GIMBIYA BALARABA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIMBIYA BALARABA COMPLETE HAUSA NOVEL

Gidansu Bushira ta wuce daganan in lokacin tashi daga makaranta tayi sai taje ta d’auko su Sadiya,

Cikin mamaki Bushira taga Balaraba a gidansu tace” hala yau b’atan kai kikayi”
Shareta Balaraba tayi tw shege ciki tana zabga sallama,babarsu Bushira ta amsa tana daga cikin d’aki,tace”kamar muryar Balaraba, Bushira tace”itace mana, “yar rainin hankali”
da murmushi a fuskarta ta shiga uwar d’akin inda mahaifiyarsu Bushira ke zaune a kan ledar d’aki tana ninke kayan sawarsu, tace”Balaraba idonki kenan”

Cikin dariya Balaraba tace”wallahi kuwa Baba ina wuni”?

“Lafiya kalau ya mutan gida,ya kasuwa”?

” Lafiyalou alhamdulilahi”

“Masha Allah” Baba tace tw cigaba da cewa”ko jiyw sai da mukayi zancan ki da mutuniyar taki, tace wai tunda kin gujeta itama bazata k’arw zuwa gidan ku ba”

Dariya tayi tana d’an hararar Bushira dake tsaye tana kallon Balarabar tace”Baba wallahi rashin lokaci ne kinga ina futa da sassafe shiyasa kuma bana dawowa sai yamma, ai ita tasan inda nake a kasuwar me yasa bata zuwa, in ta damu dani”

“Gaskiya kam laifin ta ne”
babarsu Bushira tafad’a tana kokarin mik’ewa kchin tq nufa domin kawo wa Balaraba abunci da ruwa, Bushira ta shaga d’akin sosai tana kallon Balaraba yace”lallai hajiyata kina lokaci wannan jiki haka kinganki kuwa yadda kikayi wani uban kyau da alama babu abunda yake damunki”

Tab’e baki tayi tace”ke wannan ya dama, dallah ni ki zauna kiji abunda ya kawoni, neman shawarw nake”?
Zama Bushira tayi kusa da ita tace”tofa ta samu kenan”?

Ajiyat zuciya tayi cikin tausayin kanta tace”Bushira aure zanyi, nagaji da wannan gararanbar da nake”

Zare ido Bushira tayi tace”wane me sa’a ne yayi dace a zuciyar ki”

Lumshe ido tayi tana murmushi tace”Yusuf kenan mallakin zuciyata fari mai farar aniya, mai kyawun zuciya”

Dariya Bushira ta kwashe dashi ta bata hannu sukq tafa, tace”a ina kuka had’u da wannan me sa’ar ke kuwa”

“Gurin sai da abunci”

Cikin mamaki Bushira tace”na tayaki murna aminyata,amma zanso in ganshi, wanda har ya iya mallakar wannan b’akar zuciyar taki,me shegen muskilanci”

Duka Balaraba ta kai mata, tana shan kunu tace”banason iskanci wallahi,shikkenan daka mutum ya kama kansa sai a dunga kiransa muskili ko d’an wulak’anci”

” Mubar wannan maganar mu koma waccan ta Yusuf d’in yaushe zaizo inzo mu had’u”
Bushira tafad’a tana kanne mata ido d’aya cikin sigar tsokana,

” Yau insha Allahu zaizo ki gama abunda kike sai muje gida tare”

Bushira tace”ai kuwa babu wani abu da zanyi yanzu kawai sai cin abunci sai wanka” “shikkenan muci abunci sai mutafi amma zanje d’auki su Sadiya a makaranta Hira suke irin ta k’awaye Baba ta shigo da kwano mai murfi cike da abunci shinkafa da wake, da man k’uli soyyaye sai yaji a gefe, ta aje a tsakiyarsu Bushira ta mik’e da sauri ta lek’a waje ta kira yaro ta aike shi yq siyo musi lemo na kwalba had’e da ruwan pure watar,

Dawowa tayi ciki, ta zauna Balaraba ta bud’e kwanon abunci, dariya tasa tace”lallai yau nazo a sa’a irin wannan gara haka, gaskiya inason wake da shinkafa a rayuwata, Bushira tace”ai ke dama “yar k’auye ce,sai auki son gayu kina abu irin na gidadawa, wai wake da shin kafa ta6!
Balaraba tace” kema baki san dad’i ba ne”

Yaron ya kawo musu aiken sannan suka fara ci Balaraba taci sosai rabon da tayi k’oshi irin na yau har ta manta, k’arfe d’aya saura sun shirya tsaf, Baba tai musu fatan alkairi suka futa, babu nisa dama tsakanin gidansu Bushira da makarantar sabuda haka a k’asa suke tafiya, Balaraba tace” kin san wani abu kuwa Bushira”?
Bushira tace”sai kin fad’a”
“Humm kwanaki sai ga mutumin ki a k’ofar gidanmu”

“Wanene”?
Bushira tafad’a cikin rashin sani

” Sarki! Almansur”

Tsayawa Bushira tayi cikin mamaki tace”gurin wa yazo”?

” Gurina sukazo shi da Yusuf ya rakoshi”?

” Ke ban gane fa ba kiyi min bayani dalla-dalla, nan Balaraba ta kwashe komai tafad’a mata, Bushira tace”yanzu dai kice Yusuf d’in naki jinin sarauta ne kenan”?
d’aga kai Balaraba tayi alamun hakane

Bushira tace”gaskiya lamarin ki da akwai abun mamaki Balaraba, Allah ya sanya alkairi, yasa za’ayi damu, ina fatan baki masa rashin kirkin ki ba ko”?

“Kinsan sai nayi, sabuda in nace bana son mutum to har abada bana sonsa, sai da na nuna masa bai isa ba, shine ya tofa min miyau d’insa, ni kuma na d’auki alwashin sai na rama”

Dariya Bushira tasa tace”a ina zaki ganshi balle ki rama”?

” Na fad’a muki fa yadda suke da Yusuf,watarana dole mu had’u Bushira tace”gaskiya zanso inga wannan game din naku ke dashi”

Balaraba tace”ni zanso ki gani wallahi ke kin san halina bana manta abu komai dad’ewarsa sai na rama”

Bushira tace” yaya mutan gidan ku sukayi da sukaji labari”?
“Basu sani ba tukkuna”

” Nasan zasu tada hankalinsu, “yan bak’in ciki kawai”

Dariya Balaraba tayi tace”sai dai suyi kuwa in dai nice”
Haka suka k’arasa makarantar suna hirarsu gwanin sha’awa

Daf da zasu shiga gidan suka ci karo da Walidi, ya futo daga lungunsu yace”yawwa Gimbiya dama ke nake jira, ki dawo,na kira wayar ki naji a kashe”
cikin tashin hankali yake maganar

Balaraba tace”menene ya faru”

” Yanzu Kawu ya tafi gurin me unguwa, da goro da alwa,wai yau da asubah a d’aura miki aure da Iro,kan sadaki dubu biyar”

Wani irin yammmm! taji a jikinta jin abunda Walidi yace Bushira tace”anya kaji dai-dai kuwa,ko Shamsiyya a ke nufi”?

” Ya zakice haka abunda a kayi a gabana, wai jiya wani babban mutum ne yazo gurinta,shine yake fad’awa Lantata tace”maza yaje ya siyi goro a d’aura auran da Iro sabuda taga alamun yarinyar jininta na masu kud’i ne”

Balaraba tsugunawa tayi a gurin jiri yana d’ibarta tarasa abunda zatace, Walidi yace”yanzu meye abun iyi ne”
Bushira tace”kaje anjima zamu kiraka” wucewa yayi yana fad’in ina saurare, ni da cewa nayi ko zata gudu ne kawai sabuda nasan tunda suka had’a wannan makircin babu abunda zai hana a daura auran”

“Hakane komai nufi ne na Allah babu wanda yasan mijinta sai Allah, kaje kawai zamuyi shawara”

Tafiya yayi, Bushira ta kamata ta mik’e tsaye suka shiga gida, zama sukayi gefan katifa Sadiya da Usuman suka nufi d’akin Iya domin cin abunci

Bushira tace”ana wata ga wata yanzu me kika yanke”

Wayarta ta d’auko cikin jaka tafara lalubar numbar Yusuf d’in ta fada masa halin da ake ciki, hankalinsa ya tashi sosai yace ta saurare shi zaizo kafin la’asar sukayi sallama

Yana gurin wani abokinshi wanda suke harkokinsu a tare a kasashen waje, lissafi suke na irin ribar da suka samu bayan dawowar shi daga Swiziland , hankali a tashe yayi masa sallama kai tsaye gida ya koma bai zame ko ina ba sai sashen Sarki! suka had’u a farfajiyar gurin, yana tare da Buba Direba zasu fita wata jana’iza yanzu, wanda me Martaba ya wakiltashi, yana sanye da wata alkyabba mai kyau da walwali kanshi ned’i ne irin na sarauta, k’afarshi sanye da wani takalmi mai gashi-gashi yayi bala’in kyau in ka kalleshi sai ka k’ara kallonsa,wasu fadawa ne uku tsaye a bayanshi, tsayawa yayi yana kallon Moddibo har ya k’araso inda yake, fuskarsa ya kalla yaga kamar yana cikin damuwa, yace”har ka gama jin haushin nawa”?

” Muje mota,zamuyi magana”

Tab’e baki yayi kawai yq fara tafiya cikin kasaita, Moddibo yq rigashi zama ciki sabuda yanayin tafiyarsu ba d’aya bace, yana shiga Buba ya rufe motar, ya zagaya da sauri ya zauna a mazaunin sa, su kuma wad’an nan fadawan suka shiga mota guda suna bin bayan motar a nutse

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button