BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,

????????2️⃣7️⃣????????

YAR UWA NOVEL DIN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , , , , , , ,

Yaya Saadu yana tuki yana min sannu yana jin wani tukuki a zuciyar shi gamay dani, yana ji kamar ya rabani da wanan ciwon gaba daya a jikina.
Tausayi nake bashi jina yake tankar yar uwar shi da suka fito ciki daya ba komai ya yasa yake ji dani ba sai irin girmama shi da nakeyi.
Wanda ko wayanda suka fito ciki daya basuyi mai yadda nake mai ya lumshe idon shi tare da nisawa.
Yace a ranshi Safiya nai maki alkawari zan dinga kula dake muddin ina raye insha Allahu zan baki kulawa daya dace.
Baba ne ke magana dashi amma baiji shi ba sai da baba ya sake maimaita maganan shi yaji shi.
Saadu kayi hakkuri kasa imani da addua a a ranka nima abinda nayi nayi nadamar shi ban wa yarinyar nan adalci ba.
Wallahi ban san abinda dan uwanka da mahaifiyar ku kuntatawan da suke wa yarinyar nan yakai yakai haka ba.
Ya nisa yace baba abinda ya faru ba wanda ya isa ya goge shi sai dai tabbas tun farko anyi kuskuren aura mata shi don sanin ko waye Ahmed din sam bai dace da kamilar yarinya irin Safiya ba don sani ko shi waye da akayi.
Yace yanzun haka karuwan da ya saki Safiya a kan ta ta gudu ta barshi bayan ta gama yashe shi kaf bata barshi da komai ba.
Shima yanzun haka din ya fara jinya don ciwon nasa ya fi na Safiyan nisa sai yanzu ne wai mummy take data sani dashi.
Bayan a lokacin da yake miyagun halayensa ta kasa tankwara shi ta dauki son duniya ta dora a kan shi.
Itama karuwan naji ance takai kwance a inda take tana bukatan taimako.
Ina zaune a bayan mota ina jin su na lumshe idona don bakin ciki sun cuce ni sun illanta min rayuwa na.
Mun isa garin muka nufi asibitin direct nan ya bar mu cikin mota suka fita dashi da yaya sani zuwa ganin likita.
Gwago ta ga mai ruwa ta kirashi ta saye muna tabani nasha baba na kallon yadda nake shan ruwan da kyat yana min sannu Safiya.
Gwago ne tace Allah ya isar maki yar nan ya saka maki da gagawa sim cuce ki sun illanta rayuwanki ga banza.
Baba yana jin ta hawaye yake na nadama yana gogewa yace gwago banyi wanan hadin da wata manufa ba a rayuwa na.
Sai don zumunci ya kara karfi a ysakanin mu iyayyen mu duk abu guda suke ta uwa ta uba shine da tazo da wanan zancen naga dacewan shi nayi.
Yaya Saadune suka dawo dauke da keken da ake sa maralafiya yace a kamani asa sama yaya sani ya ciciboni ina wai ya dora a keken.
Wani daki ne muka nufa ashe likita ke ciki ya dan yi min tambayoyi su yaya da baba ke amsa mai yai rubutu ya bayar yace zasu dan kwantar dani inda masu irin case dina suke in sha magani na kwana biyu a gani.
Aduniya ban san irin godiyan da zan ma bawan Allah nan ba sai dai ince Allah ya biya shi da alherin sa.
Nan take ya sayo magani da ruwan da za a kara min da abubuwan gina jiki kuma yace ba zai tafi ba sai yaga yadda jikin nawa ya kasance.
Baba kuka yake yana mashi godiya yace baba komai nai wa Safiya kaina nai wa don yar uwata ce ta jini.
Na samu kulawan da ya dace dani ashe ciwo in ba a dace da magani ba sai ai ta wahala dashi.
Don yanzu na rage yawa jin abinda nake ji a jiki na so sai sannu a hankali nake jin sauki yana shiga na.
Kwana biyar suka sallamay mu daga asibitin, har lokacin muna asibitin da yaya Saadu da yaya sani.
Sun bani magani amin register zan dunga zuwa ansan magani a wurin su tare da fada min mata kan da zan bi don kare kaina da sauran alumma da nake zama da su.
Aka bamu sallama na dawo gida da dan karfin jiki na sai da yaya ya sawo min abubuwan bukata na rayuwa yai muna sallama ana ta yi mashi godiya ya kama hanya.
Yan gidan mu na dan ga dan canji a wurin su yaran mama sun rage tsanar da suke min amma dai suna kyamana don in na taba abu sai an wake ko a yar a bayan idona.
Kauna tace ta fada min haka sai dai nai murmushi kawai na ware kayan amfanina a gidan ban amfani da kayan kowa har da na su ummi na don na nema masu mafita.
Da sannu ina warware wa na fara harkan kasuwanci na da mutane da farko suna kyamar saye daga baya kuma suka fara saya.

* * *
Yaya Saadu daya bar wurin mu gida ya koma direct tun da ya iso jikin su ya basu cewa bai cikin dadin rai.
Sai da ya huta yai wanka yadan taba abinci kadan ya tashi ya fice gidan yaya Ahmed ya nufa.
Ba kalman dake mai yawo arai sai da ya shigo dakin ummi ina kwance na dago nace dashi yaya ya Ahmed ya cuce ni
Ya illanta min rayuwa ya kashe ni da yarinta na ya mai dani abin tsoro a cikin yan uwana da gari sai ya runtse idanuwan shi.
Yai sallama yana ciki kwance ya taso da kyat ya bude kofan gida yaya saadu ya shigo ciki yana mai wani irin kallo.
Zama yayi yai shiru ba tare da yai magana ba shima wuri ya samu ya zauna yana kallon shi don yasan magana ya kawa shi .
Don tun da na bar gidan ba sake zuwa gidan ba sai yau da yazo ya tunkare shi akan magana na.
Ya dan dago ya gyara zaman shi dakyau baiyi magana ba saida ya dan furzo da iska daga bakin shi ya numfasa yace.
Kana da labarin Safiya bata da lafiya har ciwon yai tsanani sai da naje na kaita asibiti, yace dashi ban sani ba, banda labarin ta tun tafiyan ta inbada ta haihu kazo kafada muna ba, sai yace dashi
Ahmed ka cuci Safiya ka illanta rayuwan karaman yarinya a banza saboda son kai irin nata ka zuba mata kanjamau tana ta wahala a rayuwan ta.
Ahmed din yai mai wani kallo na tambaya sai yace dashi na illanta ta kamar yaya ?
Yace kasan Safiya tana dauke da HIV kuma kaika saka mata shi don dai kai kafi kowa sanin kamilar yarinya ce ita.
Ahmed din yace tasan dai inda ta samo abinta don dai ni banda komai normal nake kowa ya sani.
Saadu yai saurin cewa normal kake kamar yaya aiko makaho ya lalaba yasan may kake ciki.
Sai yace dashi sheri zakai min ko may ?
Babu sheri anan .
Don mummy da mahaifin safiya sunyi kuskuren aure maka kamilar yarinya kamar safiya don sun san halinka na boye suka aure maka ita hakana.
In ma shi mahaifin nata bai sani ba ita mummy mu ta sani saidai ta boye masu ne.
Ahmed ba yadda ban yi da kai ba ns baka shawara ka gyara rayuwan ka ka nisan ta kanka da fasikanci.
Ba abinda ya zama ma dan adam dole may kake nema gun mace kai da Allah ya hore ma mace yarinya karama a gida.
Sai da na fada ma wanan matar da ka aje a gida ba alheri bace gare ka amma kaki ji yanzu gata ta sa ka cuci yar mutane.
Ya dafe kai gami da lumshe idanu yana tunane a ran shi yana hango irin wahalan da nake yi da ciwon a ranshi.
Ya hango surana da muryana da irin karfin halin da nake dashi wurin turzawa sai kuma muryana idan ina son abu da tsabta na.
A take ya ji jikin shi ya mace wani na dama da tsoro ya shige shi amma sai ya dake yace wa kanin nashi.
Wai may ya damay ka da nine rayuwan ka ko nawa kuje can kai da ita ku nemi inda ta kwaso cutan ta.
Please ka rabu dani don Allah da zancen wata safiya can kwakwalwata yana son hutu dan Allah kazo min da wani zancen ka na bazanza.
Yace okay haka kace ya mike ya fita zuciyar shi kamar wuta yake jin shi ba abinda yake tunawa sai halin da ya barni ciki.
Gidan su ya koma inda ya samu mahaifiyarsu da zancen, tun shigowan shi ta sha jinin jikin ta don tasan da abinda ke damun shi.
Sai daya zauna take cewa dashi ina kafito ne aikai ma abin kari baka nan ka fita.
Ya nisa yace da ita daga wurin Ahmed nake mummy kin san Ahmed ya cuci yarinyar nan safiya a rayuwan ta .
Tace may ya faru kuma da Safiya din zancen wai har yanzu bai kare ba a gare ka kana bin dan uwanka da maganan ta rayukan ku na baci ga banza kasan fa yace bai mai da ita.
Mummy yazu wake batun komawan ta bayan ya illanta ma yarinyar mutane rayuwa har abada.
Wani kallo taimai nason jin ba a sin maganan shi yace Safiya fa HIV ne gare ta kuma ba kowa ya samata ba shine.
Innallilahi ta furta da karfi tace H may yanzu kana nufin har shi Ahmed din yana dashi komay ?
Yace ai yasan yana dashi mugu shiyasa ya sake masu ya don kar asirin shi ya tonu.
Hannu ta fara tafawa tana salalami tana cewa wai ta shiga uku ta lalace Ahmed na da kanjamau ko may ?
Yace mummy Ahmed kawai kike ji mawa ita diyan mutane da kuka cuta fa ita ba abin tausayawa bane ?
Sai ta kama inda inda tana cewa ai dukkan su abin tausayawa ne itama ai dole a tausaya mata.
Yace mummy dake da mahaifin yarinyar nan kuna da kamisho cikin ciwon yarinyar nan.
Amma shi mahaifin da yasan kun cuce ta ai kuka yake kuma yana nadaman abinda kuka kulla sai dai ko kadan bai kufulece kiba.
Amma ke gaki yanzu dan ki kawai kika sani kika damu da damuwar shi ita ko ko oho ?
Idan zaki kirashi ki masa magana yaje ya duba diyar mutane tun wuri ki masa.
Ahmed din bai shigo ba saida yamma ya shigo rai a bace shi aladole an bata mashi rai.
Nan ya zauna da uwar ta dauko mai zancen da cewa abinda naji da gaske ne ko karya ne yazo ya fada min.
Nan ya shiga fada wai Saadu na binshi da mugun nufi har yana lakaka mashi mugun ciwo.
Tai ajiya zuciya tace yanzu naji magana amma yazo ya tayar min da hankali ga banza ya hanani sukuni a rayuwana duk yinin yau ko ruwa ban sha ba.
Mummy kazafi yake min ta san ida ta dauko cutan ta can ni bani da masaniya akan haka.
Uwar ta hau ta yarda da maganan shi nan ta shika fadin mugun zance akaina da mahaifana yana tayata fadi.
Sun yanke yiwa yaya Saadu kaca kaca kan maganan da yake so ya dora wa dan uwan nashi wai yana son ya bata mashi suna ga banza.
Ya shigo sunyi kaca kaca dashi a gaban mahaifiyar tasu tana tayashi zagin shi yace dasu OK haka kukace .
Time will soon come da gaskiya zata bayyana kan ta indai ana boyon komai ba a boyon ciwo ai muje zuwa ni daku.
Macucin banza da wofi kawai kawai ka cuci yar mutane kazo kana wani kamay kamay azzalumi banza da wofi sai Allah ya tona maka asiri ai.
Yace dai naji kuje can ku nemi wanda yasa mata cuta idan ma kaine ka fito fili kafadi yafi don naga zakewan ka yayi yawa akan ta dama.
Wani irin shock ya kama shi ta juyo yana duban dan uwan da mamaki sai kuma yai murmushi yace ni ba dan akuya bane irin ka.
Ina dai kokarin sauke hakkin da kai ka kasa saukewa ne akan ta amma baku ganewa sai lokacin ku gane gaskiya inyayi.
Ya fice ya basu wuri bai kara shigowa gidan ba har ya tafi bai koma wurin aikin shi ba sai da yaje gidan maman biyu ya sanar da ita halin da nake ciki.
Da taji hankalin ta ya tashi sosai ya kwantar mata da hankali da cewa ya kaini asibiti yanzu ina samun sauki an daiyi arziki cutan baiyi nisa sosai ba aka tare shi.
Ranan haka ta wuni a cikin bacin rai tana ta tsine ma Ahmed din da uwar shi ta ma kasa kirana don in ta kirani ma may zata fada min banda karin tashin hankali.
Sai dai ta kasa daurewa bayan kwana biyu ina zaune daki da ummi wayana yai kara na dauka na ga itace take kirana.
Na dauka tare da fadin Anty kwana biyu kina a raina ban samu kiran ki ba banda lafiya ne.
Asanyaye tace safiya naji komai yayan ki yazo nan ya fada min halin da kike ciki Allah ubangiji ya isar maki.
Sai na kama kuka tace bari kuka haka Allah ya kaddara da rayuwanki Allah ya nufe ki da rayuwan BAHAGGON AURE.
Komai da bawa ya gani yana cikin littafin sa rubuttace ne ga ubangiji dama sai dai muyi fatan Allah ya baki lafiya.
Nace amin anty tace ki kwantar da hankalin ki ki sha magani kada kiyi wasa da sha magani sosai don kada cutar yayi galaba a kanki.
Nan nake jin yadda yaya Saadu suka kwashe da yaya Ahmed din da uwar su tace min barsu ai Allah ba azalumin kowa bane.
Da sannu gaskiya zatai halinta in sun ce su mahainta ne ciwo ai ba a boyon sa shi zai baiyana kasa agani watarana.
Ta dade tana lalashina ina kuka tace ina ummi nace gata a kusa dani tace inba ummi waya su gaisa.
Nabata wayan suka gaisa tai mata jajen akan abinda ke faruwa tare da kwantar mata da hankalin ta takumace duk lokacin da muke da damuwa mu tutube ta zata taimaka muna.
Nai sallama da ita har take tambaya na sana, a ta nace yana nan ina yi tace to karki daina shine zai tallafa maki kina samun dan kudin sayen abinda zai gina maki jiki kiji ko nace na gode kuka ne yaci karfina na kasa magana na kashe wayan ina tunane a raina.
Bayan mun gama wayan na dade ina kuka ina tunane a raina karshe na hakkura na kyale na barwa Allah komai shi zai mun mafita da yardan ubangiji.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button