, har Inna da Baba dasu Sulaiman sunzo, yammatan Aunty ma kaf dinsu sun zo kowa yana ta daukan babies ana yabawa. Hassan kuwa baki har kunne ya kasa boye farin cikin sa. Ganin ta farka yasa hankalinsu ya dawo kanta suka yi ta mata sannu tana amsawa sai dai ko yaya ta motsa sai taji gurin dinkin da aka yi mata yana damunta, ganin bata da wani problem ya saka Aunty ta nemo musu sallama kuma a take aka sallame ta suka dawo gida.

Part din aunty suka sauka, anan Aunty ta hada ruwa mai dumi da isasshen detol ta saka ta shiga ciki, “ba za’a saka miki ruwa mai zafi sosai ba saboda dinkin zai iya budewa, zafin ruwan yana iya lalata zaren da akayi dinkin dashi” sannan kuma ta gasa mata jikinta sosai da towel tana fitowa kuma aka kawo mata tuwon kanwa miyar kukar da Inna Ade ta tashi tun asuba ta tuka mata shi ta taho mata dashi, sannan kuma aka kawo mata dahuwar nama mai romon da Aunty tayi mata, sai ta zauna ta ci naman tuwon kuma taki ci.

Tana cikin ci Sumayya ta shigo da babies din ta kwantar dasu akan gado tana cewa “ni fa Ruqayyah banga kin dauki yaran nan ba, ya kamata ki dauke su suji dumin jikin ki suji dadi suma” Ruqayyah ta harari inda babies din suke tace “bayan sun gama bani wahalar? Ai dole duk dan da bai bi uwarsa ba ya hadu da bala’i” Sumayya tace “am glad kin fara fahimtar haka” Ruqayyah ta daga kafada tace “me kuma nayi?” Sumayya ta nuna mata tuwon Inna Ade tace “baki ci tuwo ba, dan ke ta zauna ta tuka shi sannan tayo dakonsa tun daga gida har asibiti har nan gidan amma still baki ci ba” Ruqayyah ta tura baki “ni baki na babu taste ai, ya za’a yi mutum ya haihu a kawo masa wannan bakin tuwon fisabilillahi” Sumayya ta jawo robar yajin daddawan da Inna ta taho dashi tace “saboda tasan bakin ki babu taste shi yasa ta hado miki da yaji dan ki zuba kiji taste din, ga kuma man shanu ta kullo a leda duk dan saboda tasan halinki kar ki ƙi ci. Ki tuna, irin wannan wahalar da kika sha irinta itama ta sha lokacin da zata kawo mu duniya” Ruqayyah ta sake hararar yaran da suka fara mutsu mutsu tace “irin wancan harbe harben fa suke min a cikina, duk sunbi sun duba min fatar ciki na” Sumayya tayi dariya tana zuba mata tuwon tace “kin san fa naji ance tuwon kanwa yana taimakawa wajen samar da ruwan nono ga mai jego, ki samu ki ci ko suma sa samu abinda zasu saka a cikin su” Ruqayyah tace “chafdi, ai kuwa dai babansu dole ya bude bakin aljihu ya siyo madara dan bazan iya shayar da su duk su biyun ba wallahi. Sai an siyo madara an hada musu da ita” Sumayya tace “wannan kuma tsakanin ku ne, ni dai abinda nake so shine ki ci tuwon nan sai ki dauki yaran nan ki basu nono su sha. Kim san kuwa cewa wannan ruwan nonon na farko yellow marar kauri yafi komai amfani a gurin jariri? A cikin sa anti bodies suke, suna sha shi zai zama kariya gare su daga dukkan wani abu da zasu saka a bakinsu nan gaba. Dan haka ko ma ba zaki basu nonon ba kwata kwata ki daure ki basu na farkon su sha”

Da kyar da lallabawa Ruqayyah ta dan ci tuwon Inna kadan, sannan Sumayya ta dauko mata Hassan dinta tace “wannan shine babba, a fara bashi tunda ya riga dayan zuwa duniya” Ruqayyah takarbe shi tana kallon sa fuskarta da murmushi “da babansa yake kama” ta fada tana lakuce masa hanci” saura kuma kayo halin babanka” Sumayya ta zauna kusa da ita hannunta rike da dayan tana kallon yadda Hassan din yake ta kokarin kama abincin sa, tace “mene halin baban nasa? Kirki?” Ruqayyah ta harare ta “so kike yi inyi magana ki fara yi min wa’azi, kin san halin nasa ai”

Sumayya tace “hmmm Ruqayyah kenan. Ruqayyah ki gode wa ubangijin ki. Babu abinda bai yi miki ba a rayuwa. Kin san kuwa akwai matan da babu abinda ba zasu yi ba dan su samu miji irin Hassan? Amma ke kina korafi? Ubangiji bayan ya yi ki mutum mai daraja a cikin halittun sa sai yayi ki musulma wadda aka haifa a gidan ilimi, sai kuma ya baki lafiya, hankali, ya baki iyaye da mu yan uwa masu tsananin sonki, sai kuma ya dauki miji one in a million ya baki, miji kuma mai tsananin sonki sannan yanzu kuma ya baki haihuwa, da kika tashi haifa bai baki daya ba sai ya baki biyu, biyun ma sai ya baki su duk maza, zaman da shi da kansa yace sune zugabanni akan mata. Ko gaya min, which among the favors of your God do you deny?”

Ruqayyah ta saki baki tace “ni yanzu da kike min wannan lissafin me kika ji nace ne?” Sumayya tace “baki ce komai ba, na fada ne dai tun kafin ki ce din” ta mike tana ajiye haririn hannunta sannan ta tattara kayan abincin ta fita dasu.

Da kyar Inna Ade ta lallaba Aunty ta bar ta ta tafi da Ruqayyah gida wankan jego, sai dai ita Ruqayyan ce gaba ki daya ba haka taso ba ita so tayi a barta tayi zamanta a gidanta, ta fara mita “to yanzu in na tafi can Inna kuma wadanda zasu zo min barka kamar sababbin kawayena da matan abokan sa ya zasu yi kenan?” Inna Ade tace “shi ai yasan gidan, sai yayi musu kwatance su je, ke ma kuma sai kiyi wa kawayen naki. Ba kuna waya ba?” Ta kara bata rai “Ni yanzu can din ne Inna ban san inda zanke ajiye baki ba, kuma dakin Sumayya yayi mana kadan ni da yaran da ita, kuma…..”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148Next page

Leave a Reply

Back to top button