BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,

????????5️⃣5️⃣????????

NOVEL DIN NAN ONLINE NOVEL NE NA KUDI IDAN KIN SAN DARAJAN ALLAH DA MAZON SA KADA KI FITAR MIN DA NOVEL DINA YAR UWA.

Fuska biyu ga mulsumi abune mai muni ga alumma a hada dashi da Allah bai san darajan shi don zuciyar ta tayi tsauri shedan ya rinjaye shi amma kuma yana musulmi babu Allah a zuciyar shi.
Kafiri ma yana tsoron Allah balle ke mai sallah biyar a rana ina zaki da hakkin wani a kan ki naki ma ya ishe ki kaya gobe kiyama.
Bai damuwa don nasan da kayana zaki dauka ranan dauka akai babu mai taya ka sai halin ka muje zuwa yar makawa yanzu ta fara novel yar matashiya ce a cikin ku.
Ana cewa novel ba dadi ba ma ana kuma gashi ya zama kamar dole a karanta harda sato maku akeyi don kawai son duniya.
A hankali ya sa hannuwanshi ya juyo ni ta yadda zamu iua fuskantan juna dashi irin tsabar soyayyan da nagani a cikin kwayan idon sulaiman din ban taba ganin shi a cikin kwayan idon wani na miji ba.
Haka yasa ni sunkuyar da kaina kasa da sauri gabana ya na bugawa uku uku don firgice sai ji nayi idanuwa sun ciko min da hawaye ban san sun zobo ba.
Sai gani nayi yasa hannun shi yana sharewa a hankali jikin shi babu idan inda bai rawa a lokacin don wani irin sha,awa dake fisgan shi a lokacin.
Sannu a hankali yake goge min hawayen sai naji sun zubu gaba daya kuka ne yaci karfe na ji nayi ya rugumoni zuwa jikin shi.
Cikin sautin kuka nayi karfin halin bude baki na ina cewa dashi Uncle, , , Uncle sulaiman don Allah , , , don Allah ka rike ni amana karka ci amanata don Allah ka soni tsakani da Allah ka so ni saboda Allah badon wani abu ba.
Sassauta rikon dayai min yayi don yaji maganan ya doki kwakwalwan shi a lokaci guda.
Sai kuma naji ya riko ni fiye da na farko kamar zai hadiye ni, shima magana ya soma cikin sanyin murya kamar haka.
Safiya ki kwantar da hankalin ki mu fahinci juna mu zauna lafiya wallahi Safiya bazan taba hada son ki da wani ko wata ba.
Ina son kine tsakani da Allah, ina son ki sani ni ban soki dan wani abu ba ko wata manufa nawa, ina mai tabbatar maki ba zan ci amanar ki ba a rayuwana don banga ribar da zan samu ba ga yin haka.
So dan Allah ki saki jikin ki dani mu zauna lafiya cikin amincin Allah, ina tare da ke komai wuya komai dadi.
Don ba zan taba hada darajan girman ki ba da wata mace a fadin duniysn nan mahaifiya ta ce kadai zan iya hada son ta da naki don ita kadai ne mafi daraja a gare ni a duniyan nan yanzu bayan ke.
Don haka ku biyu ne kada yanzu zaku iya juya ni yadda kuke so a rayuwan ku.
Ni nace ina son ki duk yadda kike ba zan taba kowa dake ba mudin na samay ki yadda nake so muyi zaman mu lafiya mu karasa rayuwan mu a tare cikin salama.
Ya kare da fadin okey ?
Ajiyan zuciya na sauke amma ban iya dago kai in kalle shi ba har wanan lokacin sai kawai naji yayi amfani da hannun shi na dama ya dago min habana.
Kafin ince zan mayar naji ya hada fuskan shi da nawa yana kokarin neman baki na da na sa idanuwan shi a lumshe suke lokacin.
A tsorace nake an ma na kasa hanashi abin da yake min din sai ji nake yi tsikar jikina yana tashi sai kuma naji hannun shi na hagu na kaiwa da komawa a godan baya na.
Tankar yana lalashi na harshe shi naji ya zura a tsakiyar bakina tare da maida hankalin shi wurin shafar wasu sassan jikina musanman godon baya na zuwa mazauna na.
A lokaci guda kuma naji yana yana sumbatar tsakankanin wuyana da kaina haka yasani dole na shiga magana cikin inda inda ina fadin.
Uncle, , , , , uncle yi hakkuri don Allah shiko wani irin zaki yaji muryan nawa yai masa kawai sai naji ya sunkuceni har wanan lokacin bai zare bakin shi a nawa ba bai sauke ni ba sai a tsakiyar makeken gado dake dakin.
Ya kwantar dani haka ya bani daman tokara hannuna saman kirjin shi da hanayena guda biyu don gudun kar jikin mu ya hade wuri guda.
Amma sai ji nayi ya kama hannuwa nawa ya ware su sosai sai ya dafe su da nasa saman godon dole jikin mu ya hade sosai son ran shi.
Kirjin sa na saman nawa ya shiga lasar kunne na yana rada min wasu kalma na soyayya masu dauke da sunayen mu.
Rintse idanuwa nayi suratan da yake yi na sunayen mu wanda suke daidai da sambatu sam ba zan iya amsa ko daya ba.
Hakan kuma na kasa aiwatar da komai a bangare ns duk yadda yaso haka yake yi dani don tuni ya gama tafiya da hankalina da irin siddabarun sa wanda ya gama sanin sirin mallakar mace dashi don ya lura idan ba hakan yabi dani ba, ba zai sameni cikin sauki ba.
Sai da ya gaji don kan sa ya sarara min tare da sauke ajiyan zuciya tare da mirginawa gefe daya yana sauke numfashi a hankali.
Da sauri na jawo zanin dake gefena na saya jikina dashi ji nayi yayi murmushi kawai ya juya min baya.
Da haka muka kwanta sai can naji ya mike ya shiga ban daki da alamar wanka yake yi don dadewan da yayi a ciki.
Haka ya bani daman mikewa da sauri na gyara kaina kafin ya fito naji ya turo kofan ya fito da sauri nima na mike na fada ban dakin don tsarkake jikina.
Ko da nafito baya dakin zama nayi a bakin gadona ina sauke murmushin da ban san na maye ba wata kila na yau muradina ya cika ne ko kuma na na samu mai sona tsakani da Allah ne.
Haka na kwanta ban sake bi takan shi ba sai can cikin dare sosai na jishi a baya bai hanani barci na ba amma dai nauyin shi a kusa dani shiya hanani sakat.
Washe gari ya rigani tashi bai dakin sai dana gama komai na fito don in gaida su mummy sai na samu dakin nasu ba kowa har kayan su.
Na juya zan koma sai gashi ya fito daga dakin da nake tunanen nasa ne ban yarda mun hada ido dashi ba na dan sunkuya ina mashi ina kwana.
Murmushi naji yayi yace an tashi lafiya yaya bakunta nima murmushin na dan kakaro a fuska na kadan.
Au su gwago kike nema naji yace abinda yasa na dago kai na kalle shi kenan da sauri alaman eh yace sun kama kan su ai tun jiya da yamma don sun ga mai masukin nasu bata su take yi ba.
Suna part din hajiya acan suka kwana don haka muje mu karya sai muje gaishesu daga nan sai ki masu bayanin abinda yasa kika watsar dasu a garin mutane bayan ke kika kawo su garin.
Nace kai uncle na watsar dasu kuma fa kace ya fara tafiya yana cewa kin kula da kina da baki ne a gidan tunda kika dafe kan angon ki.
Binshi nayi a baya zuwa dinning inda naga ya nufa tare da zama yana kokarin jawo plate a gaban shi.
Da sauri na karasa wurin ina karban plate din tare da jawo wormer din abincin ina budewa nace amma dai a bari in fara aiki na kar kuma ace min na shagala dayin haka don naga ango na zaune.
Murmushi shima naji yayi bai hanani zuba abincin da nake zuba mai har na cika plate din da shi na juya na zauna ina jawo plate zan zuba ma kaina naji yace wanan da kika zuba dani da waye ?
Dole na dauki spoon din na saka a plate din da kyat na diba sau daya nakai a bakina don kunya ganiin bazan ci ba yasa shi diba ya miko min yana fadin bude bakin ki dole na bude badon na so ba.
A haka muka koshi muka mike zuwa part din hajiya baaba bayan na kawar da kayan zuwa kitchen muka nufin wurin su baaba din.
Shike gaba ina bayan shi muka shiga da sallaman mu don tun bamu shiga ba muke jin hayaniyar mutane a part din nata.
Sallaman shi yasa duk suka juyo gare mu zama yayi saman daya daga cikin kujerun falon ni kuma sai na zube kasa daidai inda ya aje kafan shi.
Sai naji wata daga cikin wa yanda ke falon tace da alaman amaryan tamu tana da kunya don naga ko ranan da aka kawo ta bata zauna akan kujeran ba.
Murmushi naji yayi tare da fadin kun tashi lafiya sai kuma naga ya dan zamo saman kujerar yana hajiya barka da Safiya yaya gajiyan jama a ?
A lokacin nima na samu daman gaida ita da kwana ta amsa min fuska sake tana cewa yaya bakunta ?
Komawa yayi saman kujerar ya zauna da kyau tare da tambayan ta ina bakin ta suke tace suna ciki sai wacce tai maganan farko taci gaba da magana tana fadin kada kiji kunyan mu munan duk yan gida ne.
Yace Well, Safiya meet my sisters wanan itace Aisha wanan kuma khadija, and that is my cousin sister jamila and nuriya duk anan wurin hajiya mu suka tashi.
Na dago kai ina bin su da kallo araina ina cewa ashe yana da yan uwa mata haka ya lakewa anty kawai kamar wanda baida kowa.
Mikewa yayi yana cewa bari mu gaida bakin mu kafin in fita don ina son zuwa gidan su kawu kafin mu wuce.
Hajiya ne tace dani bishi mana ku shiga suna ciki a dakin muka samay su kwance suna jin sallaman mu suka mike zaune.
Ni na fara shiga shi ya biyo ni a baya sai da na zauna na fara gaida mummy sannan na juya wurin gwago dake gyara daurin dan kwalin ta nace gwago yaya bukun ta.
Tace bari kedai ai har tunanen komawa gida nakeyi wallahi wanan uban nisan da muka kwaso nayi dariya nace gashi kuma gobe zaki kara kwansan nisan .
Tace yar nan kin faye zari da har idon ki ya kyala har wata kasan dauko miji.
Dariya yayi mata yace gwago ai tafiya yanzu kika fara don yanzu aka fara yi wata rana har waje zamu fita dake garin masu jan kune.
Zaro ido tayi waje tana cewa rufa min asiri dan nan nan ma ya isa haka ai an gode ta kalle mu tace to yanzu dai Allah ya hada wanan aure don Allah a yaki zuciya yi nayi bari na bari sai a zauna lafiya Allah ya kawar da idon makiya a tsakanin ku.
Mummy ne ta amsa da karfi da amin ya Allah tana mai daga hannuwa sama alaman addua ya karbu.
Nan dai aka dan taba hira ya mike yana fadin zai fita ya juya gare ni yana fadin zaki iya komawa part din mu yanzu don babu kowa a cikin sa.
Sai mummy tace bari ta taso zata samay ni a can tare muka fito ya tsaya magana da yan uwan shi nikuma na wuce part din mu.
Bayan na dan gyara wuri sai ga mummy ta shigo da gwago nan na dawo falo na zauna wurin su tare da kuna tv dake falon.
Kwantawa nayi saman doguwar kujeran dake falon tare da lumshe idanuwa na a han kali ina mai ci gaba da tunanen makomar rayuwa na.
Ban san lokacin da barci ya dauke ni ba sune zaune suna hiran su jefi jefi wanda hiran akan inna ne da halinta.
Shigowan sisters din shi ne yasa na farka naji suna cewa ayya barci takeyi ne sai na bude idona tare da tashi zaune ina masu sannu da zuwa.
Wuri suka samu suka zauna suna fadin mun zo muyi maki sallama ne don yau zamu koma gidajen mu sai dai Aisha ce don ita a abuja suke zama da mijin ta.
Murmushi nayi ina mikewa nace har zaku koma ke nan suka may kuma zamu yi nace ai kunyi kokari an gode nace ina zuwa daki na shiga na bude akwati na hado masu kayan shafa da kayan buki na fito masu da leda hudu a hannu na.
Mika masu nayi mamaki sukayi suka kayan naki kika kwaso muna kuma nace ai don amfani aka sayo su godiya suka yi man, nayi tare da sallama na raka su har kofa.
Bayan tafiyan su na dawo na zauna inda su gwago suke muna hira jefi jefi dasu Uncle ya dawo gidan da sallaman shi ya shigo falon.
Su gwago suna mai sannu da zuwa suna kokarin mikewa su bar falon yake ce dasu don Allah ku zauna abinku yaya kuma zaku tashi amma sai basu tsaya ba sukace dama mun shigo ne don tana ita kadai zamu wurin hajiya mu taya ta hira.
Suka fice ni kuma da nake zaune ina kallon draman su sai lokacin nayi mai sannu da dawowa.
Zama yayi kusa dani batare da ya amsa ba sai dai ni kuma ban yarda mun hada ido dashi ba ji nayi ya kamo yan yatsun hannu dake saman jikina ya rike.
Ya dago hannun nawa yakai masu sumbata tare da kura min idanuwan shi a kaina, ji nayi kamar in nutse a lokacin don kunyan shi da nake ji.
Jawo ni naji yayi zuwa jikin shi yana kokarin runguma a jikin shi nayi karfin halin ce mashi uncle baka gudun wani yashigo ya samay mu a haka ?
Cikin karfin hali ya iya fadin wazai shigo nan ko mm a sun shigo ba matana suka sama ina runguma ba da banda aure sun ga na rungumi watane.
Nace amma, , , katse ni yayi da fadin amma may ke kuwa zamu shirya dake don naga kina neman hanani abinda Allah ya halasta min.
Murmushi nayi nace ban dai son wani ya samay mune a hakan yace and so what inda an samay mu su gwago da suka san kan su baki ga sun fita ba.
Dole haka na kyaleshi yaci gaba da murzana yadda yake so ina runtse idanuwa na don kanshi ya kyale dama jan magana yakeso.
ya sumbaci kuncina tare dan dagowa daidai kunena yana magana kamar maiyin rada kina kunyan azo a same mu ne ina taba mata na.
Nace kai da baka jin kuyan ai sai kayi tayi amma ni ina gaban sarakuwa ina zan biye maka ace min jarababban amarya.
Ya fidda karamar dariya yana matsa min hannaye na yace af nine banda kunya barin nuna maki banda kuyan yanzu.
Na dan shagwabe mashi murya ina cewa Uncle kabari Allah kuwa zamuyi rigima dakai yanzu.
Dariya na kara bashi ya sake jawo ni jikin shi gaba daya yana fadin bari mu fara rigimar tun yanzu.
Zillewa nayi ya sake ni yana dariya dakin shi ya shiga ban ji fitowan shi ba har na mike nima zan shiga daki sai gashi ya fito.
Yana fadin ki fa shirya jirgin bakwai zamu bi zuwa Abuja gobe don haka ki fada ma su gwago su zauna da shiri don kar a girshesu.
Ina mamakin shi gashi dai yana son yan uwa don shi da kanshi ya kawo shawaran abar mutum biyu da zasu rakani Abuja yace kuma da gwago cikin wanda za a bari da da mama zasu tsaya sai kuma aka tsaida shawaran mummy ta tsaya su yaya Saadu zasu biyo tanan sai su dauke ta.
Amma kuma na fahinci yan uwanshi kamar basu jin dadin shi kamar yadda Faiza ta taba gaya min amma dai koma may ne yanzu tun da Allah ya jefani cikin su da sannu zan fahinci komai.
Washe gari dukan mu muna zaune gaban hajiya baaba tana muna nasiha sai lokacin take ce ga yar kanin ta nan zahar ta karbo muna zamu zauna da ita .
Koshi ashe baisan da maganan ba sai naga yayi saurin dagowa yana duban mahaifiyar tashi don kawar da komai da sauri nace mun gode baaba Allah ya taya mu riko.
Tace keda kika fishi hankali baki ki alherin da nai maku ba amma shi har yanzu ban san abinda yasa baka mantuwa ba a ranka ana son musulmi da yawan yafiya ko yaushe.
Murmushi yayi yana mike wa tare da sosa kan shi yace hajiya mu zamu tafi ai muna fatan alheri.
Addua ta shiga kwararowa tana bin mu da fatan alheri har muka fice part din su gwago kan har an shiga motar da zata kaimu airport.
Sai da muka sauka ne naga ashe da Aishan shi zamu tafi zata koma itama gidan mijin ta tare muka shiga jirge gwago kan sai kama mummy take yi.
Mun bar yarinyar zata biyo driver da zai zo da motar da sauran kayan mu don suma sammako zasu yi don su isa da wuri.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button