BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,

????????9️⃣????????

DON ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON BA A YAFE BA DON ALLAH KI YI HAKKURI DA HAKKIN WASU, , ,

A kwana a tashi zama yai tafiya saida babu wani jin dadin aure a gare ni kullun zaman hakkuri nake yi garama da zaman gidan mu mai wahala da wanan zaman ukuban da nake cikin sa yazu.
Ko ba komai a gidan mu ina ganin iyayyena ina jin dadi da yan uwa na nan ko haka zan wuni banyi magana da kowa ba na tsawon kwanaki.
Sai da na cika wata biyu cur a gidan ranan yace in shirya zamu tafi gidan su da farko murnan zuwa nayi sai kuma na tuna da abinda yan uwan shi sukai min sai murnan ya koma ciki.
Don yanzu ma ban san abinda zanje na sama a gidan sai dai nasa a raina cewa zan kama kaina da sha, anin su a rayuwa na.
Na shirya cikin cotton lace light green mai yan duwatsu kanana sai hijjab dina da na saka a falo na samay shi yana jiran fitowa na.
Simi simi na fito tare da cewa gani yaya mikewa yayi yana mai kare min kallon muka fita nasan kwalliya na ne bai kashi ba.
Don shi indon ta nashi ne baiki ace na fita ba hijjab a jikina ba ko na yafa dan gyale a kafada na mu fita yafi son na fito yar bariki sahihiyar ta amma ni na kasa yin hakana.
Mun shiga kwanan gidan tun daga nesa muka hango jama , a masu sayen abinci sun cika wurin sai ya dan ja ya mota ya tsaya nesa da gidan na su.
Yace cikin wani murya ke ki saurare ni kiji may zan fada maki dakyau hakan danaji yasa na natsu ina sauraren shi.
Yace bani son naga kin fito waje inda suke sana a ar su din nan kuma ki tabbatar kina saye da wanan abin har mu fito cewa hijjabin kenan.
Duk kika yarda na ganki wurin wanan sana an ran ki zai baci ki kama kan ki da dabiun wurin nan a sanyaye na amsa da to yata da mota muka karasa gidan.
Maza da mata a waje sai cin abinci suke yi tuwon shinkafa miyar ganye da agushi sai kamshi ke tashi.
Tunda muka tsayar da motar mu yan wurin suka sako muna idanuwan su da kallo maza da mata yan duniya.
Nan aka fara yi mai kirari da sunan shi na tan bariki nidai daga kafa nakeyi amma ji nake kamar zaa ce ke in sheka da gudu.
Wani rumfa muka nufa inda gwagon nawa take ciki ga yan matan ta nan gefe daya suna kidayan kudi sunci kwalliya sun kure adaka.
Duk yawan taron nan dake ciki bai hana ni zuwa gaban ta na durkusa ba in gaishe ta sai cewa tayi yau kun ga daman zuwa ku gaida ni koda yake baki da laifi ai ga mai lefin nan gaban ki.
Bai bata amsa ba wata maidan buje tazo ta run gumay shi sai yaja hannun ta sukai waje suna rike da junan su.
Nauyi da kunya suka kamani tace tashi ki zauna dan duniya ya hadu da mashiririta yan uwan shi.
Na juya inda sadiya take ina gaishe su don ko banza sun girmay ni ga shekaru.
A dakile ta amsa mim gaisuwa sai ga wata yar fara mai dan buje tazo da hausa ta gwargwari tana cewa a wanan ne amaryan tamu.
A gaskiya hardguy ya iya zabe mace Allah yasa a zauna lafiya amarya sai hakkuri da mutumin fa don naganki yarinya karama shiko gashi tsohon tazuru.
Cikin wani murya gwago tace da ita salima me i no wan dat wooo sai salima tace sorry ma.
Nace ashe su gwago tsofin bariki ne har da turancin go and come an iya a raina nake fadar hakan wata yar baka mace tazo ta katse min tunane da cewa.
Wai ki shiga ciki inji hardguy saina rashi na bi bayan ta ina jin habiba na mata magana sai dai ban fahinci may take fadi ba.
Ina nan zaune sai gata ta dawo tana cewa may za a kawo maki ne murmushi nayi nace a a barshi na gode a koshe nake ai.
Sai mamakin wanan rayuwan nake mace da auren ta tara kananan yaran mata a gida ana shar holiya wai da suna neman kudi.
Zuwa can ta dawo dauke da abinci a cikin tire tana cewa yace in kawo maki wai kin dade baki ci abincin hausawa ba ta sauke tire din naga tuwon shikafa ne da miyan alaiyahu ya ji agusi da naman shanu tace dani ko baki sin wanan akawo maki na yauki.
Murmushi nai mata nace a, a barshi kawai ko wanan ma na gode ai sai ta kashe murya tana dan waige waige tace mijin kine ya saya maki indon hajiya ne har kizo ki tafi bazakici komai ba a nan.
Kin santa da shegen son kudi koda yake ke bakuwa ne a gidan baki san komai ba tukun tun tafiyan ta ina zaune ni kadai ban kuma taba abincin ba duk da ina son ci.
Can sai gata ta dawo dauke da kwalban coke a hannuta mai sanyi ta dire min tace kina nan zaune ke kadai ba, yi hakkuri dan Allah hajiya bata tasowa yanzu sai ta rarage cinikin ta.
Ina nan zaune sai ga sadiya ta fara shigowa gidan cikim gidan daga wurin sanaar su tace a, a kina nam zaune na ashe.
Murmushi nai mata kawai sai ta dan fara rage kayan jikin ta zuwa can ta kai kallo ga abincin dake aje a wurin sai take cewa a, a baki ci abincin bane.
Aikoda kin ci abincin ki don mijiki yau yana can ya samu yan matan club suna sharholiyan su dama ya dade baizo ba sai yau.
Wani irin naji a raina amma na dake a fili cewa nayi abin da suka sabayi ne yin hankan ya zamay masu jiki ko.
Ko bata fahinci may nake nufi bane sai naji tace min bari in debo mai zafi nazo muci tare tunda naga kina jin kunyan ci.
Nace aida kin bari naci wanan din bata saurare na ba ta fita sai gata ta dawo da wani abincin wanan karon miyar danyan kubewa ne ta debo muna.
Tare muka zauna muna cin abincin muna hira sai na fahinci bata da matsala ita har take cewa dani tankan so zuwa gidan mu amma sai take tsaro kamar nace mata tsaron mai sai dai na kyale ta kawai.
Nan na taya ta sance kanta da ya tsufa da kitsu nai mata wani kitsun duk wace ta shigo ta samu muna kitsun sai ta yaba da kyan kitsun da nai mata.
Nan sukai ta fadan zasu zo in masu kitsu a gidan suma habiba dai ko kallo ban isheta ba sai
A wurin ta nake jin wai yaya saadu yai tafiya dama shi ba mazauni gida bane yana zuwa kasa ibom neman kudi ne a can.
zuwa can gwago na tashigo daka ciki lokacin ina masu shara son ko lokacin gyaran wuri basu dashi.
Kullun ana aikin naiman kudi a waje koma nasu kaca kaca a gidan yake nai ma wurin tas na kama na wanke wa na wanke.
Saida ta samu wuri ta zauna a dakin nata wanda na share kale kale take bin dakin dashi ta kwala min kira ina bakin famfo na amsa nazo.
Nazo na durkusa gabanta sai tace dani kwanaki na aika yaran nan gida ku kikai masu rashin mutunci su da gidan dan uwan su.
Ni har na aika a dibo min dana kice wai barci yake baki tashe shi ke har yaushe kika san dadin miji kega mai miji.
Sai sadiya tace mama na fada maki fa ba haka tace ba tace da sadiya ke rufa min baki yar uwar takine zatai mata karya ko may ?
In dai zurian Rabi ne wani irin tuggu ne basu iya ba matar da kullun cikin kullin sheri takewa kishiyoyin ta ta hana su shakat a gidan.
Na dago kai na kalle ta don jin kallaman da ta fadi gamay da mahaifiyana sai tace eh mana.
Ko kina nufin bansan shirin da kukayi akaina bane dashi kan cewa zaki shigo ki mallake min da sai a baninda kuka ce da ke da uwarki a kan shi.
Na dukar da kaona hawaye na tsiyayo min a fuskana ganin ina kuka tace a hasale karya na fada ke nan ko kina nufin nai maku sheri.
Nace haba gwago wallahi tallahi bansan komai ba akan haka, sai habiba tace wallahi karya kike yi an ina jin ki ranan daurim auren ku wai suna maki huduba
Ita ta fada habiban ta fada haka suka sani a gaba da zagi kamar ba yar dan uwan ta nake ba shi babana yai mata halarci ita kuma tai mai son ranta
Kwasan ya fado dakin kamar wanda aka turo ganin yadda nake nake kuka da rantsuwa a gaban mahaifiyar shi da habiba nata yanka min zagi.
Cikin mamaki yake kallon su ya kalle ni yana son jin abinda ya faru haka suke min masifa ina kwasan kuka.
Sadiyana ta fara mashi bayani sai uwar ta katse ta jikin shi yai sanyi ganin yadda nake kukan da rantsuwa sai zagi suke zubamin.
Ke tashi muje hakana yace dani ya dubi uwar yace muzamu tafi don banga amfanin yin hakan da kuke yi ba .
Simi simi na miki na jawo hijjab dina dake rataye ga igiya na saka ina fadin sai amjiman ku itako gwago sai faman fada takeyi tana cika tana batsewa.
Nan ya biyo ni baya ranshi yana mai suya yasani sarai safiya ba zatai wa yan uwan shi haka ba sheri yaran suka kulla min wurin uwar su tun ranan da yazo ta fada mai ya samani da maganan nai mashi bayanin komai ya yarda
Nika sai faman kuka nake ina tunane a raina wanan wace irin kiyayya ne haka may ne mata a rayuwan ta take shirin nakasa ni.
Har muka isa gida tunanen maganganun su nake akaina may nai mata a rayuwa na take son gani na a cikin ukuba can na nisa nace Allah ya fata duk abinda ya shirya zai samay ni babu makawa sai ya faru dani .
Na share hawaye na na mike zan shiga wanka ya shigo dakin yana fadin may ya hadaki da su habiba ne na ce babu komai nidai a rayuwa na.
Sai yai min wani kallon na sama da kasa yace zanbin cika idan kice baki da gaskiya zaki gane kuren ki.
Yana fita gidan nasu ya koma gwago najin dawowan shi ta samay ta ta cika fam har lokacin don yar ta habiba ta zugata ta zugu akaina.
Yace mummy may ke faruwa ne tsakanin ku da yarinyar nan ina ke kika hada wanan abin bai dace ba kuma ace akwai matsala a atsakanin ku yanzu.
Tace cikin fada kaga rufe min baki don wa nake wanan fadan duk mugun nufinta akan mu dakai mun sani duk sherin da aka kulla azo ai muna gashinan yana fita fili muna gani.
Mummy har wani hali ke gareta wanda baku sani ba tace kai ina zaka sani tunda a boye akeyi don a mallake ka da yan uwanka.
Niko kowaci tuwo dani miya yasha munafuka sai ta dinga yin abu simi simi da ita wai ita ta kwara mugun halin na nan tattare da ita na ta shiga dura mai akidar banza daiyi min wai mun zo da nufin raba shi da kowa kuma nu cinye dan abin hannun shi na gudu.
Tun bai dauka ba har ya fara dauka yana cewa aiko zata gamu dani dama ni ba yarda nayi da wanan yarinyar ba sam.
Sai da ya biya wurin abokan shi ya dawo gida misalin karfe tara na dare ya tarar dani na fito bandaki daure da tawul ya fado min dakin da masifa.
Ke mara mutunci dama na fada maki in na bincika naji baki da gaskitya zan dauki mumunan mataki a kanki watau kun hada baki da iyayyen ki kizo ki haince mu ko.
Idanuwa na suka kada sukayi jawur mamaki da takaici suka rufe min zuciya yace an turo ki anga kudi banza anzo aci ko har a kashe ni.
A hasale na bashi amsa da cewa kai dan Allah har ina kudin yake da za, a turoni tun daga arewa har nan ci ku kudi ya rufe wa ido kudin da ana nema kamar ba neman su akeyi ba.
Kafin in karasa magana na sai naji yakaiwa bakin nawa naushi saida naga wani wuta ya gitta min na duka tare da dafe fuska na.
Nadago nace ka dukeni akan gaskiyata ban karasa ba ya shiga duka na har tawul din dana daura yana sancewa.
Baisa ya daina ba sai da ya barni kwance a dakin ya fito yana maida numfashi daya baya daya ya nufi dakin shi.
Kuka ma kin zuwa yayi min a idona na dade duke a wurin da kyat na daga nakai bakin gado a haka na haye gadon na kwanta cikin dare zazzabi ne ya rufe ni mai karfi saboda zafin bugun da na sha.
Da safe har ya fito ban fito daga dakina ba ya leka ko na gama abin karyawa sai dai babu alaman ko fitiwa banyi ba lokacin.
Ya shigo dakin da niyar yai min fada nan ya samay ni cikin bargo ina rawan sanyi zazzabi mai karfi ya rufe ni.
Da zumar yai min fada ya shigo dakin sai ya samay ni a haka kwance cikin bargo ina makerketa yadan ja ya tsaya.
Ya dade tsaye yana kallona sai ya juya ya fita zuwa can sai gashi da paracitamal da goran ruwa ya kawo min da kyat na tashi ina sha na koma na kwanta.
Wasa wasa sai da na kai kwana uku kwance ina jiyan dukan dayai min tun wanan lakacin gaba daya zaman ya karasa jagulemuna a gidan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button