BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , , ,

????????2️⃣9️⃣????????

YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,

Wurin motar muka nufa gaba dayan mu saadatu na kwace a ciki sheme kamar bata numfashi kuka muka saka a lokaci daya.
Dayan dan sanda ke fadi ba kuka zakuyi ba ayi niya akaita asibiti tun lokaci bai kure ba a take baba da yaya sani suka fada motar da inna.
Suka nufi asibiti da ita har lokacin mu ba mu san may ya samay taba asuban fari baba ya dawo gida rai a bace.
Da mukaji shigowan shi lokacin mun tashi muka firfito waje mama ne ke cewa malam lafiya may ya faru da Saaden ne ?
Cikin takaici yake fadin fyade akai mata wai kuma bata san ko su waye ba tadai ce sunkan zo cin kasuwa su sai sana ar ta.
Kowa ya dafe kirji da firgici a cikin mu ta sake tambayan shi da ta farfado dai ko yace a takaice da ta falka yanzu sai dai bata san inda take ba.
Nan ya shige ya barmu a cikin tashin hankali ba kwanta ba da mukai sallah cikin kayan abinci na na diba na hada masu abin karyawa.
Na gama da wuri muka isa asibitin tana kwance sharkaf kamar bata da rai Inna na zaune a gefen ta cikin tashin hankali.
Munyi mata sannu da yaya mai jikin tace da sauki na bata abinda nazo dashi nace su mama suna nan tafe.
Maganin da likita ya rubuta ake neman kudin saye baba yace baida shi inna kuma tace dama dan abinda ke gare ta ne nan ta juya dashi sukai sana a.
Na bude post dina na kirga kudin na bayar sai lokacin aka sawo magani da ruwan da za a karamata.
Anyi mata allurai da sauran abinda ya dace a taimaka mata dashi bayan kamar awa daya ta farfado da kuwan wayyo inna zasu kashe ni.
Tana fisge fisge nan dai muka taru muka taushe ta nurse tazo ta kara ba ta allura sai aka samu tayi barci.
Ranan dai asibiti muka wuni ba dadi kafin wani lokaci labari yabi gari mutane sai shigowa suke yi dubata.
Suna asbitin kafin a sallamota sai ga yan gidan mijin da zata aura wai a basu kayan su yace ya fasa dama itace ta biyu zata shiga.
Wani sabon tashin hankali kuma nan suka shiga hayaniya da su mama tace aiko baku da imani kwa tsaya har a sallameta dai ko koma may ye sai ayi shi hankali kwance.
Nan dai aka samu suka tafi suna bakaken magana wai dama ai shi yaji yagani a kanta ina ba haka ba me zaiyi da ita ma.
Andai samu an lalaba su suka tafi baba ya shigo gidan ake mayar mashi ranshi ya baci yace ai sai su bari inda ta dawo ita data karbi kayan su sai ta mayar masu da abinsu.
Inna na can labari ya samay ta nan ta sa hannu akai tana kuka wai so suke su tozarta ta in bashi ba ai wanan abindaya faru da yar ta kaddara ne kwai.
Ji fa inna na kalleta a raina nace ashe tasan akwai kaddara shine ni taki yarda da nawa kaddaran da yazo min.
Na yar tane abin yarda ke nan mu dai hakkuri muka bata kawai muka bar dakin muka koma waje muka zauna.
Washe gari aka sallamo su suka dawo gida an basu wata uku su koma ai mata awon ciki dana HIV nan hankalin inna ya sake tashi sosai tana kuka tana fasin Alah ya tsine ma wa yanda sukaiwa yarta fyade.
Da yamma bayan sun dawo gida tana cikin jimamay maganan likita sai ga ya gidan mijin na saade sun dawo wai sun samu labarin an sallamata ta dawo gida shine suka zo karban kayan su.
Nan suka hau da inna tace baza ta bayar ba aiba ita tace ta fasa ba don haka bata yarda shi mijin yace bai yi ba sai dai in sherin yan uwan shine.
Suka tafi basu gane komai ba nan suka barta ta na halakatai a tsakar gida wai basu da imani yarinya na fama da abinda ya samay ta zasu zo masu da wani fitina kuma.
Mu dai muna daki muna sauraren ta sai baba ne ya shigo yace da ita don may bazata basu kayan su ba tun da sunce sun fasa.
Nan ta shiga kamay kamay Ummi tace dani wasu kaya kayan da ta sayar wasu kuma yarinya ta sa ajikin ta.
Nace ashe akwai cakwakiya don naga mutanen basu da alaman mutunci tare dasu.
Ummi tace na dai kallo kawai ai mun yi imani da mukai mata jajen abinda ya faru in wasu ne aiko kallo bata ushesu ba.
Da itace ba abin da zai sa ta kalle mu dama haka Allah yake ai yanzu in tana da imani tayi ai ta daina aibanta kin da takeyi a gidan.
Murmushin takaici nayi nace badai inna ba ai laifi tudu ne katake naka ka hango na wani watarama kiji tayi min fade in halin ta ya tashi.
Ummi tace dako tajini don yanzu nima Allah ya bani abin fada mata ai kowa ya ji da nasa abin fade.
Kwana biyu Saade bata ko iya fito tsakar gida koda yaushe tana daki ranan mukaji Inna na mata fada wai ta fito ta kunkumay acikin daki.
Mai ciwo ma ta fito tana walawa sai ita zata tsiri zaman daki muna jin ta ummi tace anzo wurin .
Sai ko ummi tai wuf tafita waje tace may zaki fada min bayan Allah ya nuna maki bakin halin ki tun a nan duniya.
Ai ni gara tawa ansan gidan miji ta kwaso shi ke ko fa daba a ko san suwaye sukai mata kaca kaca ba a gari.
Baba yana jin sun fara ya fito tare da daka masu tsawa yace ke Rakiya yaushe ne zaki hankali yanzu duk wanan isharan da Allah ya gwada maki bai isheki ba sai kin tsaya jan magana.
Sai cewa Inna tayi Allah ne ya nufe ta da ganin haka a rayuwan ta kuma ba zai zama abin fade ba ai.
Yace ita ko itace ta saya da kudin ta ko ke in kina da kunya har zaki kawo irin wanan magana haka wanan abin bai isheki ba.
Ko tafiya nake na koma ana gwada ni a gari banda sukuni a cikin mutane gida kuma babu dadi.
Wanan karon bazan lamunce ki ba duk kika haddasa min fitina a gida zan dauki mata mumuna akan ki ne.
Jin abin daya ambata yasa tai sanyi don ta zaburo wa ummina sosai kamar zata cinye ta danya ya kara da fadin .
Ke wata irin mace ce wata ukun da aka bamu mu koma baiti ba har kin shiga goranta ma wata halin da take ciki ki bari a san makomar yar taki tukun san nan ki samu abin fadi.
Dama Inna bata son zancen komawa asibitin nan don ko yaushe tsinewa likitan takeyi akan yace su koma a sake auna ta.
Nan ta shiga cewa insha Allahu babu abinda zai faru da ita sai alheri na gane kaima so kake wani sheri ya faru da ita a gidan nan su zama daya da yar ka.
Tai ta sababi ba wanda ya sake kulata har tayi ta gaji ta koma dakin ta tana mai zuba mugun addua ga masu fyaden da masu zagin yar ta.

* *
Ranan ina waki tufafin mu da rana naji anyi sallama muryan dai ta wace na sani ne amma kuma may zai kawo ta nan.
Naji tana tambayan ina nan da sauri na dauraye hannuwa na fito daga inda nake wanki mama biyu ne tare da yan tagwayen ta.
Sun girma sun kara wanj irin kyau dasu da uwar su baki daya ban san lokacin da nai cikin suba da murna na sai fadi take alhamdullah.
Naji dasin yadda na samay ki alamu ya nuna min kina ahan maganin ki ke nan mun shiga dakin mu na rasa ina zan sakata.
Na fara gabatar ma mutanen gidan mu da ita suka shiga gaisawa da ita suna tambayaan ta yara da maigida nan na fito na aika a sayo masu fanta kwalba da ruwa mai sanyi.
Tace no ki barshi ashe garin naku yana da nisa haka ne yanzu zamu wuce dama nayi alkwarin zanzo na duba ki ne tunda ke kin yada mu.
A kunyace nace ban yada kuba anty yanayi dai ne yazo da hakan mun dan taba hira tamike tace zasu wuce don dare yayi yau zasu koma dama buki tazo yi arewa shine tace bari tazo ta gane ni.
Ina ta rawan jiki na rasa may zan basu tace huta abinki bashi ya kawo ni ba tunda nagan ki alhamdullahi.
Ta kawo kudi tace in bawa ummi na ga tsaraba mai yawa da ta kawo muna a cikin buhu ta fito tsakar gida taba su inna dubu ashirin su raba.
Takawo wani tace aba baba in ya dawo nafita na rakata bakin motar ta anan take cewa dani idan na samu lokaci indan leko wuein su ina kuka ta rungumay ni tana share min hawaye.
Nan dai suka tafi suka barni cike da kewar au gani nike abun kamar a mafalki wai anty ce a garin mu yau.
Mun koma naji inna na fadin tunda nike ban taba rike ko dubu biyar ba na kaina a rayuwana yau ga bakuwar arziki ta zo mun dashi.
Ban tsaya ba na shiga dakin mu na bude tsaraban da ta kawo min turmin zani guda uku da sauran tarkace ne a ciki nai murna sosai tare da yin hamdala.
Mun dade muna hiran ta ina fadawa ummi irin taimakon da tai tayi min acan lokacin da nake cikin bukatan aimin din.
Ummi tace Allah ya saka mata da alheri daga waje naji mama na fadin mukan ai Safiya kin jawo muna arziki har gida wannan abin arzikin da may yai kama.
Baba ya dawo gida ummi ta bashi kudi da akace a bashi din ya shiga murna da saka mata albarka.
Yana ta godiya yace haka Allah ke ikon sa yau na tashi tun shekaran jiya banda ko kobo a aljihun nan yazu ga kyauta na samu daga sama.
Kwana biyu ana facali a gidan mu kafin su kare nidai ina kallon su kawai ba kunya ba tsoron Allah a tare dasu.
Haka rayuwan yake gudana dan dama yanzu bakin Inna ya mutu ko tayi ma sai a bayan mu don da ta fadi ummi take mayar mata.
Sai dai indan wani abin can na kishi ya hadasu daban amma dai ba gori ba don yar ta na gida kamar mujiya da ta fita sai a kama nuna ta.
Wasu ma harda kari wurin bada labari zancen nata suke karawa don maganan yai dadin fada shiyasa Saaden bata son fita ko ina koda yaushe tana gida zaune.
Yaya Saadu yazo diba mu bayan kamar wata shida da tafiyan maman biyu shima yazo muna da abin arziki kamar yadda ya saba kawo muna idan zai zo.
Sai dai wanan karon da wata yazo yarece dai amma yace matar sa ce da ya aura ya kawo muna ita taga gida.
Baba yace ikon Allah kayi aure bamu sani ba a gurina matar tashi ta sauka don bata jin hausa munyi dan hira da ita kwanan su biyu damu sukai muna sallama suka koma.
Kafin ya tafi yake min maganan aure wani iri naji don bayi zaton zai min wanan maganan ba ya kula da kaduwan da nayi sai yace.
Safiya ki daure ki samu wani mai irin matsalar ki ki aura hakkuri zaki yi bawai don kina so ba sai dai don kare mutuncin ki.
Nai shiru na dago kaina idona na zubar da hawaye nace ni yanzu yaya ina zan samu miji a haka yadda nake kowa fa garin nan ya san zance na ba inda inna bata kaini ba .
Yace ai kinji abinda na fada mai irin matsalar ki zaki aura acan gurin ansan maganin zasu iya hada ki da wani mai wanan lalurar idan hakakin ki ya kwanta sai ki daure ki aure shi.
Hakkuri zaki yi da almarin kaddarane kuma yadda kikai tawakkali yana dakyau sosai haka ake son musulumi dayi.
Shima Ahmed yana can ciwon yakai shi kwance sosai sai da nazo ne na kaishi asibiti da yana gida kwance yana karyan wai sammu ne.
Nai dariya nace shida yace baida shi yaya akayi haka kuma yace kyale su don Allah wai saida muka je asibiti ya baiyana yanzu ne mummy ke fadin an cuce ki.
Da wani ido zata kalli baba dashi bayan duk wahalan da kika yi bata zo ta dubaki ba har yau yanzu dai suna can na barta dashi ban san yadda zasu karata ba nidai na kaishi asibiti yadan samu sauki yanzu yana nan gida.
Allah ya sauwa ka nace yace ko zaki hakkura ki koma mai kiyi hakkuri ku zauna hakana.
Nai saurin cewa Allah ya sauwa ka yaya ida bakai ka fada min haka ba yau da sai an raba mu amma kaine ban cewa komai.
Yai dariya yace Allah da zaki hakkura ki koma yanzu ai yayi nadaman abinda yai maki ya koma yana daya sani ita ma Lilliya naji ance an kwashe ta zuwa garin su okene.
Nace yaya don Allah mu bar hiran su kazo zamu rabu da dadin rai kuma kana son ka bata tsarin nace ai zan shigo lagos indan anyi daidai kana nan sai na karasa wurin ku naga mazaunin ku.
Yace yaushe kenan nace idan baba ya barni sabin wata nake son zuwa nake fada mai zuwan maman biyu da tace in dai je in mata kwana biyu yace idan zaki zo sai ki sanar dani tunda ga waya.
Nan suka kama hanya suka tafi ya barmu cike da kewar shi yaya Saadu mutum ne wanda yasan kan sa yasan hakkin zumunci.
Yanzu fa zuwa yayi ya kawo muna matar da ya aura wai taga garin su da yan uwan shi don tasan yana da asali.
Rayuwa yaci gaba muna a gidan dadi ba dadi haka muke hakkuri mu zauna a cikin sa anyi bukin yar wurin mama salin alin mun sha buki inna na kallo ita da tasha alwashin yar ta zatayi aure.
Sai gashi Allah yai nashi ikon a kan ta ba maganan aure gare ta sai in Allah ya kawo mijin nasan dai ba a karkaran mu ba kan don ba inda zancen ta bai kaiba har da makwabtan garin mu.
Dole muka koma fita tare da ita tun uwar na fada har ta gaji ta saka muna ido don yanzu haka muka koma kamar aminai da ita.
Sai dai ban yarda tasan sirina don su ba abin yarda bane ga mutane sherin su yawa gareshi don ta gado uwar ta da hassada sosai.
Idan wata ya zagayo sai in tafi amsan magani acan wani ya leke min wai shi sona yake yi har da zuwa gidan mu.
Ranan da ya fara zuwa kin fita nayi sai da yaya sani ya shigo na fita bayan wuce wanshi nace da yaya sani ni ban yarda da shi bane.
Don da ganin shi manemin mata ne sosai don tsarin shi ya tabbatar da hakan yana magana yana wani iri.
Niko yanzu ba zan yarda na koma wa wala ba bayan na fito gare shi yace ki dai kwantar da hankalin ki ki bishi sannu mu gani.
Ni dai a raina nasan abinda na yanke shawara a kai so nake baba ya yarde min in tafi wurin maman biyu sai ranan da suka gane ni.
Amma ban fadawa ko ummi na ba na bar zancen a raina don naga ko ita tayi aman na da zuwan mutumin wuri na su ala dole na samu mai sona da halin da nake ciki in dai yi aure ko yaya ne su nasu kawai kenan garesu.
Basu tunanen hali na gari ko wani irin rayuwa zan je kuma na tarar ga ciwo ga taulalin miji a kaina.
Shi yasa na yanke wa kaina shawaran barin gari salin alin batare da kowa yasan manufana ba a gidan.
Don in sun sani ba zasu yarda in yi nesa da suba ko kadan shiyasa na bar abin a raina ni kadai.
Sai in lokaci yayi su san manufana idan kuma basu gane ba a tafi a hakana duk inda nake sarin kaya a birni tare da kanina nake zuwa don ya iya ya saba dasu don ko na tafi bazai sha wani wahala ba ya iya.
Harkan kasuwan ci na tare dashi muke yi yasan kan komai da yadda muke aje uwar kudi mu fidda riba daban duk ya iya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button