BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , ,

????????4️⃣2️⃣????????

YAN UWA MUSULUMAI INA MAKU BARKA DA SALLAH DA FATAN ALLAH YA KARBA MUNA IBADUN MU YASA MUNA CIKIN YANTATTUN SHI ALLAH YA MAI MAITA MUNA WANAN RANAN MAI TARIN ALBAKA A RAYUWAN MU ALLAHU MA AMIN????

Kai na dukar kasa yake cewa ai da kin sanar damu zuwan su ba sai a san shirin da za ai masu ba yanzu gashi sun zo babu komai sai dan waken da uwar ki tayi aka basu.
Nace baba ai sunci sosai sun gode yace kayya ai ina da yan kaji da su aka yanka masu amma dai na fada mashi wani zuwan ya sanar damu ida zai zo.
Safiya ina kika hadu da wanan mutumin ne bafa karamin mutum bane da ganin sa ma ba sai an fadawa mutum ba.
Na dukar da kai kasa a hankali nace baba kanin mijin maman biyu ne da nake wurin ta a can lagos.
Sai yai dan shiru sai kuma yace yasan da matsalan da kike ciki kuwa don kar ai abu a duhu a cutawa dan mutane rayuwan shi irin da sukai maki.
Kaina a duke kasa nace baba ya sani don shima matsalar mu daya dashi shiyasa anty ta hada ni dashi da sauri yace subbahanallahi.
Yanzu shima yana dauke da wanan lalurar a jikin shi nace baba yana da shi yace subbahanallahi nace shima aure yayi ashe matar nadashi ba su sani ba saida ta shigo aka sani.
Yace waiyazu billahi kai mutane basu da imani a rayuwan su mutum kamar wanan amma an cuce shi an hada shi da may ye sunan ciwon ma nace tsida don ya gane.
Yace Allah ya baku lafiya nace amin baba yana ta jijiga kanshi alaman jimamay a ran shi yace yazo da bukata auren ki nayi duk wasu kwana kwana amma yace ayi hakkuri a bashi ke yasan matsalar ashe abinda yake nufi kenan dama.
To nadai bashi baki yace zaizo da magabatan shi a tsayar da rana don bai son abin yayi nisa sosai don haka zamu iya ganin su kowani lokaci.
Nace to baba yakara dacewa Allah yasa muce gwama da akayi a raina na amsa mai da amin a fili kuma shiru nayi mashi yace
Ai na tambaya aka ce kunje gidan gwago ne nasan fitinar inna kuce yasa ki barin gida kada kije ko ina don ta nan gidan kune gidan ubanki.
Sai dai ita ta fita ta har maki gidan amma bake ba nace a a baba ai inna uwatace don haka inda sabo na saba da fadan ta akaina bani daya kowa ma bata bari ba.
Mun dade da baba muna magana akai sai yaya Nura ya kirani daga dakin baba na amsa baba ke cewa mai yake sone sai nayi dariya kawai nace baba barin ganshi yanzu in dawo yace jeki ma ki huta ai kina da gajiya a jikin ki Allah dai tai maki albarka yasa ku gama da duniya lafiya.
Na amsa amin baba na tashi na fice daga dakin zuwa wurin yaya nura nan na samay shi a dan gaba da kofan baba yana jirana.
Ina fitowa ya miko min hannu yace bani nawa duk gidan a jike suke sai ni da bana nan nace muje daki yaya biyo ni yayi zuwa dakin ummi ya tsaya daga kofa na shiga na dauko mai kudin.
Ina bashi ya washe baki yana cewa sai kin zama matar gwauna da yardan Allah sai mun je shan jar miya gidan ki.
Inna dake duke tana talgin abincin dare na semon da akazo muna dashi ta kasa kannewa da kirarin da yake min tace kuke nan da baku san ciwon kan ku ba kai da dan uwan ka.
Ku baku ko kishin zucin kanku kuyi ma kanku fada ka tsaya kanayiwa mace kirarin da yakamata aima maza.
Yace kai ina haba ai kema kin sa fadi kikayi ina mu ina kama kafan safiya ai ita tariga ta take ko sai dai bi yanzu ko mutum bai so.
Sakarai kawai Allah waddai naka ya lalace mama ta katse da da cewa a a fa ai gaskiya ya fada ke da aka baki baki karba har fa dubu hamsin aka aje maki yau a gidan nan.
Duk zaman ki a rayuwa kin taba rike dubu biyar na kanki na kan ki aiko kamar azuba mata fetur nan ta hau sai da baba ya fito duk da halin da yake ciki har yana sarkewa .
Take nasa masu kuruwa ina cewa dan Allah inna ku bari kada ku kashe muna uba da fitinan ku Saadatu ma ta saka ihu take muka sa mata kuka muna kama baba dake ta tari aiko gida ya rude da kuka yara na cewa wayyo baban mu.
Mutanen waje suka shigo gida ya cika ana tambayan may nene muke cewa babane nan maza suka kama shi zuwa daki .
Inna jikin ta yai sanyi ta koma ta rakube sai ga yaya sani da yaya nura aka ce dasu ga abinda ya faru aiko ya fito yana cewa uwar in kin kashe shi sai ki huta na tabbatar ciwon baba na da halaka dake inna.
Amma ke kulun baki saduda maimakon ki rage sai ma kara baiyana halin ki kike yi nan dai maza suka taru a kanta sukai mata tas suka fice daga gidan.
Muka taru a dakin baba kowa yayi jugun jugun baba yace idan inna ta kara kulani a gidan nan sai ya saketa.
Wanan fitinan shi yasa inna laushi sosai ta koma shiru shiru a gidan kowa ya fita batun ta bayan kwana biyu na samu saadatu a dakin su.
Tana gani na ta zauna nace ya kamata ki rage wanan zaman haka kidan rika motsa jikin ki zai fi kullun kina daki kumshe murmushi kawai tai min.
Na miko mata kudi ta karba tana cewa na may ye nace ki rike a wurin ki ki dan sai kayan baby da abin bukatan ki.
Ta fara hawaye tace Safiya halin ki na alheri ne a gare mu ko yaushe abin ki bai taba rufe maki ido ba wanan kaddaran da ya samay ni nayi kuka a zuciya na nayi a fili.
Da kina nan da haka bai samay ni ba don kudin mai man gyadan da nake daukowa a wurin shi in na sayar in kai mashi kudi sai kudin ya kare a kaina.
Kin san kudi in ana tabasu ba a kari yadda suke sai kudin ya rushe a hannu na shi kuma ya matsa min shine daga baya daya ga banda kudin ya nemi da in bashi hadin kai sai ya yafe min kudin.
Shine na diga zuwa yana amfani dani ya mayar dani kamar wata matar shi sai da cikin nan ya samu ne ya guje gare ni tare da fadin shi ba zai karbi cikin ba.
Safiya nasan inda ki na nan haka ba zai samay ni ba don zaki san hanyan da muka biya shi kudin shi ita kuma inna uwace a baki bata damu da damuwar yar ta ba.
Sai dai in kawo mata tayi bushasha shine da ya daina bani ki ka ga muna yawan samun matsalan nan da ita.
Na share hawayen da ke fuskana nace kiyi hakkuri kin san duk mai rai nada nashi kaddara a rayuwan shi.
Na fito ina hawaye dakin ranan na kasa barci ina tunanen matsalan saadatu ina neman mafita a kai.
Karshe dai na samu hanya mafi sauki na da haka na kwanta washe gari muka tashi kamar kullun a gidan kowa na ta har kokin gaban shi.
Na fita waje acan daban su yaya Sani na samay shi nan na kirashi shi da amin shi na kut da kut na kirasu gefe muka kebe dasu.
Nan na fara jero masu bukata na suna saurare na karshe dai yaya Sani ya nuna baruwan shi ga maganan sai da abokin ya kwantar mashi da hankali ya yarda.
Akan zasu je su samu mutumin nan da yai mata ciki aji hadin ta dashi sai dai zasu biya wirin kanin mahaifin mu don a samu wani babba ya tsaya muna ga maganan.
Sun yarda da hakan na shiga gida suka wuce wurin dan uwan baba sun mai bayani sai yace wanan maganan fa maganan kudi ne.
Abokin yaya sani yace adai tun kare shi aji don aiwa abinda zata haifa din gata baba baiki ta nasu ba ya tashi suka samay shi a shagon shi na kasuwa ya na tsaka da kasuwancin shi.
Sun kira shigefe da suka fito mai da maganan sai cewa yayi shi sam bai san maganan ba suka ce to za a zauna gaban hukuma.
Sai cewa yayi aje mana abu na kudi haka suka dawo da labari babu dadi daga gare su bayan sun gama magana nace haka yace suka ce eh.
Nace a hadu din babu komai nasan dai dan kudin da suke hannuna suna isana kashe maganan kauye.
Don haka washe gari muka maka shi kotu tare da ganin mai shari a saadatun tai mashi bayanin komai da zamu tafi na kawo hamsi na bashi nace ga goro.
Haba abin nema ya samu aiko take ya aika yana neman shi washe gari za a zauna kotu bai ji wani tsoro ba don yasan dubu ashirin na raba su da alkali.
Ya rigamu isa kotun don yaga alkali nan ya cin na mai dubu ashirin din ya karbe da farko sulhu ya kiramu yi don dani aka je amma nace ban san hakaba nan na dan turza har ina cewa idan sharian baiyi anan zamu tafi abuja.
Kajini fa sai alkalin ya rude nace idan mun tafi can ai akwai awon da za a yi a tabbatar idan na shi ne koba nashi ba.
Sai ga Isah mai mangyada na share gumi a fuskan shi yana cewa ai maganan bai kai can ba ciki dai nawane amma kuma ai ba wurina kadai take zuwa ba.
Saadatu tai saurin rantsewa akan bata taba zuwa wurin wani ba in ba shi ba nace tun da bai yarda ba abari kawai aje birni a hadu a can .
Daga alkali har mutumin suka fara cewa haba ki kwantar da hankali abi maganan sannu a hankali a fahinci juna.
Kowan su na gudun zuwa gaba don ba zasu ji dadi ba sai suka ce mu fito waje suyi shara muka fito wajen muka basu wuri.
Kiran abikin yaya Sani sukayi suna tambayan shi wai yanzu may na zama ne sun ga na waye da yawa idona ya bude sai yace masu kai yanzu fa ta wuce sanin ku.
Don wani hamshaki daga Abuja ne yazo neman auren ta sukace gaskiya kan na ganta haka idon ta ya bude da yawa.
Sun fito suka kiramu ankan ya yarda zai karbi cikin nace ita fa to sai ya fara shafan gumi alkali dai ya tillasta mai akan idan ta haihu za a daura masu aure.
Muka samu madafa akan ta sai da naji ta sauke wani ajiyan zuciya don a kusa da ita muke da muka fito yana yi min magana ban tsaya ba.
Muka dawo gida sai da dare na muka samu baba ni da yaya Sani mukai mashi bayani halin da ake ciki kan Saadatu din.
Bai iya magana ba sai hawayen da yake yi kawai muna bashi hakkuri har ya daina mun fita ne ya kira su mama gaba dayan su yana masu bayani abinda muka zo mashi dashi.
Nan inna ta tsaya tai tagumi ta rasa abinda zata ce sai kuka aka bata hakkuri haka dai suka watse ni har na kwanta sai ga inna dakin mu.
Ina ganin ta na mike zaune don ban san da may tazo ba wuri ta samu takai zaune sannan ta soma maga Safiya wurin ki nazo nace to inna gabana yana faduwa.
Ban san abinda zance maki ba ga kokarin da kikayi ga yar uwar ki indan bake ba da haka zama zauna da wanan bakin cikin a rayuwan mu.
Don Allah kuyi ta hakkuri damu karkubi ta namu kishin mu ba karewa zaiyi ba sai ranan da muka kare nai murmushi nace inna kudai yi hakkuri da junan ku.
Ummina tana zaune batace muna komai ba har inna ta fita tace munafuka kamar da gaske nayau ne kawai baikai ciki ba don bata san kuya ba har zatazo wai wani godiya.
Nace kai ummi baku dai barin halin ku wanda kukeyi a kan shi ma yana fama da kan shi bai son fitina wallahi.
Ummi tace tadai bari ita da ta dauki duniya da fadi yar bakin cikin mata kawai na kwanta ina mata dariya nace kishin ku dai bai karewa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button