BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,

????????1️⃣8️⃣????????

YAR UWA NOVEL NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KAR KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,

Satin shi guda cur a gidan yana zaune yana jin ya Lilliya takar itake jinyan shi kusan ma a gidan take kwana nai magana ya zundumi ubana tun lokacin ban sake kallon su ba.
Idan dai gari ya waye zan masa ina kwana da yaya jikin idan tana kusa zai amsa min da kyat kamar baya son gaisuwan nawa.
Sai in bata kusa zan samu ya dan amsa min har yasani wani abin in mashi ranan maman biyu tazo duba shi ta samu Lillya mane dashi.
Ya dan ji nauyin hakan amma abin su na yan duniya sai bai nuna a fili ba ya basar ta kasa yin shiru tace wanan fa da take manne dakai haka.
Matar kace ko mai, sai yadan yunkura yana cewa No kawatace take dubani.
Kallon mamaki taimai tace amma kasan hakan ba daidai bane agidan ka wata karuwa zata shigo ga matar ka na sunna da sunan wai tana duban ka ai duk abinda zakuyi ku tsaya iya waje ku yi shi.
Lilliya ta dago kai tai mata wani kallon banza tace ke wacece da zaki zage ni da sunan karuwa ai karuwancin ma isa ne ko.
Tace OK yanzu zaki san ni ko wacece ya dago da sauri yana ce mata will you keep quite.
Take ta har zugo mashi maman biyu batai mata magana ba ta mike zuwa kofa ta sa mashi key ta rike ke din a hannun ta.
Waya ta dauko tai kira dashi aka amsa mata sai lokacin suka kulla da ita Lilliya ta dago tana cewa may zaki yi in bariki ne nafiki iya wa tace bissimillah ina son yau inga iya barikin naki.
Taso taja da ita jacket din dake jikin ta tacire sai uniform din ta ya baiyyana dakatar da abinda tai niyar yi mata tayi tana cewa haka kawai zaki zageni.
Karyan bariki kike yau zan gwada maki akwai wa yanda suka fiki suka riga ki shiga bariki da lasisi.
Mari takai mata naji dadin hakan daga inda nake tsaye a rakube jikin kujera.
Taso turzawa amma karfi ba guda ba take ta murde ta kafin tai wani abu aka fara dukan kofan ta je ta bude sai ga kartan sojojin tsaye a kofa ko wani a cikin shirin shi.
Hakkuri ta fara badawa harda shi munafukin yana cewa madam don Allah ayi hakkuri rashin sanin ke wacece yasa tai maki haka.
Arest her tace da su take ko suka kamata saura shi tace shima a tafi dashi fuskata babu burbushin rahama take maganan.
An fice har dashi a gidan wani dadi ya kamani sai hawaye bata ko tsaya ta kaina ba ta fice gidan itama ta bisu.
Daga inda nake tsaye a cikin fargaba da tsoro na mara masu baya ina tsaye motocin su suka wuce dasu.
Ko ba koma yau maman biyu ta daukan min fansan wullakacin da ake min a gidan don ya gama zagine ke nan a kanta ta shigo gidan ta samay ni daki ina kuka nasan abinda ya kara harzuka ta kenan.
Ina zaune takure a cikin damuwa sai gashi ya dawo duk ya jirkita azotana da yadawo zai hauni da duka da zagi yadda ya saba ne.
Sai gashi naga sabanin hakanan ya dawo ya bukaci ruwa masu zafi zai gasa jikin shi dashi sai kuma dan abinda zaici.
Yana zaune bayan ya fito wanka ga abinci a gaban shi yace Safiya ina daki na amsa masa na fito kujera ya nuna min da hannu alaman wai na zauna.
Sannu a hankali na kai zaune saman kujeran ina fuskantar shi tare da sauraren abinda zai fada min a lokacin.
Yace kin dai ga yanda wanan matar suka yi a gidan nan ko na dago kaina a hankali ns dubeshi ya tsare ni da idawan shi.
Na sake dukar da kaina kasa ba tare da na amsa mashi ba yace yanzu dai ba wanan ba abinda nake so dake shine.
Kiwa ita madam din nan magana a sake Lilliya don ba karamin tsaro sukai mata ba yau kawai duk ta jemay saboda tsaro da horo irin nasu na sojoji.
Ban san cewa girman ta da kimarta yakai haka ba sai yau din nan da na gani ke kaidace zakiyi magana a saki Liliya da sauri inba haka ba abin zai jawo min matsala sosai gani zaune gida banda lafiya.
Banyi magana ba naji yana cewa umurni na baki ba son jin raayin nake so ba ki mata magana a sake ta.
Na nisa nace shike nan kiran yace eh shike nan nake so ki fada mata a sake ta.
Na mike ina ce mai ai da kai kai mata magana zai fi don zata fi jin maganan ka sama da nawa do ni ban san ta inda zan dauko mata zancen ba.
Rashin mutunci tai mata ta dauki mataki ta dauka irina ne da kuke wa son ranku a gidan ku taka ni iya son ranku a zauna lafiya.
Ni banga laifin maman biyu ba da ta dauki mataki ga marasa mutunci irin ku wayan da basu san darajan aure ba.
Ke ya isa ya dakatar dani ta hanyan daga min hannu shi yace umurni fa na baki in kina son kanki da lafiya gidan nan kiyi abinda na umurce ki da shi.
Fuskan shi babu alaman sauki gare shi don haka na juya na tafi kawai ba tare da nai wani magana ba.
Da safe nai sammakon zuwa gidan maman biyu nayi sa a tana gida kasa na zube ina mata godiya ga hawaye na zuba a idona.
Ta ce assha safiya tashi tashi don Allah may ye hakan ai dole a tausaya maki don kinyi karanta da irin wanan rayuwan.
Dudu fa baki kai ashirin ba amma kike fuskantar wanan bahangon mijin naki mai rayuwan kazan ta.
A gaskiya dani wata ce a cikin zurian ku da sai ince a raba wanan auren don baida alaman nadama ko gaba duk kaga namiji yakai haka alamarin akwai ban tsoro cikin sa.
Nace yanzu ma shi ya turo ni akan nazo na baki hakkluri a sake ta wai idan ba haka ba zan gane kurena gare shi.
Tace da sauri kinji ba na fada maki ai baida nadama ko kadan ai dana sani abarshi can shima amma sai na tausayama luluran da yake ciki.
Gaskiya naso yin wani abu akan zaman nan naku amma sai ina ganin kamar ciki ne dake .
Nai saurin dagowa ina duban ta a gidimay nace ciki kuma anty tace tabbas indan ba hasashe nake yi ba kina da shigan ciki.
Gabana yai mugun faduwa tace yaushe ne rabon dakiyi jini a tare dake ?
Nai shiru ina nazari can nace gaskiya wata uku kenan tun da nayi ina gida ba sake yi ba.
Tace shit,
Zargina ya tabbata gaskiya akanki na dade dama ina zargin hakan amma zan sa aimaki test a gani.
Yanzu ki ci abinci zanyi waya a sake ta don ba imani ke ga irin su ba tare suke da yan daba sai dai da yake zamu kafa hujja akan in wani abu ya samay ki nan da shekara biyar itace.
Naga tasa akawo mata abinyin test ta auna fitsari na ya nuna positive alaman ina dauke da cikin wata ukun.
Nai bakin ciki da jin wanan labari kwarai da gaske munyi sallama zan tafi take cewa in kwantar da hankalina killa sanadiyar cikin nan in samu sauki a gurin shi don wasu maza nason yara.
Ta dan bani shawarwari masu mana ta cika ni da abin arziki na bar wurinta zuwa gida zuviya ciki da bakin cikin labarin cikin dake jikina.
Yana zaune ya kura ma tv ido na shigo bako kin dawo sai cewa yayi yaya kin samay ta a gida ?
Nace eh na samu dama zata sa a sake ta saboda kai koda banje ba din tace abin da tayi matane ya bata mata rai ai.
Bai yi magana ba kuma naji ta yadauki waya kowa yake sanar ma zancen sakin nata oho nadai ji ya dade yana waya din.
Nikan abinda ya damay ni ya damay ni zancen cikin dake jiki nakewa bakin da nadama ina tausayawa rayuwan da abin cikin cikin nawa zai taso ya ga ubanshi nayi a duniya.
A haka ma ba tarbiya yaya za a ce aiwa yara tarbiyan rayu kirikiri bani shiga mutane duk da bariki ana cewa ba ruwan wani da wani .
Ina ganin barikin dane bana yanzu ba don wata mace da tazo kitso ya dawo ya shigo murtun compound din tace .
Na dis yeye man you marry , .
Dis man too dey follow women .
Murmushi nayi mata kawai ban bata amsa ba sai wata da take zaune ne tayi mata magana da cewa hakana fa ba kyau.
Sai tayi shiru damuwa ya isheni da fargaban halin da zan shiga nan gaba a garin mutane .
Sai wuraren sha dayan rana aka sako lilliya daga hannun sojoji bayan tasha dan banzan wahala.
Haka ya daure ya fara fita tun wanan ranan baya zama gida yana wurinta acan kafar ta karasa warkewa a hanya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button