BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

Yanzu yar uwa kin kwamace in barki da Allah da kike fitar min da novel waje kiba rabawa group group ki tuna duniya ba matabbata bane.
Akwai ranan hisabi tsakanin mu dake ban san kin shigo da fuska biyu bane amma idan baki iya rikon amana ki magana na baki kudin ki don bazan taba yafe kaki ba ko wace ce ke ubangiji yai gagawan isar min a gare ki idan kika kara fitar min da novel ga wanda bai biya ba.
Allah yai min sakayya a gare ki ko wacece ke.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , ,

????????3️⃣1️⃣????????

YAR UWA NOVEL NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA ZAN YAFE MAKI BA IDAN KUMA KIKA FITAR MIN DA NOVEL UBANGIJI YABI MIN HAKKINA A KAN KI, , ,

Washegari misalin karfe goma na safe ina zaune a daki sai ga dayan yan biyu ta ta shigo dakina tace dani mumm is calling you.
Ban bata lokaci ba na mike nabi bayan ta zuwa amsa kiran sama naga ta nufa don haka nabi baya yarinyan nata can .
Wanan ne karo na farko dana taba haurawa wa sama dakunan gidan koda muka hau sai naga saman ashe babba ne da dakunoni kamar kasan.
Ina mamakin girman gidan yarinyar ta tura kofa ta shiga nima na mara mata baya tare da sallama na shiga.
Na samu tana tsaye tana gyara rigar uniform din ta a jikin ta ta dauko abaya ta dagwara a sama fara gaida ita nayi nace anty ina kwana ta juyo tana fuskanta na fuskanta dauke da murmushi tace Safiya an tashi lafiya.
Nace Alhamdullahi ta sake tambayana da kin ko yi break fast don yau banda time din fita ina shirin zuwa office ne.
Nai murmushi nace yanzu zanyi anty tai saaurin ce aa kada kiyi wasa da karyawa keda kike shan magani zaki tsaya biye muna kada ki bari tara yayi baki karya ba a kullum.
Kai na gyada mata kawai alaman to tace dama na ce akira min ke na kara fada maki don fita zanyi don Allah a kada kishiga shirgin su faiza ki zauna da kowa da zuciya daya.
Fati ba kirki ne da ita ba don bata da kunya koma kisan hiran da zaki yi dasu don inda halima ina son ki kama bakin ki akansu maana sirin ki kibar wa cikin ki shiya sama ban hada kowa a daki daya ba nabawa kowa nata dakin daban.
Tace da fatan zaki fahince ni na ce a sanyaye da eh anty nagode ta sake cewa idan kina son wani abu ki tambayi mai aiki ko Faiza su baki nace to ta juya saman gadon ta tace kwashi wayan nan kayan ki fara amfani dasu kafin na dinka maki naki.
Na fara mata godiya sai ta dago min hannu alaman in bari duk da haka sai da na gode mata din.
Daki na koma batare da na hadu da kowa a falon ba har na shige na aje kayan yadda na dauko su da zata fita saida ta leka kowan mu sannan ta fice gidan.
Na gyara dakin sai lokacin na bude kayan don in kaisu a wardrabe din kayana kaya ne masu kyau har kala biyar sai dogon riga daya cikon na shidda kenan.
Na gwargwada sai naga size dina ne ma nasan ta dade dayin su ba yanzu da ta kara jikin girma ba dai.
Nai murna a raina ranan doguwar rigar na sa don yaba kyauta kenan maishi ya ji dadi indan ya ganka da abinda ya baka a jiki.
Shiru yai yawa a daki na fito waje anan na samu yaran zaune suna kallo su kadai suna gani na suka nufoni nan muka zauna ina biye ma shirmay su suna bani labari wai uncle yace zai zo ya kaisu birch zan bisu ko muje tare eh kawai nace dasu.
Ganin kan su ya tsufa da kitson dake kansu yasa nai shawaran sance masu nai masu wani mai kyau na hannu don dai indai kitsone Allah ya hore min iyawa ko wani iri.
Faiza ce ta fito ta samu muna kitson karshe dagani daga barci ta tashi tace wai ashe kuna nan na saba ba in fito ba kowa a falon dole nima na koyi zaman daki ta kai zaune tana yaba kitson da mukeyi tare da cewa ashe kin iya kitso ne haka ?
Na dai yi mata murmushi a raina nace ai kitson ne ya jawo min wanan alherin da nake ciki don lokacin da ta fara kawo su har sau biyu tana zuwa amma bana karban kudin su sai ince su din ai yara nane.
Haka yasa uwar ta daina kawo min kudi a lokacin sai dai wani abin da tafiya yai tafiya kuma ta fahinci halin da nake ciki ta shiga taimaka min.
Jefi jefi muke hira da ita na gama tare da daura masu ribon don shuku biyu nai mako waccen su sai take cewa nima gobe zan sance kaina ki mun ghana wiving don shi nake so nace da ita Allah ya kaimu kawai.
Fati ne ta fito daga dakin ta ko kallo inda muke bamu ishe ta ba zata wuce mu nace mata anty Fati ina kwana cikinciki ta amsa min gaisuwan ita ko Faiza ta ja wani tsaki tare da kawar da kanta.
Dining ta wuce ta bubude kulolin dake wurin ta wani tabe baki tace duk ma an jagule abincin ambar jagwalgwale.
Ba wanda ya kulata sai kuma naga ta zauna tana diba nan ta zauna taci ba tare da kula mu ba sai dai tana yi tana satan kallon mu a fakaice.
Ni dai ina mamakin ta a raina dayar yan biyun ta nufeta take cewa ta dubi kitson da Anty tai masu korar yarinyan tayi daga wurin ta ta wuto tana yi tana waigen ta kamar zatai kuka ganin haka yasa nace zo nan kada ki kuka kyale anty.
Ke naji ta fada kamar wacce ta samu diyarta don haka ban dauka da ni takeyi ba sai da ta sake fadin ke Safiya bakiji bane san nan na dago kai ina kallon ta.
Tace ban faye son ana shiga harkata ba don haka ki kiyayye yar kice ko yar yar uwata koda yake ma kalan dagi ce ke don naji anty na fadin wai kema kauna tace ko a ina ta samay ki oho ?
Ko da yake kila ta wurin mamanta kika fito ban sani ba nan na fahinci ba uwarsu daya ba ashe kila uba suka hada.
Ni dai ban ce da ita komai ba sai Faiza ce tace mata amma dai kin san ba girmuwanta kikayi ba da zaki fada mata haka.
Koda yake baki da laifi don ita ta fara kiran ki wai da anty shiyasa kan ki ya fasu haka kike jin kanki wata babba can.
Ya ishe ki gida dai ne baki iya korana don nima gidan yar uwata ce dariya naji tayi tace yar uwa ko muna yar uwa ai da yar uwan kwarai ce da kin so abinda take so ke yanzu baki ji kuyar korar wanan yarinyar a gurin ki.
Nan dai sukai ta cacan baki wanda nake gani ba yau suka fara irin haka a tsakanin su ba da naji abin yai yawa nace da ita ta kyale ta don Allah maganan ya kare ai mutum guda bai fada.
Sai kuma ta juya kaina tace wai ai dama taga zubina na munafukai ne don haka sai dai hassada ya kashe mu don ita ta wuce ajin muko.
A raina nace wata sabuwa kenan kuma nayi gudun gara na fada ma zago in na gudo gidan mu don inna ga wata kuma na samu a nan yan kuwa zamana nan mai dorewa ne kuwa.
Maigidan bata dawo ba sai hudu na marance daya bayan daya muke shiga muna gaida ita da dawowa koshi ban san ta dawo ba sai da Faiza ta fada min sannan na tafi.
Dama yaran na wuri na sun rigani isa don sai da na tsaya nai sallah na fita zuwa gaida ita din da dawowa.
Zaune take kasa yayin da diyan nata suke saman jikin ta ta mimike kafa suna zuba mata surutu saman jikin ta na gaida ita ta dago har kullun fuskan ta a cikin murmushi tace dani safiya yaya muka wuni nace lafiya kalau anty kin dawo lafiya ta amsa a sake da lafiya.
Sai na juya tace kin ga Safiya debo min abinci na nan don ban iya saukowa kasan nan yanzu na gaji yau da yawa.
Na juya zuwa dauko mata abincin ashe baya wucewa na sai yar tace mummy kin san may yau da baki nan mummy fati tana ta fada su Anty tana ta zagin su .
Sai dayar tace sai da wanan anty tai kuka ita gwagon mu batai kuka ba tana bata amsa sukayi ta fada sosai.
Na shigo dauke da ture tace dani ashe kunsha kitso ne haka sannu da kokari murmushi kawai nayi na aje mata tana cewa yauwa sannu yar gidan anty na gode.
Na juya na fita dakin har nakai kofa tace don Allah yimin magana da Faiza idan kin fita nace to anty.
Ina fita na nufi dakin faizan tana zaune tana waya na isar mata da sakon anty na fito daga dakin.
Sai da ta gama ta fita daki na koma na kira ummi na don jin lafiyan su da sauran mutanen gida .
Nan take fada min bayan wuce wana ai anyi fada da baba da inna har don bata san inda naje ba sai daga baya da taji take zage zage wai naje yawon dandi zanbarbada wa maza cuta.
Shikuma baba ya kasa kyale ta nan dai abin ya kaisu har da duka abin da bai taba yi wa wata mace ba a gidan nan.
Nace ni kuwa ummi may na tsare ma inna ne a gidan tafi dason in zauna in wulkanta tana min gori ko yaushe a gida ?
Yanzu dai ai ya dauki mataki a kanta don da wuya ta sake maganan ki kuma ai a gidan nan yadda suka kwasa dashi abin ba dadi wallahi.
Nan dai muka sha hiran mu kan matsalan gidan namu da ita karshe nai mata sallama na tashi don gyaran daki sam bani barin dakin da kazanta ko kadan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button