BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/5/20, 11:23 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , ,

????????7️⃣1️⃣????

Uncle ya shigo dakin da muke wanda shine kamar mallakina a gidan shi na bauchi sai faman shiri baby khadija keyi acikin wani riga da wandon maza duk da kayan yara maza ba a faye samun wani sauyi a cikin su ba iya ka dai wando da rigace kawai kayan adon su.
Amma shi wanan din da uncle ya sawo yazo muna dashi yana da matukar kyau sosai don gaskiya ya hadu sosai.
Ina zaune gafenta ina waya da ummin mu da suka dawo bamu samu ganin su ba tana bani labarin taba inna tsaraba ta dawo mata dashi wai bata so saboda anyi rikici da ita anka yara tsakanin su.
Nace yanzu ummi ya kamata ace kin fahinci waye inna ita kullun gari ya waye tana neman wanda zata sauke masifan ta ne akan shi.
Ban karasa maganan ba iya abinda yajike nan shigowan shi sai na kara da fadin ta kyale ta kawai ta aje kayan indan ta sako daga fushin ai zata dawo ta karba ne.
Maganan da yakewa khadija dakewa yaro shiri tana fashi wasa yace zaki koya mai kiuya yazo bai san kowa ba sai ku ko?
Katse wayan nayi da ummin nace uncle fita zakayi ne yace eh daga can yana son ya samu halartan daurin auren gidan su miji Aisha din da zaayi.
Nake cewa zamu tafi dasu anty suwaiba idan sun zo yace yaji kawai nasan fitar ya zama mai dole ne kawai ya barni kudi ya fida yana miko min wraper din yan diri biyar biyar har biyu tare da fadin a watse lafiya.
Godiya nayi mai ya miko ma khadija dake zaune itama sai dai ban diba a lokacin balle in san ko nawa ne ya bata.
Yadan dauki Abba yana mai wasa tare da fadin kayan nan sun matukar karban ka babana nace anbinda khadija take fadi ke nan.
Ya aje yaron ya fara tafiya ya juyo yana ce min sai kuyi amfani da dayan motar don ni zan fita da dayan ne.
Makuli ya miko min tare da tambaya ko ya bar muna driver ne nace ai zan iya ja kada ya zauna a takure a cikin mata.
Murmushi yayi yasa kai ya fita mukai mashi adawo lafiya yace amin fitan shi khadija tahau murnan kudin da ta samu awurin shi ta shiga kirgawa cikin murna.
Nice na kawar mata da murnan da jefo mata maganan su ummi dake ci min rai tace ba dai ummi ta karbi kayan ba nace eh ra karba tunda har daki ta kai mata.
Tace ai shike nan mana inna fa sune basu san halinta ba har yanzu gurin ta shine kada ta ga wani yafi ko ta wullakanta mutum kan abinda bai kai ya kawo ba.
Muna cikin maganan su anty suwaiba ta shigo nan muka shiga gaida ita take fadi bamu shirya ba don mu samu waliman da za a yi .
Aisha tace ta bugo min waya ban dauka ba sai na tuna wayan na guda yana dakin uncle na barshi acan tunda safe ban dauko ba .
Nace ai wayan yana dakin uncle na barshi yana caji a can tace tana tambaya ko anbarki zuwa gidan nasu nace mata mun rabudake jiya akan zaku zo din ai.
Nace tasan halin dan uwanta shiyasa take ganin kamar ba zamu zo din ba tace ita fa so take muje mu cika mata daki lami tasan tana da yan uwa da yawa.
Aiko zata ga gaiyya yau don kowa zai tafi yar dariya nayi kawai nace ana dai zuba kishi a gidan su Aisha kan.
Tace ai yanzu haka ne ako ina kedai sai idan baka da kishiyace ka huta da wanan kwamacalan rayuwan.
Ba birni ba ba kauye ba duk abin daya ne wallahi nace lokacin muke da kishin fili akeyi bana boye ba irin na iyayyen mu da ya wuce.
Fita tayi da Abba a hannun ta tana jadda muna muyi mu shirya don Allah idan sauran sun iso sai su samay mu a can.
Nace yanzu anty gamunan fitowa wani buje da riga na saka dan dubai wanda tsayawa fadin shi bata lokaci ne sai gyalen su mai kyau ga taushi da sanshi yana lefewa ajikin mutum.
Takalma da jakka da suka dace da kayan jikina takalman mai tsones da hill sai daukan ido yake yi don kyau da har handbag din shi sai sarka da awarwaro dana zuba a jikina masu tsadan gaske.
Turare na shafe jikina da gyale na dashi itama khadija shigan ta na yan matan zamani ta yi don shigan yayi mata kyau sosai a jikinta.
Mun rufe part din na kai wa baaba makulin koda uncle zai shigo bamu nan khadija na rataye da dan jakkan da muka zuba kayan Abba a cikin sa maikyau dashi.
Muna shigowa kallo ya koma kan mu a falon na baaba inda yan uwa duk sun hadu bamu jima ba muka fito don tafiya don mutum uku ne basu iso ba a lokacin.
Hajiya baaba tace mutafi zasu samay mu acan haka yasa muka mike tafiya gidan su Aisha din gaba dayan mu dake falon.
Mun fito alokacin sauran sun iso aka tsaya don motacin su anty suwaiba dake wurin zamu tafi dasu a zaton su da tasu zamuyi amfani dukkan mu.
Nan nace da suwa zamu tafi a motar mu motar suka kalla gaba dayan su suna fadin au da taku motar zaku tafi ashe nace eh kawai.
Yan matan suka ce a tamu zasu tafi don haka na bude na shiga suma suka biyo mu a jera mota hudu muka nufi unguwar su Aisha din inda a tsohon uguwar su gidan yake.
Suke gaba muna bin su a baya har muka kai gidan dake can unguwan su tsoho wurin a cike yake da jamma, a maza da mata saman kujeru roba kungiya kungiya.
Duk sai kallo ya dawo gare mu a wurin wuri muka samu muka tsaya inda ba mutane da yawa mun fito muka kulle motocin mu.
A lokaci daya muke shiga gidan wanda da alama gidan yawa ne mai part aciki lungu lungu har muka isa wani wanda yafi yawa anan dakunan su Aisha din yake.
Kafin mu iso labari ya iso mata na mun iso duk mutanen sai kokarin kallon mu suke suna aiki Aishan ne ta ratso mutane tana muna sannu da zuwa inda bata bari mun shiga daki ba sai da takai mu wurin uwar mijin su a gidan.
Nan muka shiga dakin dattijuwar ta tare mu ba yabo ba fallasa a fuskan ta tare da tambayan hajiya baaba muke tana gaida su.
Har mun juya zamu tafi take cewa ance har da matar Sulaimana a ciki ko itace wanan yar farar ko tana nuna ni cikin su.
Aisha ne ta bata amsa da eh tace ai naga alama mukan muka fita zuwa dakin ta anan muka ga lami a kofar su suna hada zobo na buki.
Tunda ta dago ta kalle mu tayi muna sannu da zuwa ta dukar da kai kasa tare da ci gaba da abinda takeyi bata sake dogo kai ba har muka shishiga dakin Aisha din.
Wanda a falo muka zube mutanen dake cikin dakin kafin mu shigo suka firfito daga dakin a kujaran dake fuskantar waje na zauna don haka ina iya hango wanda ke waje suna gittaiya a inda nake zaune din.
Aisha tazo muna gaisawa da ita tama rasa da wanda zata gaisa a cikin mu a lokacin don mu goma sha biyar muka zo gida cika taron buki.
Nan ta juyo kaina tare da dafani tace madam kin kuru da kika zo da wanan mijin naki mai rowan matar shi wa mutane sai nayi masa yajin wata uku gidan shi ban leka ba.
Dariya nayi ina kamota nace aida kin ga nazo bikon ki har wata uku bakizo inda muke ba da zama bai ganin ba.
Tashi tayi tana dariya ta fita daga dakin mu kuma akaci gaba da hira irin na mata idan an hadu wanda gulman Lami aka dauko da uwargidan Aisha din.
Ido na zuba masu ina sauraren kalamin kowacen su a lokacin don har yanzu ba sabawa nayi dasu sosai ba shigowan Aishan daki anty suwaiba ke ce mata ashe lami tazo ne ?
Tace gashi ko jiya ina fadi cewa ta shigo tun shekaran jiya da kawayen ta suna nan sai feleke suke muna a gidan.
Ido na kurawa Lami din a inda nake zaune don ina iya hango su daga zaunen da nake din kafin wani lokaci ancika muna gaban mu da abinci kala kala na nau,in bukin da sukayi.
Nan aka baje ana ta faman ci ana raha kamar yadda mata suka saba idan aje buki sai anty suwaiba ne ta farga bani cin komai a wurin take tambayana.
Murmushi nayi ina fadin a koshe nake sai dai idan anjima din kila zanci maryam ta ce kin san fa su ba abinci suke ci mai yawa ba yan kaidan cin abinci ne kada suyi kiba.
Dariya nayi kawai tare da cewa kai anty maryam zolaya ne kuma haka Lami ne ta shigo dakin tana gaida mu sai raba ido take a kan mu tana raba ido da alama wani gulma sukayi a wajen tazo gani don hankalina na gare su da suke maganan a waje.
Nan dai ta juya tafita tabar dakin don ta gama ganin abinda tazo gani din a cikin mu naga ta koma tana magana da sauran abokan hiran nata.
Munkai awa daya da rabi aka fito don yin walima bamu fito da wuri ba don har an fara waliman munka fito wuri ta tanadar muna daga can baya inda matan da muka samu a wurin idanuwan su ya dawo a kan mu kamar ba walima akeyi ba.
Mun zauna muna sauraren walima hankali na wurin matar dake muna waazi akan aure inda wasu matan ke gulma suna dan leken mu lokaci lokaci.
Zuwan mu wurin ya hana Lami da kawayen ta shakat a lokacin don ji take kamar ta bada umurni a kore mu a gidan bukin don duk wani ahurin da ta shirya ma bukin don taso ta gwada ma kishiyoyin nata ta zarta su ne.
Amma sai taga cewa Aisha yanzu ta mata zara a ko wani fage duk da bata aiki itace mai aiki da uwar gidan su .
Bata san cewa uncle yanzu yanawa yan uwanshi ihisani ba duk wata da dan abinda ya ware ake basu suna samun na kashewa.
An tashi walima lafiya an raba snack’s da drinks a wurin da aka mika min da sauri yaran da mukazo tare dasu suka karba daga hannun mai rabawan.
Ciki muka koma inda wanan karon ban zauna a falo ba kuryan Aisha na shige nida maryam muka baje saman godon ta daya sha gyara nan wasu suka shigo sai firan yadawo kuryan dakin.
Muna ciki ne mijin ya shigo gaida mu har kurya inda nake yana fadin hajiya safiya ashe kun samu shigowa yana ta min godiya don ya dauka bukin ya kawo mu muma.
Yana fita yake tambayan abba nace yana nan falo wurin yan mata nan ya fice maryam tace dan iska mai ladanin shegu ai dole yazo gaida ke ya samu gurin tatsa yanzu yadda yake so.
Dariya nayi mata nace kaji min mata tatsar may yake yi kuma tace da ba gori suke hadewa suyiwa Aishan ba yanzu daya ga akwai ci shine babu kunya yake wani ashe kunzo ne ?
Aisha da ta shigo taji tana zagan mata miji tace wa ake zagi tace mijin ki mana da baida kunya nake zagi.
Tace wanan shigowan dayayi gaida ku yanzu sau yaja fitina a gidan nan gun matan shi da mahaifiyar shi in ba ai hankali ba.
Nace gaisawan kawai kuma muna gidan akai sallah mun yi sallah a dakin ta sai bayan mun idar aka shigo muna da abinci .
Jeloup yaji hadi sai tuwo da miyar taushe nace aban tuwon shi zan ci sai gashi an zubo min da yawa a plate nace wai anty kubara ina zan kai wanan abincin haka maryam tace abarshi muci tare.
Mun zaune akace mu fito wurin wanke amare nan kowa ta gyara muka fita dakin Abba ke ta kuka wanda nasan zafi ne ke damun shi.
Muna dakin sai da mukayi mashi wanka khadija ta saka mai wasu kaya muka fito inda ake wasan a fitar da amare a tsakiyan fili ana ta zuba masu kudi suna rawa a hankali.
Anty suwaiba tace muje muyi wa amaren liki take muna kwantancen kaunan su Ado din mijin Aisha din muka saka Aisha gaba muna binta a baya haka muka ratso tsakiyar filin nan kallo ya dawo gare mu .
Mun zuba mata kudi sosai inda yan matan bukin ta ke kwashewa suna zubawa a wani jakka.
Nan wuri ya dauki sowa da fitowan mu sai gulma mata keyi ni dai na fito na zauna a ida muka tashi don a tsawale nake gurin.
Abba khadija ta miko min tana fadin tana zuwa na karbi yaron da duk wahala ya jirkitar dashi a lokacin maryam ta dawo tana zama nake ce mata mu koma ciki in kwantar da yaron ta suri jakkan ta muka shiga ciki.
Mun dan jima zaune sai fa su anty suwaiba sun shigo na dan make murya nace anty gida tace yanzu nima maganan da nakeyi ke nan nasan baaba tana can tana fadan rashin dawowan mu akan lokaci.
Haka yasa muka mike don haramar komawa gida inda sai da aka nemo muna yan mata muna doso gida naga motan uncle a waje alaman yana gida ke nan.
A falon gidan da ban daka ana amfani dashi ba naga takalman maza wurin zube ba iyaka haka yasa nasan da mutane yake lokacin.
Muna shiga ina gaida baaba tambayan mukulin mu nayi ta miko min tana fadin mijin ki yazo yana fada wai may kuka tsaya yi tun da safe gidan mutane nace dama nasan sai yayi fada don mun dade.
Nan na fita zuwa part din mu na barsu nan muna shiga na shiga cire tufafin dake jikina don wanka nake son yi sai dai ban shiga ba na tsaya tube Abba da har yanzu fita yake yi fanka na dan sake mai da ac sai yayi shiru ina fitowa na kashe fanka na bar mai ac din.
Zaune nake kafin magariba yayi nasa wani dogon riga na shan iska a jikina sai gashi ya turo kofan khadija na kwance da Abba saman kirjin ta tana dan buga bayan shi a hankali.
Kallo daya nayi mai na hango fitina a kwayan idon shi gaishe shi muke da kyat ya amsa ma khadija yace sai yanzu kuka dawo ?
Zan yi magana ya tare nan ya haufada har yagaji ya fita sai bayan ya fitane khadija ke fadin ashe haka yake da fada ?
Nace kadan ma kika gani don ya ganki ne baiyi fada sosai ba kuma bai son abashi hakkuri shiyasa kikaji na kyale shi ai.
Mun idar da sallah muna zaune muna hiran bukin ne maryam ta shigo muna da ledojin bukin a hannun ta na juya gun khadija ina tambayan zataci ne tace a koshe take gaskiya nace maryam kije dashi ku kara ko kin barshi nan ba ci za muyi ba.
Tana fita sai gashi an shigo muna da abinci na karba na aje saman dining table din dake part din nace mun gode kafin ya shigo na gyara wurin ya shigo har yanzu fadan nan a fuskan shi.
Don haka ban wani zure mashi ba don sanin hali da nayi raban dai haka muka kwanta yana hasale dani a ranshi washe gari na fahinci Abba baijin dadin jikin shi ne don da dare koka yayi tayi sai da khadija ta tadani na bashi magani ya sha nakoma dashi dakin uncle muka kwata dashi can.
Ranan kan nasha fada sai da nakai ga yin magana nace uncle a cikin taro mukaje fa kana ganin zan dawo na barsu can ne ni kadai na dawo gida ?
Ya dauki yaron yafita dashi sun dauki lokaci basu dawo ba sai can gashi da magani a leda yace a bashi yasha idan ya falka daga barci.
Tunda naje gaida baaba da safe ban koma part din ba ina cikin barci naji muryan ta a wurin mu tazo duba jikin Abban tace uban shi yana ta fada wai kun kwaso mai zazzabi a gidan buki.
Murmushi nayi nace haka yace min har yana fadin wai zamu koma abuja idan banyi hankali ba.
Murmushi tayi tace kyale shi kinji haka dai ya fada nace mai ya taba ganin yaron da aka haifa bayi ciwo ba ai da shima baijin dadi hakan don ranan da zai yi ba za ayi mai kyau ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button