BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGO, , , , , ,

????????4️⃣4️⃣????????

DA FATAN ANYI SALLAH LAFIYA ALLAH YA MAIMAITA MUNA NA BADIN BADADADA YA BAMU CIKAWA DA IMANI A ZUCIYAR MU, , , ,

Sai bayan kwana takwas ya samu zama da yaya sani din bayan sun gaisa dashi ne yake cewa yaya sani dama maganan da zamuyi akan yadda za a gyara gidan nan naku ne kafin daurin auren mu.
Yaya Sani ya dago ya kalleshi da sauri yace kana nufin gidan baban mu ko ina yace cikin gyada kai eh nan nake nufi a gyara .
Ya ce dashi dakuna nawa ne a gidan ya fada mashi yadda tsarin ginan gidan mu yake sai yace ba a samun fili daga waje sai a kara yawan fadin filin gidan.
Yaya Sani yace daga gaban mu har bayan mu filin babane wanda yake shuka masara da damana a cikin su don haka akwai fili sosai daga bayan.
Yace abu yazo ka da sauki nan ya fitar da plan din yadda yake so a yi ginan gidan namu nan yace gobe in Allah ya kaimu nake son ka tafi amma kuma idan akwai fili a kusa daku kadan ina so don akwai abinda zanyi dashi.
Yaya sani ya rasa abinda zai ce mai sai ya kama kuka kawai don bama zai iya bude baki shi ya yi mashi godiya ba.
Ranan haka ya wuni suku suku yana tunanen wai gidan su ne za a mayar kamar na yan birni a garin mu gidan bulo da bulo wanda sai wani da wani suke ginan bulo da bulo zalla.
Gaskiya Safiya ta kasance alheri a cikin mu dan ta zama muna hasken rayuwa shi ko ma a haka aka tsaya ai ta wadatar dashi don ya samu karuwa.
Washe gari tunda safe ya gama shirya mai komai na tafiya yaya sani ya fara hanya shi wanda zai mayar dashi gida.
Sai yamma suka isa don sun tsaya hanya sun sai doya da su majan da sauran tsaraban Abuja suka kama hanya.
Mutane na zaune sunyi daba kamar yadda yanzu maza suka koyi yi a ko wani gari gungu gungu ya shigo garin sai budawa yake yi shi a dole ga dan birni ya dawo.
An bi motar da kallo har ya tsaya a kofan gidan mu abokan shi na ganin ya fito suka dauki ihu shiko sai faman washe baki yana mika masu hannu .
Da kyat ya samu ya shiga gida bayan an gama kwashe mashi kaya daga cikin mota zuwa cikin gida.
Yara na shiga gidan da kayan sai suka nufi kofan ummina da shi kamar yadda ya fada masu sai inna tace maza su kawo kayan a kofan dakin ta.
Yana shigowa ana mashi sannu da zuwa bai ko amsa ba ya hango an tara tulin doya kofan inna yace kai amma yaran jan nan suka zube kayan nan kuma bayan na fada masu inna zasu kaiwa.
Inna tafito da sauri daga dakin ta tace kamar yaya akai kofan Rabi kuma ba kai kazo da kayan ba ?
Yace kayan ummi ne don ita surikin ta yace a kawo wa don haka ku kwasa ku mayar don Allah yace ma yaran dake shirin fita daga gidan.
Bayan an gama kawarwa sai da ya tabbatar sun kwashe komai ya kara yana cewa mama, mama ga mutan Abuja sun dawo fa.
Mama tace ai naga kashigo kana ta sababi da yaran ta fada a fakaice yace wallahi fa ga inda akace sukai abu sun kwasa sun kai wurin da bashi ba.
Inna tace muma Allah ya bamu ba sai anbamu ba ta diya har ana daga muna kai a cikin gida yaya sani ya kada kai yace inna ke nan.
Kin ko san gidan da Allah yakai Safiya kuwa inna da kike fadin wanan magana haka gida ne fa gidan bene sai inna din ta katse shi tace rufa mana baki sakarai kadawo kenan da katobaran ka kamar , , ,
Tau tau baba ya fada may akai wa cirko cirko haka kuma ya fada daidai yana shigowa gidan da leda baka a hannun shi.
Mama tace umm umm mutan Abuja ne suka iso muke shan labari yace to kai haka akeyi kazo da mutum sai ka barshi a waje kuma ?
Sai lokacin ya tuna da yabar driver a waje baiko kai mashi ruwan sha ba sai inna tace ya kai kai ruwa yaya nan yana fadi ba a tambayeka ba.
Mama tace ai abinda ya gani yake fadi magana ne yakawo magana har yake fada muna yaya Sani ya fita daga gidan yana aiken yaro ya sawo mai ruwan pure water.
Bai shigo ba yana can yana nema wa bakon shi wurin kwana don haka bai samu zama su gaisa da mutanen gida ba ranan.
Sai washe gari tun da safe inna ta samu baba a dakin shi wai yaya sani yazo da tsaraba inna takama tasa shiyan ta.
Bata raba ba yace anya Rabi zatai haka kuwa a gidan nan amma barin kira ta inji dalilin ta nayin haka din ?
Da bi ar bane in magana ya kama ya kirasu dukan su don haka har da mama aka kira suka zo bayan sun zauna yace da ummi na.
Rabi yaya akayi kuma sani ya dawo da tsaraba kin kwashe kin tura dakin ki ko dan tsaraban ya fito daga gefen diyar ki ne kikai haka don yanzu Rakiya ta samay ni da maganan .
Salati ummina ta saka tace ni malam da dare fa Sani yazo da kayan kuma tun fitan shi bai dawo gidan ga ba balle inji yaya kayan suke ya dai ce ma yaya akai kayan kofana .
Sai mama ta tara tace kai ba haka zancen yake ba da yara suka shigo da kayan ita Rakiya tace su kawo kofan ta.
Sani na shigowa yace su kwashe sukai kofan Rabi surukinta ne yace a kawo shine ma ka shigo ka samay mu muna maganan dashi jiya.
Ko da dare Rabin ta samay ni da zancen kayan nace tabari har Sanin ya shigo muji yaya kayan suke sai kuma nace ta kwashe tasa daga cikin dakin ta don sata kuma da dabbobi.
Ya juya ga inna yana ce mata kinji dama na fada maki tun farko Rabi bata yin haka ke gajin hakkuri gareki Rakiya.
Ta mike zabban kuya tana cewa in ba a bayarwa ne a barshi mana doya ne mutum bai taba ci ko manja tana kokarin fita yaya Sani yana shigowa gida neman kulan da zai ba bokon shi abin karyawa a ciki.
Ummi ya nufa yana kiranta yace ummi don Allah bani kula zan sai ma boko na abin karyawa ta mike a kasalance tana cewa dashi ai nasa an mashi abin karyawa ko.
Yace da kyau ummi ashe barince mai abincin ta wuce din har na tsayar da ita baba da yaji muryan shi yace kai sani kai ka dawo baka zauna da mutane ba.
Yace baba ina zuwa akwai labari mai dadi yau a gidan nan barin ba bako abin karyawa jin haka da inna yayi sai ta shiga daki ta aika yaro ya kira yaya sani.
An samay bai ko tsaya sauraren yaron ba ya korashi ran inna yakara baci sosai dashi ta cika fam tana jiran shigowan shi gidan.
Don taso ta jamai kunne akan in alheri ya samo da kada ya fada kowa yaji a gidan subar zancen a yi su dakin su ba sai kowa yaji ba sai ga yaya sani din yaki shigowa.
Sai da ya gama da bakon ya samu shigo dakin baba ya nufa direct nan ya samu baba yana shirin fita kasuwa don yakan dan leka saboda sabo kasuwan.
Yace baba mun samay ku lafiya yaya jikin naka baba ya amsa mai da Alhamdulillahi baba yace yaya kabar su can ya gyara zama yace lafiya .
Ai ita Safiya tun ranan da muka rabu nan ta hau jirgi ta wuce lagos daka can bata kwana abujan ba don ba mace a gidan.
Baba yaji dadi yace dakyau dama tunanen da ya tsaya min acikin raina ke nan yaya yace ai baba sai kaga gidan da aka gina ma Safiya.
Wai ita zata zauna a ciki da mijin ta baba mutumin nan ba karamin mai kudi bane ko a abujan don gidan kawai zai nuna wa mutum haka a zahiri.
Baba albishirin ka yace goro sani don naga a rude kake yace ai dole ne baba kaga zuwan nan da nayi baba ya amsa mai da eh sani.
Yace baba nazo ne da shirin rushe gidan nan gaba daya a gina ma wani.
Baba yace kai sani a cikin hankalin ka kake kuwa koko dai ?
Yace wallahi baba abinda ya kawo ni ke nan yanzu yau din nan zamu je birni muzo da masu aikin da zasuyi ginan don yace bai so ya wuce wata daya ba a gama komai ba.
Ido baba ya zaro yace Allahu Akbar wai sani da gaske kake yi ko kowa wasa yace wallahi baba da gaske nake yi abin da ya kawo ni ke nan yanzu haka.
Su mama ya kwala ma kira yana fadin kuzo kuji ikon Allah da sani yazo muna dashi gidan nan.
Da yara da manya suka nufo dakin baba nan yace yaya sani ya kara maimaita abin da ya fada mashi ya mayar masu.
Gida ya dauki ihu mama tace haihuwa tai ranan ta safiya kin kai diya Rabi kin iya haihuwa tankar da dubu.
Mama na guda ummi ko ko bakin magana bata samu ba inna tace a dai yi sannu kar aje a debo muna wahala muna zaune zaman mu.
Don yan birni babu abinda basu iyawa sai ta tashi ta fita daga dakin tana maganganu tana fadin ba inda zan daga ni.
Tana fita ummi na ta nisa tare da fadin anya malam ba a bin abinga sannu ayi binciken wani irin miji yarinyar ta kwaso muna kada idon mu ya rufe.
Yace nima dai abinda nake tunane kenan yaya Sani yace zaka iya yin bincike mutumin da keda company na tayoyin mota da da gidajen mai zaku tsaya yin wani bincike.
Su wayanda take wuri su amana basu san ya kamata bane da zasu hada ta dashi basu hana ba ya mike yana fadin ni zamu shiga birni yanzu sai na dawo.
Kaunana baba yace ta lalabo ni a waya sai aka samu akasi ba layin neatwork wayan bai shiga ba lokacin.
Zuwa rana su yaya sani suka zo da mutane masu aiki har cikin gida suka shiga aka shiga aune aunen gidan da baysn gida inda filin baba ya tsaya.
Za a fara daga dakunan su inna don haka zasu fake a wani wurin sai ko inna tace bata san da hakan ba sai da baba yayi da gaske yace sai dai tabar mai gidan shi.
Mutane suka shiga tsakanin su duk wanda ya tambaya sai a fada mai mijin Safiya ne da ta samu ya aiko a rushe gidan nasu.
Karamin gari da daukan magana sai magana yabi gari washe gari suka tashi da masu aiki a gidan.
Inda suka koma gida jen yan uwa da zama suda yaran su ummi na kan gidan gwagon ta koma ita da yaranta da kayan su.
Mama ma haka inna kuma gidan yan uwanta ba wanda ya yarda ta koma can dole family house din su baba ta koma.
Ko wani gida yaya sani yakai masu abinci kamar yadda aka umurce shi yayi aiki ake yi ba dare ba rana gari duk an dauki maganan kwaaaa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button