BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON

????????5️⃣3️⃣????????

NOVEL DINA NA KUDI IDAN KIN FITAR MIN ALLAH YABI MIN HAKKINA A KAN KI IDAN KI KARATA BAKI BIYA BA BAN YAFE BA NA FADA NA SAKE FADA A KIYAYYE DON ALLAH DON CIN AMANA BALA,I NE, , , , ,

Shigana daki yayi daidai da shigowan wayan Faiza nayi saurin dauka don nasa magana ya samu ke nan ina dauka tace wai safiya may ya faru ne daga jiya zuwa safe dai surfa maki zaki ake a gidan nan babu kakautawa.
Tace bari dai zan kiraki ina zuwa sai ta kashe wayan nata na bi wayan da kallo kamar shine faiza na bashi amsa da cewa sunji zancen auren ke nan.
Shigowan gwagom Ummi na gidan ne ya dawo da kowa a cikin sai tin shi don ta shigo gidan ne da gudan ta tana fadin ayyurriri amarya Allah ya kawo mu lokaci ya kawo mu yan bakin ciki kunji kunya masu hassada kubi bango ku narke don Saifiya da Sulaiman zama daram.
Su yaya Nura ne ke fadin gwagon ummi gudan bai isa ba sai ta kara fadin ayyurriri Amarya.
Yar shagali yar biyan bukata yar galari , makulin mota ke akaba na kofan daki ke akaba sai yaya Sani ya manna mata kudi a goshi nan ta kasa karasa kirarin nata ta saike guda tana fadin Amarya bakya laifi, ina amaryan take ne.
Sai mama tace a a gwago karkizo ki sa min yarinya kuka fa munyi arziki tunda aka daura aure bata wani bata rai ba.
Gwagon ummi ta juya ta kalli mama tace kuka kuka fa kikace
Yo kukan may ina so kina so sukayi fa kinji ki da wani zancen badai yaran yanzu kuka kan.
Aiko na munafunci basa yi koda kuwa budurwace sun daina kuka tace yo Allah na tuba wanan din ma ai tayi kawaici da watace da yanzu ta kafa muna DJ a gida ta ruda unguwa da gaiyatan shedanu masu hana auren zaman lafiya.
Ummi ce ta fito fuska a daure tana yiwa gwagon sannu da zuwa ta bi yar dan uwan nata da kallo tana amsa gaisuwa nan tabar mama da sauran yara tsaye ta nufi dakin umin nawa.
Kara gaisawa sukayi ta kasa daurewa tana tambayanta make faruwa ne naga ranan farin ciki a gare ki gashi kuma kin bi fuskan ki duk kin daure ?
Ummi bata iya yin magana ba sai hawayen dake zubo mata sai nice nayi karfin halin fito ina cewa gwago an shigo tace a a kina ciki dama ?
Nace na kwanta ne dama tace may ya samu uwar taki ne haka kuma ranan farin ciki a gare ta gata tana kuka kuma ?
Nace ba wani ubu bane zancen Inna ne dai shine takema bacin rai ,
Innan taku tayi wani abune mara kyau ne kuma nace gwago takan rasa ne ai mai hali baya barin halin shi.
Zuwa tayi ta fadama ma dagin mijin antyn mu wai suyi bincike anty mu na da cuta a jikin ta amai rufarufa ne don acuce shi.
Salati gwagon ta saka tun kafin taji karshen maganan tana fadin amma dai anyi yar banza mata anan .
Da ita nufinta haka za a hada auren bai san halin da take ciki ba to mu bamu da gadon sheri a tare damu.
Yanzu may ake ciki tana sake tambayan Aisha kauna na don ta san ni da ummi ba zata gane komai a wurin mu.
Aishan tayi mata bayanin komai yadda zata fahinta tace hakan da malam din yayi yana da kyau tunda dai Rakiya bata da niyar gyaran halinta.
Nace ni gwago na rasa mai nayi wa inna a duniya tun ina karama bata kauna na haka.
Tace bazata ko kaunace ki ba don indan kika ga mutum da yafaye wanan halin yaje bakar bincike binciken ta an fada mata abinda ya tayar mata da hankali shi ne abin yake wahal da ita haka.
Kin san wasu basu da dogaro gun Allah da zaran kishiyar su ta samu ciki zasu je a bincika masu mai zata haifa da sauri nace kai haba gwago tace Allah sarki ai wanan abin abu ne da ya kewaye birni da kauye don ko ina akwai marasa imani.
To duk yadda akayi irin haka ne ke damun Rakiya taje an mata buncike an fada kata cewa abinda zaki haifa na da arziki sai ta ce a jefo mao kaddara da karshe kuma ba mai iya hana ikon Allah sai kaddaran ya juye Alheri ga bawa.
Shiru mukayi muna sauraren gwago da al,ajabin abinda take fada muna tace don yanzu an daina wasu abu saboda wayewan kai da mutane suka samu.
Amma har gobe a kwai masuyin zagon kasa don su basu bar gida ba don haka yake da kyau mutum ya nema wa kansa rigakafi tun kan rana ya baci.
Don haka kema yanzu ki saurare ni don zaki tafi cikin bakin fuska da baki san su ba baki san halin su ba .
Don haka zan baki makarin kwarce ko wani zai maki ba zai kamaki ba murshi nayi a raina nace kai gwago ho.
Zaki samu kwai na zabo guda ukku sai ki samu kayan aduwa 99 a hada su da kwanzaben nan a dafa sai ki hada bawan kwan da kayan aduwa a dakesu adinga zubawa a kunu anasha.
Maganin walwale turbuda shine turbuda kuma idan kina zargin wani na maki asiri shine,
Zaki samu ruwan tsami ko ruwan tsami da ganyen zogala wanda aka shuka iyankan gona sai ki jika da kai kayi koma kan mashekiya ki hada da ruwan tsamin da zogalan na iyakar gona kiyi wanka ki sha.
Da yardan Allah komai mutum ya dauko a kanki sai dai ya koma mai badai ya kamaki ba.
Wayana yai kara sai na mike na koma daki na bar gwagon nan falo zaune da ummi da su Aisha.
Na dauko wayan da sauri gabana ya fadi don ganin lambar anty na kira na a lokacin wada dama ina tsamanin hakan ko yaushe.
Na dauka da sallama ta, sai naji ta katseni da cewa amarya ke nan ke nan kai duniya ina zaki damu ashe tsintaciyar mage dai bata taba zama mage.
Lalai mutane sunyi gaskiya da suke fada min cewa ke din tsintaciyar mage ce a gare tabbas ko ya tabbata hakane.
Kafin in magana sai naji ta kashe wayan ta dip ajiyan zuciya na sauke tare da sake murmushin bakin ciki lokaci guda.
Na a sanyaye na fito falo inda suke na zauna ban iya cewa na fahinci hiran su alokacin sai da naji tace ai kinga idan yaro ya na dauke dauke zaki samu kaucin malge a samu kashin mai satan a hada da malgen a shaya in ya bushe a daka in ya zama gari sai a dinga sa ma mai shi a kunu ko shayi yana sha har kwana bakwai da yar da Allah zai bar satan don da yaje daukan abu warin kashin shi dayaci zai hana shi daukan abu yaji satan ya fice mashi a rai.
Sai kuma mallaka da sai abinda kika ce a gidan zaki samu kaucen gwanda na daji ki dake shi ya zama gari a samun kan tunkiya da ta kosa adafa su tare in ya dahu sosai ki zauna kici duka amma bada kashin ba.
Allah sa mu dace naji tace sai lokacin na kallo ta ina cewa ummi yanzu anty ta kirani fa.
Da sauri tace yaya kukayi da ita ta sake fadin taji ke nan dai ko ?
Na gyada mata kai da alaman eh gwago ne tace may taji auren sai ummi tace eh gwago tace dama bata sani bane Aisha dake zaune ummi ta kalla sai tayi shiru.
Na ce ummi ai yanzu ba maganan boyo bane tunda abin na ta kamari tace wai may ke faruwa ne kumbar mu a duhu haka ?
Ummi tace ummi kin san sun samu matsala da uwar rikon nata tace subbahanallahi shine baku fada muna ba asan abin yi.
Ummi tace abin ne wallahi da daure kai zaman su ba wani matsala sai daga baya ne kuma wani hali ya shigo masu.
Don ita bayan ta hada su da kanin mijin ta sai kuma daga baya bata son hadin wai tana son hada shi da wata yar yar uwar mai gidan ta.
Shine ita ta risketa tana waya suna fadin wai zasu zo suyi kata korar kare a gidan da take zaune shine shi wanda ta aura din ya bata shawaran ta dawo gida.
To shine da nake fada ma malam halin da suke ciki sai malam din ya yanke shawaran cewa da sun zo tambaya sai a daura aure da yani.
To yanzu nasan taji ne shine wai ta kirata yanzu din sai gwago tace may tace dake to ?
Nakwashe abinda ta fada min na fada mata sai tace aikin banza ai Allah ya riga yayi ikon shi ko a kan su yanzu sai dai hakkuri.
Nace ni yanzu ce min da tayi wai tsintarciyar mage bata zama mage shine abin ke damu na wallahi tana ganin nice na yaudare ta ko may gwago ?
Tace kun ga yanzu duk ba wanan ne a gaban mu ba koma may ye idan kin tare daga baya sai ki nemi shiri da ita da sannu zata fahinci ke ba tsintaciyar mage ba sai ta soki fiye da magen da aka haifar mata a gida.
Ummi tace shine kan mafita gwago don yanzu duk yadda za a fahintar da ita ta riga ta hau ba ta yarda damu ko kadan.
Gwago tace may ake ciki ne don shi ya kawo ni yau din don nasan baku shirya komai ba ga auren nan gashi kuma ba kananan mutane bane su.
Ummi tace wallahi gwago abinda muke shawara ke nan akai tun jiya da malam ya daura wanan aure don nasan ba komai zamu samu a bangaren shi ba.
Gwago tace karki yanke hukunci da sauri don baki san ajiyan shi ba nace humm gwago ai abar zancen baba kawai don yanzu baida yaushe ne ya fara fita kasuwa.
Nace akwai wasu kudi a hannu na barin dauko sai a kaima su mama asan shawaran da za a yi dasu na mike sai gwago tace dawo ki zauna zasu yanzu don na fada masu mu hadu nan ban san abin da ya tsayar dasu ba.
Sallaman su mukaji a tare suka shigo suka tsaya suna gaisawa da mama dake zaune a kofan ta tana raba abinci.
Suna shigowa suka fara gaisawa nima gaida dsu nayi da zuwa sukace amarya ke ce haka ba wani shiri da zai nuna farin ciki a gare ki?
Murmushi nayi nace kai haba mama tace ai gaskiya ne Safiya tun yanzu fa za a fara shirya ki don wanan auren ba irin wancan bane.
Tace to ai kune uwayen nata kuka tsaya nawa na fada maku mu hadu nan tun da safe amma sai yanzu kuka zo.
Yanzu dai ba wanan ba yanzu shafiu ke fada muna abin da bakar daga can tayi jiya kuma asirin ta ya tonu.
Gwago tace don Allah ku fita batun ta kuyi abinda ya kawo yanzu don ba isasshe lokaci ake dashi don tace yace a sati biyi yake son ta tare gidan shi.
Suna hada bakin wurin fadin sati biyu fa ?
Yo mai za a tsaya jira kuma aure ya dauro ba sai ta tare gidan ta ba yanzu duk wani abinda za ayi ai aladane kawai don wajibi ya auku ko tunda an daura aure may ya rage kuma ?
To yanzu gwago maye abin yi tace yanzu take fada muna akwai kudi a wirin ta sai a san abin yi nace ta bari har ku iso ne muga kudin sai a san yadda za a kasafa su.
Mikewa nayi na shiga daki tare da kirgo kudi dubu dari uku na kawo masu na mika ma mama Jummai don itace babba a cikin su.
Tana kallon kudin tace ai ina ga a dai tallakance wanan din zai isa ko sun kai dari biyu ai nake gani nace dari uku ne nan tace tirkasa.
Ta juya gun su ummi tana cewa may ye abin yi yanzu ga dai kudi sun samu gwago ta katse su da fadin akwai raguna na sai a kama biyu ku hada a laurar taku.
Nace gwago baki barin abinki tace ai don haka dama nake kiyon su yanzu ba sai ai lalura dasu ba sai dai zanso ku soya masu shi ku jefa a gara kun dai ga gidan masu shi zaku kai kayan.
Zan so ace kun tsaya kunyi abinda zai cika ido yadda ba za a raina maku ba.
Mama Suwaiba tace mu dai yi iya karfin mu amma ina zamu ita dasu nace mama may zai hana ku kira mama na nan gidan kada a kebe ta zaifi ace anyi komai da ita.
Gwago tace yanzu abin da nake shirin fadi ke nan kika riga ni fada sai ummi tace gaskiya kan kiranta aka tura Aisha da ta make dakin tana sauraren mu akayi .
Bata dauki lokaci ba sai gata nan dai akai mata bayanin ta nisa tace da son samu ne kada muyi kayan abinci mu dai tsaya ga wanda za a rabawa yan uwa da abikan arziki don shine abi magana.
Alabashi gaba in ta haihu sai ai mata wanan ko yaya kuka gani ta dago kai tana kallon su ko wayace sharan ta yayi.
Na suka fara kitasta abinda zasu inda za a kai yin cicin din a birni can wajen kaunan miji mama jummai dake zaune a birni su kuma zasu yi sauran abubuwan a nan .
Kowa ya dauki part din abinda zai yi a cikin su inda aka bar wa mama da ummi yin suyan kaji da ake so cika roba guda dashi.
Tun wanan ranan basu zauna ba kowa da abin da yakeyi don kar a girshe shi muna waya dashi ko wani rana yana kara kwantar min da hankali.
Faiza ne ke fada min cewa su anty uwa sun koma abuja a fusace wai Nafisa tana ta kuka tana fadin ba zata yarda ba.
Ita sai ta auri uncle ko ta halin kaka wai da kyat ta yarda ta bisu ta kare da cewa wai yanzu ashe an daura auren ku da uncle baki fada mu na ba sai a bakin mutane mukaji.
Nace wallahi Faiza nima ban san za a daura min aure ba a wanan lokacin kawai daga zuwa tambaya sai gashi ance daurin aure za ayi.
Tace ai dake da madam din mu ne yanzu don naji tana ta zage zage tana ta fada daga ke har uncle din wai kun munafunce ta.
Nayi murmushi kawai nace ba haka bane wallahi kowa baba bai fada wa zancen daurin auren nan ba sai da akazo yi aka sani wallahi ki yarda dani Faiza tace wallahi na yarda.
Tace yanzu yaushe ne tarewa kuma ?
Nace da ita babu rana Faiza don bamu tsaraba sai ya dawo zai saka rana tace aini abin yayi min dadi wallahi sai dai nasan yadda madam ta hau ba zata barmu mu zo wurin bukin ba.
Kin san may nace a a Faiza tace naji suna magana wai ai gidan ku ba abinda zasu kai tin anan zaiji kunya ita ko mutumiyar kullun tana daki tana kuka wai bata da lafiya.
Allah ya kyauta nace da ita ban yarda na furta wani kalma da zata kaini gaba ba don sanin halinta da nayi.
Mun gama wayan ta barni cike da tunane halin da muke ciki da anty don da ka gan ni na ramay babu walwala a tare da ni kamar wacce za ayiwa auren dole na koma.
Nasan dawowan shi Nigeria sai da ya kwana biyu ya wuce bauchi wurin mahaifiyar shi don kiran gagawa da tayi mashi akan maganan mu.
Ya iso sai dai mutane basu bari ya samu kebewa da ita ba sai da dare suka samu ganawa da mahaifiyar tashi.
Yana zaune kasa tana saman kujera ta kafa mudubin ido a fuskan ta da ke taimaka mata vurin gani.
Shiru dakin yayi kafin tace babana wata irin mace ka dauko muna don ban ji dadin labarin da ya kawo min ba.
Ko da yake mutanen duk da bamasu karfi bane amma sun san mutuncin kan su a yadda mahaifin yarinyar bai karbi sadaki mai yawa ba kuma da irin taron da sukai ma wayanda na tura daga nan.
Sun yaba kwarai da mutuncin da aka nuna masu a gidan sai da abin damuwa wanan labarin da Nafiu yazo min dashi shine banji dadin shi ba.
Nafi son kayi bincike mai karfi kafin yarinyar nan ta tare don ni ban kita ba don kaine mai zama da ita amma tunda kananan magana ya fara fitowa daga gare su sai a tsaya a bincika a hankali kada azo ai abu a cikin duhu.
Ban son ka kara auren dana sani kamar yadda kayi a baya auren da baida amfani a gare mu sai barnan suna.
Shiru yayi kafin ya dago kai yace hajiya akwai abin da nake boye maki da dadewa wanda baki sani ba har yau.
Gyara zaman tabarau ta tati dakyau ta dago kai tana sauraren shi tare da fadin baba na maye kake boye min wanda ban sani akan ka.
Ashe akwai abinda zaka iya boye min wanda ya shafi rayuwanka yace hajiya kiyi hakkuri don Allah fada maki wanan zancen tashin hankali ne a gare ki.
Nan dai ya fara bata labari tun auren shi da Samira matar shi ta farkko sai innalillahi kawai take furtawa har yakai yadda anty ta hada ni dashi dakuma yanzu da take shirin ruguza auren namu.
Innalillahi take ambata tace yanzu shi Nuhu da matar shi sun san maganan ga suka iya boye maka sirin ka ta yadda ko ni da na haife ka ban sani ba.
To amma ita maimuna may zai sa tayi haka bayan ta hada alheri kuma ta bata rawanta da tsalle a karshe.
Yanzu na gamsu da kai sannan ita wanan yarinyar itane rufin asirin ka ga kowa ta yadda ba kowa zai san abinda kake ciki ba.
Allah ya albarkaci aure ya baku zuria mai albarka ya amsa da amin tare da mata godiya ta kara kwantar mashi da hankaki tayi tare da cewa tasan yadda zata kashe maganan daga bakin kowa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button