BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/9/20, 9:21 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , ,

????????7️⃣5️⃣????

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU KU

NOVEL DINA NA KUDI NE IDAN KI FITAR MIN HAKKIN AMANA YA BI IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA INA BINKI BASHI HAR BAYAN RANKI, , , ,

Nabiku bashi masu karantawa ta sace har bayan ran ku don online novel ne na kudi kun sani kuke take sani saboda son zuciya idan baki biya ba don girman Allah kada ki karanta min novel don Allah Allah kuma ba wasa bane.
Kamar yadda maryam tace sai ga mai gyaran jiki da yaranta tun da safe a gidan namu suka sallama tare da fadin itace tace suzo suyiwa anty safiya gyaran jiki.
Allah ya taimake ni nagama dan abinda nake yi na koma daki na fada ma uncle Allah ba da saa yace min ya koma ya kwanta.
Da yake su hudu ne nan wasu suka fara sance min kaina dake da kitson da nazo dashi wasu kuma suka kama kafana suka shiga wanke min shi mai min dilka tanayi.
Kafin wani lokaci sai gashi ya fito da shirin shi yace zai shiga wurin baaba acan zai karya haka yake kamar mai gudun baki har nakan yi maki yadda yan uwana ke zuwa ya sake dasu.
Kafin wani lokaci sun gama sance kan ka shaga wake wa ni kaina yau nasan na hadu da gamo na wurin gyaran jiki haki ne turare na duk anbini an shafe jikina da komai nidai iyakata ido suce yi kaza in yi shine nawa.
Kafin wani lokaci munyi nisa ga komai sun gyara ni tas mun kusa gamawa sai ga maryam din ta iso tana min dariya nace ke baki fada min in shirya da wuri tace nasan ba zaki jure wanan abin ba idan na fada maki.
Gaisawa sukayi nan suka juya a kan ta wanda suka gama aikin su suka shiga gyarata ita ma ko ban duba madubi ba yau na san an hadani iya haduwa nan take fada min cewa ai yan sundan ne su aikin su ke nan gyara.
Nace wanan ai in da Abuja suke dana samu wirin gyara matar tace min ai akwai yar uwarta dake yi acan zata ban nombanta idan mun gama.
Kafin wani lokaci sun gama maryam zata sallamay su nace ta bari in sallamay su na shiga na dauko kudi duba ashirin na basu a mu biyu suna ta godiya suka wuce tare da bani wasu turaruka wai idan zanyi wanka in dinga digawa a ruwa.
Maryam ta koma part din hajiyan su ta barni na shiga wanka in gyara jikina washe gari ina cikin wasu material yellow nayi mai dinkin bubu tare da daura dan kwalin shi akaina.
Sai ga diyan baaba sun shigo gidan alokacin ina wurin ta muna hiran masu gyaran jikin da suka zo jiya mun gaisa dasu suke fadin yawwa safiya da anty suwaiba ta iso sai mu tafi tunda kun shirya nace ina da sauri ?
Maryam tace gidan buki mana nace sai kun dawo may kike nufi baki zuwa ko may nan suka hau bakin su sai ga Aisha ta shigo itama ta hau bakin ta tace wallahi ni na dauka shirin ke nan kikayi ai.
Nace ba zan samu zuwa ba kun ga ma ranan da naje sai da Abba yayi zazzabi zasuyi magana hajiya ce ta katse su tace kun fa san halin mijin ta wacan ma zuwan gidan ku da tayi ba karamin tashin hankali sukayi da shi ba.
Sai ga anty suwaiba tashigo ta samu ana maganan tace gaskiya hajiya don ko ni ranan dana biyo daukan ta muje wurin kamu a gaban shi amma wallahi kemay may yaya ya hanata zuwa.
Nace bama zan tafi ba ban iya jidalin shi ke Aisha aikin san halin shi ba sai na fada maki ba don kin san komai na karasa fadi ina kauda kai gefe.
A sanyaye tace nafa sani gaskiya yaya baida dadi halin shi sai ke Safiya hajiya tace bani waya na ku kira min shi ai mantawa nayi har ya fita ban fada mai ba.
Nace hajiya da kin barshi don Allah ni ba zan tafi ba amma bata bi ta kaina ba sai da ta kirashi tace matar ka zasu gidan buki da yan uwan ka nakuma ce ta tafi amma tace bata zuwa don sanin halin ka datayi.
Yace tunda kince ta tafi ta tafi mana tace gata kai mata magana tamiko wayan na karba tare da karawa a kunne na inajin shi yace wai bazaki tafi ba kikace nace eh banjin fitanan ne.
Yace to ki shirya ku tafi yanzu zan turo maki da mota don ina nan gidan gonane zanyi magana yace nace ku tafi ko ?
Ya kashe wayan shi wallahi hajiya dakun barshi Uncle bahagon mutum ne yanzu sai na dawo zai samu wani laifin yace nayi mai ni na gaji da halin shi wallahi.
Nan dai suke ta magana ba yadda na iya dole na mike zuwa part din mu don in shirya tare da maryam muka tafi bayan tafiyana hajiya tace.
Abinda nake fada mai ke nan kada yakai yarinyar nan makura ta daina jin tsoron shi Aisha tace ai in dai yayane yafi danan tana dai iya halin shi ne kawai.
A daki kuma shiri nake yi muna maganan da Aisha take cewa kin gani ba idan mutum bai sani ba sai yace kece ke juyashi ke amma fadi ai don da akaga yana muna abu yanzu cewa ake kece ke sakashi yi.
Wai duk yan uwanki sun mamaye shi sai abinda kikace yake yi Aisha ce ke fada ma hajiya karya ne kema ba dadin sa kike ji ai.
Di dai hajiyan bata da daukan irin maganan ne kin ga shegiyar yarinyar nan da aka tura maku kwanaki yar isakan yarinya ce sosai wallahi duk ita tazo da wanan zancen.
Nace zarah ko tace ita mana nayi bakin cikin da hajiya ta yarda tabi ku a lokacin wai mako tazo gaida ke da kuka zo ?
Nace ban ganta ba wallahi nima na dauka ko bata garin ne ai tace tana nan yar iska in kinji abinda take fada ai abin bakyau wallahi akan ku.
Har na gama shiri muna hira akan zarah da iyayyen ta wasu kaya ta gani ta yaba nace idan kina so ki dauka ban taba saka su ba ma.
Tace cikin murna ashe abinda ake fada kan ki gaskiya ne nan ta barni ina shirya Abba ta fita don khadija sun fita da yan matan gida da wuri yau.
Tsaba na shirya na dauko yaron da jakkana dana abincin shi na rufo kofan part din mu zuwa part din hajiya ko da nazo maryam har ta shirya cikin kayan dana bata ta kwabe wanda tasa.
Ina shiga suka dauki ihu suna fadin dole ma yau mu fasa taro don dole kallo ya dawo wurin mu murmushi nayi ina aje kayan dake hannu na na mika wa hajiya key din idan uncle ya dawo.
Bamu jima ba muka kwasa sai gidan bukin kofan a cike yake da jamma a yan buki har ta cikin haraban gidan inda muke kokarin shiga.
Matane ko ina zazaune saman kujerun roba ana nuna hali tun da muka tun karo wurin kallon su ya dawo kan mu wata tobashiyan su ce ta tare mu tana fadin matar sulaiman di ne nan ?
Gaskiya yake daga hanci ashe yasan zarin da yayi mun gaisa da ita tana mi ba ina dariya dago kan da zanyi in kalli wurin sai a idon anty dake min wani kallo tun daga nisa.
Gabana yaba da wani irin kara a lokaci daya nace innalillahi Aisha ga anty can tace wata anty suna kokarin kallo suga wacece nake magana.
Anty suwaiba tace ko maimuna kike magana wai nace ita jikina sai rawa yakeyi da ganin ta Aisha ne tace kin ga tsaya safiya maimuna may can ai itama yanzu tasan kin fi karfin ta tako ina wallahi ki dake kamar ba abinda yafaru ku gaisa kawai idan ta jaki da mutunci ayi .
In kuma ta nuna maki wani abu akasin haka gamu wurin ai sai na dake sai da muka dan gaisa da mutane muka karasa wurin da suke zaune da wasu mata ashe su anty uwace.
Mun karaso aka fara gaisawa yan biyun ta suna gani na sukayo kaina da murna suka rungumay ni nima na rungumay su muna murnan ganin juna.
Sai can na dan juyo ina fadin anty sannun ku da zuwa tace ai dukan mu ke da sannu da zuwan don duk baki muke anan .
Anty uwa sai kallon na takeyi tana batsarwa kasa da sama tana tabe baki nace da ita anty ina wunin ku tace lafiya kawai ta juya kai ga kallo na.
Sai yanzu na fahinci inda muka zo watau family house din su daddy ne mijin anty gidan su hajiya baaba kenan famnin mahaifan ta gidan kawunan su uncle ke nan.
Mun gaisa dasu muka wuce zuwa cikin gidan don gaisawa da mutanen gida mun bar maryam a wurin tana magana da wata basu ankara ba gulma ya ci su a wurin basu kula da ita ba.
Suna hada baki wurin fadin duniya maimuna yar aikin kine ta koma haka inji anty uwa ke magana sai anty din tace bari ke dai ai ni na suma zaune wallahi .
Uwa din ta sake cewa kin ga kayan jikin ta da sarkan ta kuwa tace ai shi nayi wa mutuwar zaune ana inji anty ta basu amsa .
Anty uwa tace da bamu san asalin ta ba sai mu dauka ai yar wani da wata ce nan ko ba diyar kowa ba wallahi.
Maryam ta kasa hakkuri tace shi fini da uba ai in fiki da miji yanzu haka abin yake ba yar kowa ba gata Allah ya kaita gaba ta basu amsa sai duk suka yake don basu san tana kusa ba.
Suka mayar da abin wasa don dama tobasai suke tace yayan mu ya iya kiwo ke nan ashe ta fadi tana wucewa suka bita da harara.
Nan sukaci gaba da zagina har uncle din sai da yasha zagi ranan wurin su anty dai kasa magana tayi tace ni abin ma mamaki yake bani wallahi.
Mun shiga ciki mu dakin tsohuwar gidan ana gaisawa sai ina akasaka take faman yi damu nan aka kawo muna abinci da sha su yan biyu su manne da mu.
Sai faman daukan Abba suke suna tambaya na wai yana tafiya nace ko zama bai fara ba ai maryam ta shigo nan dai take fada muna abinda suke fadi a gamay dani.
Murmushj nayi kawai nace dama nasan abinda zasu fada ke nan bayan mu bayan mun gama cin abincin ne ni dai ban taba komai ba a wurin muka fito waje don mu sha iska.
Kujeru aka kawo muna muka zauna dukkan mu ahankali nake fahintar komai a wurin ina kallon su yan biyu suka kai mata abba ta dauke shi tana mai wasa.
Kamar babu wani abu a tsakanin mu take nunawa a lokacin sai wani washe baki suke yi karshe dai muka hade wuri daya dasu don rana da yacin ma inda suke zaune.
Nan suka kare min kallo tsab ba yawan magana nake dashi ba ko banza balle yanzu da nake jina kamar a bakin kura na zauna.
Naga Faiza nake tambayan ta fati tace tanan garin amma bata shigo wurin bukin ba sai da anty uwa ta tashi don an kirata na samu tayi min kallon mutunci.
Kamar mai jin tsoron ta dai nan muka zauna muna hira kamar ba abinda ya faru a tsakanin mun dan taba hira har zuwa karfe uku da wani abu nace zan tafi gida tace ba zaki zauna har a wanke amare ba.
Nace zan kai Abba ya huta ne gida anty don bai da jimirin dauka da yawa murmshi tayi kawai nace yaushe zaku koma anty tace daddy bai yi magana ba amma tana ganin basu kai ranan tuesday.
Nace zan shigo in gaida ke su yan biyu suka lake min wai sai sun bimu zata hana wata yar uwar daddy tace ta barsu mana su bine ai za a dawo dasu.
Ko da nace zan wuce su Aisha basu hana ba don duk sun san kwanan wasan tare da maryam da Aisha muka dawo gida muka bar sauran a can.
Tunda muka shigo yaran suka ga uncle suka koma wurin shi mu kuma aka zube falon baaba sai hiran abinda ya faru ake yi a wurin.
Baaba sai murmushin manya take yi kawai tana sauraren mu sai can tace kuma maganan kuke so ai kusan dole tayi bakin ciki tunda ba haka taso ba .
Har ga Allah banjin dadin aibanta anty da suke tayi don dai ni kan batayi min komai ba sai alheri a tsakanin mu.
Duk abinda tayi min ban dauke shi komai ba a raina uncle dai ne da yayi min iyaka a tsakanin mu nan dai na mike zuwa part din mu don in sauya kayan jikina.
Sai da dare ya mayar da su yan biyu gida wurin mahaifan su, su sundage wai anan zasu kwana wuri nace suje gobe zan zo in dauke su.
Sai da ya dawo ne muna shirin kwanciya yace danu ashe yau kin hadu da anty ki nace wallahi uncle baka fada min sun zo ba ai.
Na manta ne ya bani amsa a takaice sai na kyale shi don nasan baison maganan ne yasa nayi shiru sai can naji yace yaya akayi ta bari twins suka biyo ki ?
Nace wata mata tayi mata magana don bata so su biyu ni ba ai yace naga alama ni yanzu sama sama muke da ita.
Mijin ta dai ne bata da yadda zata rabamu dole ta saka ido itama uwar da take mara wa baya naji ance kwanaki sunyi rikici a tsakanin su ai.
Nace tare muka gansu zaune yace zaman dai ne amma sunyi ba dadi har mijin ya tashi sakin ta wai su uwa sun sama mashi wata bazawara a abuja shine taji dama ko akwai kudi ne a tsakanin su ban dai saurari maganan ba sosai.
Nace kuma suna fada haka a tsakanin su ba aminan juna bane na gani yace ke ma ba uwar dakin ki bace kuka samu sabani da ita.
Washe gari da yamma sai ga daddy ya kwaso su sun zo gaida hajiya baaba lokacin duk muna falon ta zaune mun masu taro na arziki sosai daddy ke fadi a a Safiya jiya su yan biyu ke fada min sun ganki har da baby ki wai.
Dariya nayi na durkusa har kasa na gaidashi a lokacin yake min barka ya karbi yaron hannun khadija anty dai sai kamay kamay take yi kawai a wajen.
Tana fadin gashi nan safiya ya biyu sak sai daddy da hajiya ke fadin ai wanan yaron duk gida ya kwaso wallahi ba inda ya raga sulaiman ko kadan.
Yace ni ban ga inda ya biyu safiya ba ai da anganshi anga wanda ya dauko gidan su sak tace don dai kai baka kallon safiya ne killa shi yasa.
Hajiya ta dan yi dariya tace ba abinda ya debo na uwar shi kowa ya gane shi yana fadin gida ya biyo sai dai ke ce ke ganin kamar shi da uwar.
Fita nayi daga falon dasu yan biyu sai zuwa part din mu sai da na fice ne hajiya ta dauko maganan abinda ke faruwa a tsakanin mu din .
Nasiha tayi wa anty din sosai sai da jikin ta yayi sanyi ta kara da fadin ku sasanta dake da yar uwar ki wanan duniya har nawa yake gamay tunane ?
Nan dai anty tace da hajiyan babu komai komai ya wuce ita dama bata dauki abinda zafi ba safiyan dai na ta dauki magana da zafi har waya ta daina bugo min yanzu hajiya bata ji nauyin fada mata cewa uncle ne ya hana in buga mata waya don bai iya jure wulakancin da take min din.
Tayi wani iri tare da dukar dakai tace hajiya wallahi yarinyar nan makira ce ban san may ta fadawa sulaiman ya dauka haka dazafi ba.
Daddy ne ya katse ta da fadin a a maman twins safiya bata tatanci wannan shedan da a gare ki ke dai sai dai in akwai wani abin a lokacin uncle ya shigo falon don daddy ya buga mai waya gasu gidan shi.
Tace kin gan shi nan hajiya yanzun ko wayana ya daina dauka sai ya ga dama safiya ta shiga ysakani na dashi ban san may ta fada mai nayi ba.
Safiya bata shiga tsakanina dake ba don ba ita ta hadani daku ba kawai dai ba zan yarda bane da wulkanta min mata da kike yi koda kuwa ciki daya kuka fito da ita.
A iya sani na har zagina mutane ke yi akan ki yau ko ashe duk abinda na ji na gani ina so ashe in akwai amana takamata kiso abin nan.
So nikuma shiyasa nace duk ranan da na sake ganin ta buga maki waya sai na bata mata rai sosai don ba zan juri gani irin yadda kike mata gaskiya.
Tunda ya fara magana kallon shi suke yi dama daddy ba gwanin surutu bane sosai don haka kai kawai yake kadawa yana saurare.
Sai da uncle ya gama magana yace dashi duk sherin uwace na fada mata tun farko ta fita hanya uwa ba son zaman lafiya suke yi ba su taki yarda yanzun da yafita a tsakanin su ai tayi hankali.
Sun kai wani lokaci a falon hajiya tana sulhunta su sai daga karshe anty ta mike zuwa part din mu inda ta samay mu da su yan biyu muna ta zuba game abin mu hankali kwance.
Mun dan zauna kowa bai sake da dan uwa ba sai da zasu tafine take cewa ashe mijin ki ya hana ki hurda dani ne ban sani ba ?
Nayi dan murmshi nace akan may anty tace nasan abinda kika fada mashi ne tunda ya iya cewa hakan sai dai ina son ki tuna koda shi ko ba dashi ba zan iya rayuwa a duniya.
Nace na sani anty amma kiyi hakkuri tace wa yaran ta su tashi su tafi yaran basu so wucewa ba dole suka mike suka wuce nayi masu rakiya tare da basu tsaraban da na saka masu a leda suka wuce na sallami daddy ya amsa min cikin dadin rai.
Tare da dan yi min nasiha akan duniya bayan wucewan sune khadija tace wai anty may wanan matar ke nufi dake ne haka ?

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button