BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , ,

????????2️⃣0️⃣????????

YAR UWAN NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , , ,

Abin yai min yawa a tare da ni ga yunwa ga ciwo ga ciki sai yar dadiron gida da tazo ta kakace gidan da zama .
Ga miji dani da babu duk daya a gare shi bai san cina ba bai san sha na ba ko ciwo gashi har wanan lokacin maman biyu bata zo gidan mu ni kuma ban fita ba.
Don da zaran nafita da ya dawo fada mai take yi ya samay ni yaita jibgana sai ya ga dama ya yabar ni.
Suna zaune falo sun sayo kaji gassasu suna ci ga kayan shaye shaye nan mai sanyi agaban su wasu ansha wasu ba a taba ba.
Kayan abincin da maman biyu ta bani duk sun kare banda komai da zanyi dabara dan kitson da nakeyi ya hanani wai ana cika masa gida.
Jin motsin su a falo da dariye dariyen su yasa ni fitowa na samay shi, da farko da nai magana tankar bai jini ba.
Sai da na kara cewa yaya wurin ka fa nazo tun jiya ban ci komai ba a gidan nan sai ya dago ya dubeni wani irin yai karfin halin daga Lilliya daga jikin shi.
Ido ya zubamin na sake cewa tun jiya da safe banci komai ba a gidan nan, Lilliya ce ta sake kwanta mai a jiki tana wani iri da idanuwanta.
Yai karfin halin sake daga ta daga jikin nashi again yace baki ci abinci ba mai kike jira da baki dafa ba.
Nace wanda ka saya min ya kare sai ya juya ida take zaune yana kallonta ya zuba mata ido yana kallon ta.
Yace baby kin san ba a horo da yunwa a bari ta dinga dafa abinci tunda akwai shi kuma ke ba damuwa da dafawa kikayi ba.
Ta wani ya mutsa fuska tace abata badon halin ta ba don albarkacin wanan baby dake jikin ta.
Tsayawa nayi ina masu kallon mamaki abincin ma da zanci wai sai ya nemi yardan karuwasa idan ta yarda a bani indafa.
Ganin ban wuce ba yasa yace bakiji ba abinda tace kinci albarkacin cikin jikin ki tace eh don kuwa babyn dear na ne kinga kuwa bazamu barshi da yunwa ba.
Kije mana ya daka min tsawa yana harara na wai na wuce mana tunda an bani na kalle shi nace haba yaya kaji tsaro Allah.
Yanzu cikin daren nan karfe goma ya wuce wani abinci kake son na dafa inci a wannan lokacin.
Ya zuba min ido yana kallona da idanuwan shi da sukai ja amma ya kasa fadin koma sai bina da kallo da yake yi.
Sai a lokacin Lilliya da ke jin mu ta dago jajayen idanuwanta da suka rine tace wannan abinda muke ci kike so komay
Kasan mai ciki da gwada zai yiyu kamshin shi taji tafito daga dakin ta, idan har shi ko kika biyu wallahi kwalelen ki idai wannan ne.
Kofan da aka turo ne yasani juyawa bani ba harsu din suna diban kofan don suga mai shigowa lokacin.
Bakowa bane illa yaya saadu ya shigo gidan fuskan shi a daure da alaman har yanzu yana cikin zafi da maigidan.
Tunda yai sallama ya shigo gidan jikin shi ya bashi cewa akwai wani tsiyan da aka shukawa a gidan.
A hankali murya a sanyaye na gaida shi da zuwa sabanin yadda na saba gaida shi abaya idan ya zo.
Tambaya na yake a gagauce yana yi yana kallon inda suke zaune a ciken hasala maynene matsalan safiya may sukai maki nace , ?
Ganin shi yasa kuka da banyi niyar yiba yazo min a lokaci guda .
Durkusawa nayi a gaban su ina tsananin kuka kamar na fita yacina Yaya Ahmed ya daga zaune ya zuba min idonsa da suke jawur , ya kasa fadin komai, .
Kumshin naman kazan daya rage guda daya basu taba ledan shi ba shi ya dauka ya miko min yana fadin.
Indai wanan ne kikewa kuka don ba a baki ba gashin nan kije kicke baby bari zan saya maki wani kafin mu kwanta.
Ban karba ba kuka kawai nake yi ya sake cewa karbi mana kibani wuri da kukan nan naki hakanan.
Yaya Saadune yace safiya in nama kikewa ki karba gashinan ya baki sai na dan tsagaita kukan da nake yi nace yaya tun jiya ban ci komai ba a gidan nan .
Na fada mashi yace wai wanan ta bani indafa yanzu yaya yaushe zan dafa har inci da daren nan .
Na juya ina fuskatan shi nace yaya ina cikin wani babban matsala da tashin hankali da ban taba tunane ko tsanmanin zan shige shi ba.
Yaya Saadu ka mai dani gida inyakani baba zai yi kan naki zama gidan dan yar uwanshi sai dai ya yankani a kan hakan ko dabba aka daure a gida ana bata abinci taci balle mutum.
Yaya saadu kai kadai nake jin saukim rayuwa a wurin ka sai kuma maman biyu da tai min tsaye, .
Ita ma bakin ciki da takaici ya sa ta dauke kafanta da zuwa dubana bani da kowa dake zuwa dibani sai kai da kazo yau din nan.
Ya tausaya min sosai yace kinyi hakkuri safiya tun jiya na dawo motana ne keda matsala sai na tsaya gyara da na dowa nike tambayan mummy ke sai take fada min wai kina nan da ciki kuma kuna samun matsala.
Ya juya wurin dan uwanshi yana cewa yanzu kai rayuwar daka zabawa kanka ke ga ka dauko karuwa har cikin gidan kana sunna kana fifita ta sama ga matar ka.
Yaushe zaka girma kasan ana mutuwa ayi hissabi wai har ace kace matar ka ta zubar da cikin da kuka samu wai har ka tsaya kana mata wullakanci akan hakan.
Wanan matar banzan daka dauko ka kawo mata gida fa a matsayin may take ita in ma har zakuyi abin ku , ku tsaya can kuyi inda bata ji balle ta gani.
Yanzu bakajin nauyi da kunya kana ciyar da matar banza abinda kake so ka kasa ciyar da matarka ta sunna ga ciki ga bakin cikin ka da yunwa yaya kake son tayi.
Tsawa ya daka mai yace ya isheka Saadu ya isa haka gidan ka ko gidana ka sani matar da kake kira da matar banza matatace.
Mata mata fakace yai masu wani kallo yana tafa hannun shi yace dakyau wanan ce matar kake nufi ko may .
Tun wuri idon ka ya bude akan wanan ya nuna Lilliya yace wan yan kaddangarun bariki masu ma mutum shigo shigo ba zurfi.
Yanzu ka dubi wanan yarinya wata take dashi garin nan bayan mu bata da kowa Allah ne gatan ta kaine gatan ta amma ga ciki jikin ta kuma ga horo da yunwa.
Nice na katse su nace yaya bansan yaya zanyi da matsala ta ba ya zama wajibi na zubar da cikin nan dake jiki na.
Gaba daya suka dubo ni nace shine kwanciyan hakalina a yanzu ina ni kadai ban san yaya zanyi da kaina ba ina ga mun zama mu biyu nan gaba.
Na san idan na zubar ina da daman yin wasu abubuwa , ban kai ga fadin abinda zan fada ma sai naji yaya Ahmed yace duk kika taba cikin nan a yanzu bakin auren ki.
Nai mai wani irin kallo na juya ina fuskantar shi nace tsaron mutuwar aure na shine zai hana ni fitarwa ba, indai zubarwa zai kawo min kwaciyan hankali..
Matsala ta guda shine baba don nasan bazai barni in zauna mai gida ba don ya rantse kan haka.
Tausayina ya kama shi baisan lokacin da idanuwan shi suka kawo hawaye ba ya kalli wan nashi da yake hassale shima yana sauraren mu .
Wani kallon yake min ga alaman yunwa a tare dani da rashin kwaciyan hankali, kai bashi ba ma duk wanda ya ganni sai ya tausaya min saboda nayi kankanta da shiga irin rayuwan nan.
Shi kanshi lokaci na farko da yadan tausaya min kenan a gidan don wanan shine lokaci na farko a rayuwan shi da yaji ya tausaya min ya sake kallona ina cikin kun ci da tashin hankali.
Shiko yaya Saadu wani irin radadi da bacin rai ya dinga ji a zuciyar ji yake kamar ya samay su yai ta dukan su a lokacin.
Do yana tausaya min ya son abani kulawa yadda ya dace amma wan nashi yaki ya saurare shi.
Ganina da tayi cikin wanan halin kuncin fa ciwo ga yunwa da bakin ciki ya fi komai bata mashi rai.
Ya kasa jure gani na cikin wanan halin ya fita waje ya barmu a yadda ya samay mu shiko gogan harara ya watsa min yace.
Ban san abinda yasa kike son hadani da dan uwa na ba a dalilin ki bamu shiri yanzu da shi.
Sai liliya tace munafunci mana munafuka wai harda cewa zata zubar da cikin jikin ta da da akace ki zubar uban wa ya hanaki zubarwa.
Ke kilaki rufe ma mutane baki don ba a kasa dake ba a zancen nan kibar masu magana suyi.
Nan cacan baki ya kaure tsakanin mu don bazan in mata bane ko banza tafini karfi ga tsayi ga komai turwa kawai nakeyi ina maida mata martani ganin shi zaune.
Shiko gogan taba ya jawo ya dinga kunnawa yana zukewa yana fesar da hayaki sama kwakwalwan shi ta dinga caji yana neman mafita.
Yaya Saadune ya dawo ya samay mu a haka da kayan abinci niki niki ya jani zuwa dakina ya bani magana da kalamai masu kwatar da hankali.
Yace safiya na fahinci matsalar ku muddin bai daina hurda da matan bariki ba zaku samu zaman lafiya ba.
Nai maki alkawri zan kula dake da abincikin cikin ki har ki haihu bazan taba batin ki kwana da yunwa ko kishin ruwa ba.
Safiya ban san abin ya kai maku haka dashi ba har yana horon ki da yunwa ga kuma karuwa ya dauko maki a gida.
Nan dai ya sani gaba har saida yaga na ci abincin da ya sayo min din saidai na kasa cin abin kwarai a lokacin don ciki na ya kulle sosai.
Ya rasa abinda zai yi ya fice ya daho ruwan zafi tea ya hada min mai zafi shina samu na dan sha a lokacin sai kuma na fara shega amai.
Yana ta faman yi min sannu waya ya dauka ya kira habiba da safiya suzo su kwana dani .
Shedaniyar ko bata san yana kulle da ita ba jira yake yaga hankalina ya kwanta ya koma kansu.
Sai cewa tayi amma wanan abin da kake mata baiyi ba wallahi kune ke kara shagwabata takeyin abinda taga dama.
Sadiya kawai tazo habiba tace wai kanta ke ciwo itama ta tausaya ma halin da nake ciki sosai tace bakida lafiya har haka amma bamu sani ba kuma gashi yaya suna zuwa gidan mu shida lilliya.
Suna nan zaune inda suke yaya saadu ya fito yabar ni da sadiya ta taimaka min ya dawo wurinsu falo.
Lilliya tasa halin shi sosai bai daukan raini tun farko ya tsane ta sosai don baison taraiyan ta da dan uwanshi .
Ahmed har yaushe zaka zauna macen banza tana dinga juya ka a gidan ka tana yiwa mutane iko haka, na tausaya wa rayuwanka da ka kare a gidin wanan matar da duniya ta gama yayinta.
Tasan halin sa sarai tana son magana tana gudun jibga yace idan matar nan bata bar gidan nan ba sai na sa andaure min ita a garin nan.
Fada yake yana zare idanu halinshi ba dama dai tai magana tasha na jiki a gurin shi da daren nan mikewa tayi ta shige daki.
Nan ya zauna yana suna magana nasiha nasiha fada fada dashi karshe dai yace wai yayi kuskure zai gyara .
Amma zancen Lilliya tabar gida bai taso ba shi kanshi ba fa dadin ta yake ji ba don ta gama isarsa dan kwanakin da sukayi tare amma kamar jaraba bai iya rabuwa da ita.
Shi kuma yaua ya kafe akan lalai sai tabar gidan tunda ba auren kwarai sukayi da ita ba.
Lalai kuwa Safiya ba zata zauna da wanan yar duniya a gidan nan ba kaji na fada maka tun wuri kasan abinyi.
Yasan yaya saadu ya fishi zama dan duniya sai ya dafe kai ya rasa abinyi do maganan shi ta girgiza shi ainun .
Muna daki muna jin badakalar da suke kwasa tsakanin su jikina yai sanyi don kirikiri ya fifita da ni yadda yake maganan aibanci gamay dani.
Jiki na yai sanyi sosai tsananin tausayin kaina ya kama ni na tuna yadda nake cikin yan uwana yau gashi an kawo ni dani da tutu duk daya.
Hawaye ne ya wanke min fuska itama sadiya dake jin fadan da sukeyi kuka takeyi karshe dai shigewa yayi yabar kanin nashi a falon yana fada.
Dakin ya shigo wurin mu ya kalle ni tausayina ya kama shi yasan duk mahaifiyar suce ta jefa ni wanan halin .
Don tasan halin data sarai amma ta nace sai yayi aure a zurian ta wai ko zai daina abinda yake yi wanan yarinyar haka ina zata iya shirya wanda ya haura talantin da wani abu can.
Yace Safiya ni zan tafi dare yayi nai maki alkawrin da sannu zan dinga warware ko wace irin matsala a rayuwan ku muddin ina raye.
Ko ina gari ko bana nan tankar kauna na da muka fito ciki guda nake jin ki mijin ki yayi nisa sosai da bariki sai addua lamarin sa.
Yai muna sai da safe yana ma sadiya tuni da ta tabbatar da naci abinci da safe na sha magani na.
Bayan tafiyan shi munajin suna hayaniya a dakin su nan sadiya ke kara fada min ko wacece lilliya da halayen yayan nasu da abin da yasa uwarsu ta auro mashi ni din.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button