BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,

????????2️⃣1️⃣????????

YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,

Tun muna jiyo maganan su sannu sannu har suka fara daga murya mudai har barci ya kwashe mu bamu san lokacin da suka kwanta ba.
Shiko yaya saadu gida ya tafi ya samu mahaifiyar da yanzu jikin sai a hankali sun kammala cinikin dare habiba na kirga kudi da sukai ciniki.
Dinban habiba yaya yace munafukan banza da wofi kizo ki zauna da yar uwar ki kikace baki da lafiya ne.
Yanzu may kike yi anan zatai magana ya dago kamar zai make ta yana cewa duk dai abinda kawa wani kasani sai an rama mashi.
Mahaifiyar su tace kai kada kazo fa kace zaka samin yara gaba da hitina kan safiya.
Idanuwan shi sukai jawur ya kalleta yace mummy halinda yariyan nan ke ciki ba wanda ya ja mata sai ke saboda son kai,
Kin san danki yafi karfin ki kema da kika haifeshi baki iya shi rayuwan mu ba daya ba da tashin arewa amma kika rufe ido kika nace sai anyi.
Mummy ansan mukadari ne ba wanda ya isa ya goge shi amma kuma sai ki saka ido a kanshi aike kika haifi abin ki.
Ajiyan zuciya tayi wani bakin ciki ya tokare mata zuciya, tace Saadu, nayi kuskure da na dauka Safiya idan ta auri yayan ku zata gyara rayuwansa na jefa rayuwan yarinya cikin kunci da wahala.
Ni kaina nasan ba aiwa yarinyan nan adalci ba amma ba yadda na iya dashi sai ya ce zai dauki mata akan magana na.
Gashi mahaifinta dan uwa na gari ya dauki amana ya damka a hannu na don ba da halin zuwa gidan su gun mahaifanta takai kara uba yace bai yafe mata ba.
Yaya saadu ya katse ta da cewa safiya tana cikin kunci da bakin ciki wanda duk wanda ya ganta yana da imani dole ya tausaya mata ace ana horon mutum yunwa saboda Allah fa.
Sannan mummy keda kanki kika bashi goyon bayan a fitar da cikin da jikinta keda kanki mummy mu mai yasa baki fitar da cikin mu ba da kika samu.
Wani kallo ta watso mai bai damu ba ganina acikin kunci da bakin ciki yafi komai bata mashi rai yace yanzu gashi tace zubar da cikin zatayi ta huta da wahala.
A razane tace zata zubar kuma da cikin yace eh to ba abinda kuka zaba kenan ba dama itama yanzu shiyafi mata sauki zubar da cikin.
Mummy zan inya hana wani abu mummuna da zai faru nan gaba kema kiyi abinda abin da ya dace akan zaman nan nasu amatsayinki na uwa gare shi.
Don sai karuwan nan ta bar gidan nan wallahi ko ta halin yaya, ya juya zai fita daga dakin a hasale tace saureren nan Saadu kaji.
Ban son kana shiga harkan gidan dan uwanka haka nan kabarshi shike da gidab shi da su.
Ya zamana na karshe kada ka sake zuwa mai gida katayar mashi da hankalin iyalin shi.
Ya juyo ya kalle ta yayi dariyan takaici yace mummy da kun hana ni na yarda nabar zuwa don biyyaya a gare ku.
Amma yanzu na fahince ku bakin ku daya ne akan yar uwata muddin Safiya tana gidan shi bazan taba fasa zuwa gidan nan ba.
A wane dalili zan nisanta kaina da yar uwana saboda karuwa ko may, zanyi haka wanan karon ba zan sake dauke kafana a gidan ba indai safiya tana ciki.
Muddin ina raye ina numfashi ba zan sake bari a kuntatawa rayuwan safiya ba, danki yana danne mata hakkin ta batada matsayi da yancin a gidan shi amma duk baiyi laifi ba
Mummy kin dauki yariya karama kamar safiya kin aura ma mutun irin Ahmed, ya dauko karuwa mata karuwa a gida ya hada tada ita sun taru suna kuntata mata kice wai baki sani ba.
Duk kece sillan lalacewa rayuwan rayuwan mu haka mummy yarinya na zaman ukuba a hannun danki kice wai kada a taimaka mata, duk kece mai kawo matsala a tsakanin mu mama.
Yana gama fadi ya juya ya fita yabar gwago cikin kunan rai ta bishi da kallo har ya kule tace Saadu kao baka san uwa da soyayyan dan ta ba.
Inda zaka bincika kaga yadda nake cikin damuwa da bacin rai akan yaran nan da baka furta hakan ba inda kasan nauyin da maihaifin yarinyar nan ya danka min banda yadda na iya ne.
Baka san nauyi da rikon amana kedashiba da matukar wahala duk abin nan ina sane dasu amma son dana ya rufe mun ido.
Shiko dan waje ya koma yana jigina jikin shi ga mota yana tunane ya dinga kuna wiwi yana zuka yana wa kwakwalwan sa caji tare da neman mafita akan matsalar mu.
Ya nisa yana cewa a ranshi hakika Safiya ke yar uwata ce ta jini kuma mata ga dan uwa na zan tabbatarb kin kasance cikin farin ciki zan fuskaci duk wanda ya nemi ya kawo maki kunci a rayuwan ki.
Burin mahaifinki akan hadin auren ki shine da dan uwana yaga an hada zuria mai dorewa a tsakanin shi da yar uwar shi amma dan uwana yana son yaga rushewan wanan alakan saboda rayuwan duniyanci daya dauka.
Ya Allah ka tabbatar da farinciki da kwanciyan hankali a rayuwan ku kar zumunta ya baci a sanadin auren ku.
Iya sani na mummy bata da gidan zuwa a arewa wanda ya wuce gidan mahaifin Safiya don ko sako ne ta gareshi take turawa a sayo mata abu a aiko dashi nan.
Haka dai ya kwana yana yawan tunane barkatai da samo fita ga matsalar mu .

* * *
Fitanan sune ya farka damu daga barcin safe da muka samu mukeyi a gidan nida Sadiya.
Fada suke yi sosai shida ita hakan yasa mu fitowa da sauri dakin mu danbe suke yi a tsakanin su.
Suna ta faman fashe fashen kayan falon da suke fadawa da gani har sadiya ba mai iya raba su don sun fimu karfi.
Sun dauki lokaci suna abu guda saida sadiya takira yaya saadu yazo ya raba su ta kwashe kayan ta tana mai zagin kaskanci irin na yan duniya.
Wani magana da ta fada sai da yaya saadu ya kadu bayan tafiyanta ne sadiya ta taimaka min don mu gyara gidan mu mai da komai inda yake.
Kuka nake ban iya aiwatar da komai ba a lokacin sai gasu sun shigo gidan da shida dan uwanshi.
Sun zauna suna fuskantar juna yaya saadu yace dashi matan bariki dama haka suke su raba ka da ta kwarai su kuma daga karshe su guje maka.
Kamayi arziki bata kai ga kore maka mata ba ta tafi ya dago ya kalli dan uwan nashi ai ba tafiya tayi ba barazana ne kawai.
Yaya Saadu yace yar bariki ne zata iya dawo ma rayuwana in yau ta ga dama ko gobe sai dai ka sani.
Yarinyar na Safiya yar uwan muce jinin mu ne ita kamar yar cikin mummy take a wurin mu infact dai kasan wanan auren naku anyi shine don kara zumunci.
A ganina bai kamata ace abinda iyayye sukai maka gata akan saba shikake wullakantawa.
Na tabbatar da mahaifin yarinyar nan na kusa ko yasan halin da yarsa take ciki da tuni ya raban auren ku da ita.
Ya kamata ace Safiya ta samu kulawan ka fiya da komai a gidan ka bata isa ta hanaka barikin kaba amma kabata kullawa yadda ya dace don kauce ma shiga hakki.
Nasan da mahaifinta yasan halin da yarsa ke ciki a gidan ka da duk wanan abin bakai ga yinsa ba.
Don basu san halinka na boye ba mummy ta rufe massu kokai waye ta aura maka karamar yarinya da yaci ace yanzun tana karatu ne.
Please Ahmed ka gyara rayuwan ka duk wani abinda kasan yana kawo nakasan rayuwan ka nesance shi.
Ba abinda ya zamo ma dan adam dole a rayuwa mussamman abinda zai nesantakan da ubangijin ka yazama dole ka yakeshi a ranka.
Musamma giya da mata ba alheri bane ga rayuwan dan adam ba dole bane ba kuma inda yazama ma dole sai kayi shi.
Don Allah bros ka rabu da wanan rayuwan ka rugumi matarka ka rike yarinyan nan amana zaka ga yadda rayuwan ka zai canza duk wanda ya samu mace kamar safiya yayi saa a rayuwa shi ga tsabata ga hakkuri da biyyaya.
Ya sa hannu ya dafe kanshi kamar maganan yana shiga zuciyar shi can ya lumshe idanuwan shi yana hango kyakkyawan fuskan na da suran da Allah yaimin da natsuwa da hakkuri.
Yace kai baka ko gudun ka dauko maku cuta ka manna wa yar mutane matar nan fa baka san iya mutanen da take hurda dasu ba har wata kasa take zuwa.
Yaji zuciyar shi da jikin shi yai sanyi saboda maganan da dan uwanshi ke fadi gaskiya ne ko abokan shi sun sha fada mashi hakan.
Gaba daya jikin shi yaji yai sanyi amma kuma yasan abu mai wuyane ya iya rabuwa da lilliya ko ya rabu da kowa bai iya rabuwa da ita wasan dadi.
Ya kalli yaya Saadu yace na gode daka tunarta dani wasu abubuwan da na manta dasu a rayuwa.
Yaya saadu bai tafi ba sai da ya tabbatar da ya daidata komai a tsakanin mu yabar gidan .
Abinda bai sani ba shine na kudiri aniyar kwatar kaina daga gare su bazan kara yarda da irin cin fuskan da yake min ba agaban matan bazan shi da yake kwasowa.
Kwana biyu kamar komai ya lafa sai dai a raina nasan kwanton bauna yayi kawai na kwana biyu.
Yana kawo min abinci kai da kai kuma idan zai fita zai sallamay ni kuma idan ya dawo nakan taso daga dakina ko nabar abinda nake yi nazo na gaida shi da dawowa.
Wata rana zai fita na tambaye shi zuwa wurin maman biyu indubata kamar ba zai barni in tafi ba sai dai kuma yace kada in dade.
Na gama shiryawa na rufe gidan na kama hanyan gidan ta nayi saa ta dawo wai ashe bata garin duk wanan dadewan da tayi.
Take tambaya na ko nazo bata nan ne sai nake fada mata irin kullen da yasani da dauko Lilliya da yayi ya kawo gidan.
Da irin horon da na sha a wurin su har yaya Saadu yazo ya kwace ni a hannun su daidai lokacin da nake ganuwan shan wahalan su.
Ta nisa tare dacewa safiya wanan mijin naki bariki ta aure shi rashin sani yasa mahaifinki ya nace da ki zauna dashi hakana.
Amma wanan da kike gani tuban mazuru yai maku kawai may yuyuwa ya canza mata gidana suna haduwa baki sani ba.
Nace inma gida ya canza mata baida may ni ba don ban gani ba abinda sukeyi bisa ga yadda suka zauna min gida ana iya shege a gabana.
Nifa anty yanzu cikin nan ne kawai matsalata badon ciki ba da duk abinda baba zai mun sai dai yai min ba zan zauna ba.
Sai dai nakan tuna furucin baba sai jikina yai sanyi da yake cewa indan aurena ya mutu in tabbatar da zaman ummina ma ya kare a gidan shi.
In badon wanan ba aida tuni na gudu na koma ga iyayyena ko don maganar kine wallahi don da dan uwanshi kemai magana ya rabu da Lilliya cewa yayi.
Wai abinda yasa ba zai rabuda itama ba sun jima tare ni tun baida komai suke tare tabar maza da yawa take zaman shi shi kadai.
Wai cewa yayi har musulunta tayi saboda shi saida sukai alkawari da ita cewa bazai wullakantataba kuma ba zai taba rabuwa da ita ba shi dalilin da yake duba.
Sai dan uwan ke tamabayan shi yana ganin Lilliya ta musulunts ne matar da ko shiga irin na musulmai batayi kuma ita bata daina hurda da wasu mazan banza ba har yanzu.
Kai amma mijin nan naki wani irin soko ne wallahi indan ka gan shi a fuska kamar mutumin kwairai inji anty.
Tace yanzu shi baiji kunyan fadar wanan dalilin nashi na bazan ba shi watau baiyi tunanen harcin da iyayyen ki sukai mashi ba sai na wata matar banza can.
Nace ai haka dan uwan ya fada mai idan yana son zaman lafiya da kwanciya hakali sai ya rabu da matan bariki.
Sai cewa yai mai wai bayajin zai iya rabuwa da lilliya ko ya rabu da kowa don baida matsala da ita tana binshi shi sau da kafa tana mashi komai ko wanan akasi aka samu suka sami matsala.
Kanin yace mai aiko ya zama dole ya rabu da ita don farin cikin gidan shi nace kin san may ya cewa kanin ?
Wai mau zai sa kanin na shiga mai harkan shi wai ai lilliya ma tarsa ce don haka zai zauna da wacce ya ga dama a cikin mu ya saki wacce yake son saki ko kuma ya zauna da mu dukkan mu.
Sai cewa yayi dan uwan ya rabu dashi kar ya caja mashi kwakwalwa don yana bukatan hutu tare dashi.
Na kinga kenan bazai iya rabuwa da ita ba ni ko yana iya rabuwa da ni inya so.
Haka dai dan uwan ya lalaba shi har suka samu suka rabu lafiya dashi ya wuce in ba haka ba ranan nasan ba karamin tashin hankali za a yi ba a tsakanin su.
Tace kin ga ni yanzu so nake ki kwantar da hankalin ki ga komai ki kula da kanki sosai don ki haihu lafiya.
A hankali na daga mata kai alaman na gane ta kawo kudi masu yawa ta bani da zan koma tare da kwantar min da hankali.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button