BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM – Ummi Tandama: BAHAGON, , , , , , , ,

????????3️⃣ ????????

FREE PAGE, , ,

SEENABU MAKAWA, , ,

NA ROKE KI DAN ALLAH DON SON MANZON RAHAMA IDAN DA ZUCIYA BIYU ZAKI SHIGO GROUP DIN KADA KI SHIGA DON ALLAH DON BAZAN YAFE MAKI BA WANDA KIKA TURAWA HAKKIN YANA AKAN KI YAR UWA DON ALLAH KI HAKKURI DA DAUKAN HAKKI AKAN NOVEL DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE KIN SANI BA PUBLISH NOVEL BANE DA KI KE FADI KIN BIYA NE DON ALLAH MU SAHIRCE WA JUNA AKAN HAKA YAR UWA KAN ABINDUNIYA DAFATAN ZAKI KU FAHINCE NI.

Yau alhamis bamu shiga islamiya don haka na ke son zuwa ziyara gidan yan uwan mahaifiyar mu dake a cikin gari.
Zaune nake ina kwaliya a kofan dakin mu yayin da mutane gidan mu ke ta aiyu kan su na yau da kullu a cikin su har da ummi na wacce ke wanke kofi.
Sallama aka shigo dashi gidan dashi shi ne ya dauki hankalin kowa a gidan baki daya tare da amsawa.
A, a mutanen lagos yau she agarin abinda su maman mu ke fada ke nan mu yara muka shiga sannu da zuwa.
Ta dan tsaya a tsakar gida suna gaisawa sama sama da mutanen gidan da ga nan ta kwasa tai dakin mama,
Daya bayan daya ake shiga gaida ita tana amsawa don sanin muhinmanci ta ga iyayye mu baki daya.
Gwago kulu ke nan kauna ne ga mama kuma yar uwa ga mahaifin mu don mama da mahaifin mu yan uwane dukkan su auren gida ne sukayi irin matar fari zabin iyayye din nan.
Haka yasa mama ke shimfida mulkin ta yadda taso a cikin gidan daga ita har yaran ta ko magana ake a gidan wanda ya shafi gida zakiji mama tace mu din kujera ne dole a bi mu.
Don da mijina aka samay ni ko anki ko an so dole ne a gan mu a gidan babu yadda za yi damu dan mu yandagi ne.
Watarana idan tana irin wannan habaicin Inna takan biye mata suyi tayi sai sun gaji har ta kan ce ban ga macen da zato tace zata shifida min doka ba a gida na.
Sai dai duk wannan haukan ga may wayau da hankali yasan Inna ce ke shimfida mulkin ta a gidan don baba a can hankalin shi yafi karkata.
Ni dai nakan ce tsoro ne don wani lokaci zaka ga ya juya gun wata da zaran inna taga haka yau zata birkice mashi da masifan dare daban na rana daban saiya dawo a kan ta.
Duk wani dan uwan mahaifin mu da zai za gidan wirin mama zai yadda zangon shi ba zai tafi wani daki ba sai in wani dalili ya kawo mai shi.
Wannan abin yana kona wa inna rai don ita mace ce mai son taga komai ita ne a kan gaba a gidan namu.
Saida na kanmala kwaliyana na saka hijjab dina na karasa kofan mama ina fadin sannu da zuwa gwago alokacin sun hade kai da mama suna magana a hankali kasancewan su biyu ne a dakin ki.
Cikin dan hanzari ta amsa min da yawwa na juya zan tafi sai take cewa wa nake gani kamar sai tai shiru can tace ba yar wurin Rabi bane ?
Mama tace itace tace, mana tace ikon Allah girman dan mutum baida wuya har yaushe yaushe aka haifi yarinya nan diba yanzu yadda takai da girma.
Sai naji mama tace ta biyo tsawon kafan uwar tane kisan Rabi ba baya ba wurin tsawo shine suka kwaso ai duk haka yaran suke in kin gansu.
Nidai na tafi ba abina ban tsaya jin sauran abinda zasu fada ba don dai zancen bai kare ba na bar su akai.
Dariya naji sun kwashe dashi wanda nasan wani sheri aka fada wanda yai dadi har sukayi hakan .
Mu Huda muka fita da kannena gidan gwagon mahaifiyar mu muka fara zuwa inda muka samu taro na arziki ta rasa ida zata saka mu.
Haka mu ke gani idan munje gun ta muna samun taro yadda ya kamata sabanin dagin mahaifin mu, wanda basu ma san da zaman mu ba nake gani.
A binci ta shiga girka wa don idan muje wuni muke a gidan ta, nafito na kama mata aiki yadda ya kama ta har muka kan mala yin komai.
Abinda bamu saba ba gidan mu an cika muna kwano da shinkfa da mai da yaji sai ci muke yi hannu baka hannu akushi.
Ga zobo mai sayi data sayo muna mu sha dashi mun kai kat na kwashe kayan da mukai aiki da amfani dasu da wanda mukaci abin ci akin sa.
Na gyara mata gida sai nace da ita zamu mu gaida su mama watau diyan ta ke nan dake aure a cikin uguwa.
Tace kada mu dade don mu koma gida da wuri mun tafi inda can ma muka samu taro yadda ya kama ta sun bamu alheri su man shafi da sabulu da omo da dan kudi muna ta murna mun samu kyau ta .
Gwago ma tai muna abin arziki muka dawo gida bayan sallah la, asar cike da zudin kyautan bajin ta da muka samu.
Muna tajin dadi muka nuna wa ummi alherin da tan uwanta suka kai muna ta sani tare da fadin shine abin dayasa bani son kuna zuwa gidan su don dawai niya kuke kai masu.
Kani yai caraf yace ummi cewa sukayi fa mu dinga zuwa ko yaushe kuma kikece damu kada mu koma abamu .
Gaba daya dariya muka sa mai ummi tace damu tare da dubana nida nake da wayo a cikin su yawan zuwa zai sa su gaji daku ne ku zauna matsayin da Allah aje ku Allah zai dube mu.
Jikina yai sanyi don na fahinci may ummi take nufi din a sanyaye na ce in sha Allahu ummi baza kara zuwa mu kai masu nauyi ba haka.
Dan abinda muka samu ummi ta ware min wani abu acikin sa waina kara jari dashi na sana, a na da nakeyi kada mu kashe a baki daya.
Wanan kudin shine sillar da har takai mun da samun sauki a dakin mu don a hankali na fara sarrafa kudin biyar na kamowa goma gama na zama ashirin ashirin ya koma wazo har zuwa sama.
Idan baka raina sana, a tau watarana sai ya koma maka babba don tun ina dan madara har na koma ina soya ruwa ana saye a gida.
Sai gashi har nawaje suna shigowa saye na hada da aya da sauran makulasa sai sanaa ya koma na ummi na.
Sannu sannu ina sana,ar har muka koma mangyada da sauran abin amfani kudi na shigo muna.
Sai hassada da kyashi ya shigo a cikin wa yan gidan mu nan kuma bamu da sauran shakat gare su zasu ce damu ganin muna dan sana,an dake kawo mu kudi ya muke son yi masu gani gani.
Sai suka da habaici ya tashi har zance yakai gun baba na magana kadan yanzu zai yo cikin ummi da zagi yace wai mutane suna shigo mai gida don su din ga lekan may asirin gida suna fita waje suna fadi.
Nan mama ta turza don kan taki yarda da zancen baba na wanga karon ta ko hankace mashi da fitina tana cewa ai da takoma in irin halin da ta fito gara ta hankura dashi ta tafi inda ake son cigaban ta yafi mata don ta ganne cigaban ta akewa hassada bakomai ba.
Inda watane ke wanan sana, ar aiba za hana ba amma don anga tana samu za ai mata bakin ciki ga sana,an ta, kowa na dan sana,an shi cikin gida bai yi magana ba, sai nata ne za ia wa bakin ciki.
Da haka zancen ya mutu karshe mama ta ce ya kyale ta taita sana an ta tunda kowa na saman sanaar ashi badon aina tasa ba dole ta kyale ummi ta ci gaba da sana, an ta tana na kallo ba yarda zata yi a gidan.
Wanan ke nan ya wuce saura wani kama don ummi ta kyatare wanan karon daga kaidin ta.
Wanan abin da akeyi ina yar shekara goma sha uku da haihuwa amma duk idon gidan mu na ga kaina gaba dayan su kamai yan yazu ace safiya ce.
Koban ji ban gani ba don dai kawai ai min fada suji dadi yanzo zasu jawo abinda za ai min fadi din .
Duk wani aiki aike yi mai dadi da akasin sa duk ni zan yi amma duk wanan ban tsira akan shi ba don cewa suke wai lalaci da raggaci yai min yawa.
A haka jebawan mu shiga secondary yafito inda naci makarantan kwana aiko take yan gidan mu suka nuna bakin cikin su ka zancen.
Suke cewa makaratan kwana ko lalacewa may zaki koyo banda lalacewa a makarantan kwana bokon diya mace ko lalacewa.
Kai komai sun fada akan wanan zuwa karatun nawa karshe dai baba sha zuga sai cewa yayi abar zancen karatu don shi bai ga amfanin yin karatu ga ya mace ba.
Ina ji ina gani aka watsar da zancen karatu na ganin da gaske baba keyi na sulale jiki na tafi wurin gwago na fada mata komai.
Batai sanyi ga gwiwa ba ta sami babana a kasuwa don magana bai yi a gida nan dai gwago ta shawo kan shi har ya yarda amma da sharadin .
Baba hannun shi a ciki ko kwadalan shi ciki gwago tace taji ta dauka akwai Allah zakawo mafita.
Amma yace ba zai yarda da batun zuwa makarantan kwana ba gwago tace taji zasu samo jeka ka dawo na tafi.
Wannan shine dalilin zuwa na makaranta da nayi mutane gidan mu dai sun ga ina shirin ba su san komai ba.
Ranan da zan fara zuwa hankalin kowa a gidan ya tashi don sai suke zargin mahaifin mu ne yai min ko mai.
Nan ko ina ta saka shi a gaba da cewa munafucin banza da wofi idan an tanbaye shi kudin yace bai dashi amma ya dau ki yar gwal ya saka a makaranta don ran uwar ta yai dadi.
Ba dole ba yana gudun bacin ran uwar ta kada ta hana shi kwana da ita ya rasa jin dadin shi.
Da abin ya ishi baba yai ratsuwa har ya gaji shi ba dasanin shi bane baiba ma san wanda yai samo min makaranta ba amma nasu yarda ba.
Sai cewa yayi ya biya min din suda yake wa dayan su lalurori fa saiko fada dashi da inna har takai ga yin ya ji a gidan.
Yaya sani yace safiya ki shirya da kaina zan kaiki in ga wanda ya isa ya hana ki zuwa na gane yan bakin ciki ne mutanen gidan nan.
Da yaya sani muka tafi makaranta sai da yaga komai ya kamala ya dawo gida.
Tun wanan lokacin aiki ya rage man agidan namu saboda ban da lokacin zama a gida har su ganni suce in ma su aikin.
Sannu a hankali girma ya shi gana yanzu na fara ganewa bawai son ummi ne mahaifin mu ba yayi ba kawai dai shakun matan shine yake ji.
Na gane hakane ta yadda idan ya fakaici idon matan shi yake nuna kulawan shi kan ta har nama yakan dan ja ta da wasa ko da ba, a.
Sai dai idan matan shi sun gani ya kan dan yi kamay kamay kamar bashi ne daga karshe dai ya koma fada kamar bashi ba.
Kadai muke zaman mu da dadi ba dadin a gidan watarana mu kwana da farin ciki watarana akasin sa.
Sannu tashi na kamal aji uku zan shiga babba ajin aga da secondary sai ga gwago tazo daga lagos nan mukai ta murna da zuwan ta sai awan kararon bata ita kadai tazo muna ba.
Ita da zurian ta da maigidan tazo ganin mu nan aka shiga ina aka saka da ita da diya ta da maigidan ta don dai ba karamin son ta yan uwa keyi ba, in zata zo takan sayo abubuwan anfani tajo ma iyayyen mu da shi.
Nikan ina saurin naje makaranta don haka tsayawa nayi daga kofa na gaida su dan suna dakin mama ne zaune har mijin nata da yaran ta.
Take cewa wanagani kamar yar wurin Rabi haka koyaushe za a gan ki kamar ke kadai ke kiwo a gidan gaki tsatsab dake kamar wata wayyayiya.
Murmushi kawai nayi zantafi sai naji tace wanan ai takar ita koke kiyawu agidan.
Ta juya tana magana da mama bandaiji abin da suka fada ba nai tafiyana don ina saurin in tafi makaranta.
A kofan gida muka tarar da wani matashi yana shan taba zaune saman mota kallo daya nai mashi na kawar da kaina daga gareshi.
Sauri nake na wuce don da gani tare suke da gwago mu sai naji yace ke shiga ciki ki dabo min ruwa nasha.
Na dauka badani yake ba ina kokarin wuce wa naji ya sake cewa dake nake fa na juya baya na ko zanga wace yake magana da ita.
Sai naga babu kowa a tare dani na dan tsaya kadan yace ruwa nace ki debo min a ciki.
Juyawa nayi nakoma na debo mashi ruwan nakawo mashi ya kurba sau daya yake cewa wanan wani irin ruwa ne mara dadi.
Nace shi muke sha a gidan mu don haka shi ke gare mu, oho i see waya kaleni sama da kasa yake cewa karbi ki mayar .
Haushin sa ne yakama ni lokaci guda don ya rena muna wayau da arzikin gidan a haka dai na karba na wuce shi don warin taba duk ya isheni da hamami.
Na dawo zan wuce yake cewa dani ke yana kokarin kuna wani taban a bakin shi shigo kice wa su mum sufito haka nan dan Allah.
Kamar nace bazan tafi ba sai dai na juya zantafi sai gasu sun fito daga cikin uban na gaba suna biye a bayan su.
Nikan nawuce abina ban tsaya kara sauraren su ba don dama nakara zuwa islamiya duk da nasan bawai buguna za ayi ba amma ya kamata ace na isa a cikin lokaci.
Har na isa makaranta ban dana jin warin taban da aka sha a jiki na ba gani nake duk jikina warin taba yake kamar nice nashi taba din .
Mun dawo na debi kayan mu na wanke don ban samu wanke wa da rana ba aka raba tsaraban gwago ko wani daki aka bamu.
Saida na shigo dakin mune na samu tsaraban da gagwo ta kawo muna a gefe, na samu wuri na zauna gefe ina cewa da ummi.
Wanan mutumin dasu gwago suka zo dashi dazun baida tarbiya zama fa yayi kofar gida yana shan taba a gaban ko wa.
Ummi tace dani wa kina nufin ubale aishine dan gwago kuna fari duk sain an ni shi sunyi aure amma shi, shashanci ya na shi yi wai shi dan fari yana takama da zama cikin kabilu ya saje dasu.
Nace Allah ya kyauta amma kan wallahi bai yi ba wallahi mutun sakace wani ibom can.
Muna cikin magana mukaji fada ya kaule a tsakanin mama da inna kan kayan da gwagon mu ta kawo tsaraba inna ke cewa da mama wai tarage kayan ta basu abin da taga dama.
Mama ta bata amsa da cewa yar uwarki konawa ina yar uwa nane dai ko kaya kuma abinda naga dama kenan na bayar inkina so ki karba inbaki so zaki iya mayar.
Mama tace idai kayane je ki ta ci saukin abindai muma muna da yan uwa bake kadai keda su ba balla ki kawo muna bakar magana.
Muna daki da ummi muna sauraren su har suka sude bamu leko ba sukayi suka kare ba mu leka waje ba.
Washe gari kuma da safe suka aza sabon fitina a gidan baba na dakin inna ya fito yake cewa daga yanzu indai rabo zai kawo fitina kowa ya rike abin sa a zauna lafiya.
Da haka karshen fitinan ya mutu kowa in yaga dama ya rike kayan shi ba dole araba wa saura inna tace yafi nono fari.
Mu dai namu dasu ido don sun fi kusa wanda yace zai shiga fadan su a ciki zai kwana minti goma yai kadan aga sun shirya tsakanin su.
A yau asabar bamu zuwa makaranta don haka na shirya cikin kayan da mama lami ta ba ina son zuwa gaida kawata da bata da lafiya.
Wanan ne karo na farko da na sa kayan a gidan mu don basu san ni da kayan ba nan sukayo mani ca da idanuwan su naji mama tana fadin.
A yau kwaliya akaci haka yau sai ina da wanan adon nai murmushi kawai ba tare da na bata ansa ba sai naji inna na fadin ke ma dai yaya da wani zance ki.
Yarinya kekaga tana wanan irn kwalliya haka ai kin san abinda take yi inba mashin shine ai banza ya kai zomo suwa ke ma kin san aida wallakin wai goro cikin miya.
Muka hada ido da ummi na sai taimin da alama da ido na kyaleta na kara shiryawa nake cewa zan tafi tare da yi masu sallama.
Inna tace dama diya mace inta dadani namiji ai ba tafiba hankalinta bai taba kwanciya yawon gantalin za, a ake sallaman mu.
Kai akwai ki da wani zance wallahi ina safiya da ga wani saurayi kyalle ta dai da nacin son karatu a rayuwan ta inji mama ke fada mata haka na.
Ta ja tsaki tace ai ku ke kara zugata wanda baida lokacin kan shi a gida kulun boka watafi son karatu adaiyi shaani kawai wai an cuci na kauye.
Na fito gida ina tunanen kallamin inna ba zaka taba jin kalman alheri abakin ta ba in ba yayan ta bane sai na sheri.
Ita da bakin ta take fadi wata rana yarinya ga kyau ga wanka amma babu saurayi yau kuma ta can za ta kuma ce maza naka bi.
Naje gidan su Amina na samu bata da lafiya sosai amma ta samu sauki na dan zauna da ita mukai hira nawani lakaci na mike zani gida don kar na dade Inna tace sai da ta zubar nadawo kuma.
Mun fito tare da Amina donta dan taka ta walwale jikin ta muna tafe muna hira inda muke tafiya a hankali ina bata labarin text din da kayi muna, bata nan yadda ya kaya.
Hon din motane ya damay mu daga bayan mu da kara daga ni har ita ba wanda ya juya dan gani ko wa nene mai mator kuma bai daina hon din ba.
Ganin ba zamu tsaya ba yasa shi fito wa a motar ya biyo mu, sallama yai muna duk muka juya a lokaci daya muna kallon shi.
Nikan a zato na sun san juna ne sai kawai na fara tafiya na barsu tare ban tsaya ba kada naja wa kaina magana ban yiba ance nayi ina ga na tsaya.
Sai naji yace don Allah malama ko zaki taimaka taimaka min da yar uwar ki ta saurare ni min ti biyu in ba damuwa.
Safiya dake ake magana inji Amina, na juyo nace wani a cikin mamaki yace nasan badaidai ba ne na tare ku a hanya.
Amma kuma dole yasa na tsada ku a hanya yanzu don idan kun tafi ban san ina zan kara haduwa daku ba.
Nace gaskiya bazan tsaya ba sunana ya baci ga ban za a saman hanya sai yai murmushi yace naga alama ai amma don Allah kibani dan lokaci nasan wani abu gare ki.
Allah daya ke hada mu dashi har da Amina din yasa na tsaya badon na so ba ya ce sunana sulaiman ni dan garin nan ne saidai ba anan nake ba.
Ina fatan zaki bani amsa ga tambaya a wurin ki don Allah ida bazaki damu ba zan so nasan gidan ku don na gabatar da kaina.
Gaskiya malam kayi hakkuri saboda karatu nake yi sai an jima nan nabar su tsaye awurin na wuce.
Ya dan rintse idanuwa shi tare da sauka da ajiya zuciya yana mai sauke num fashi , ya dan yi murmushi tare da duban Amina dake gefen shi tsaye yace.
Idan ba damuwa ki tai makeni da noba ta kokuma gidan su zai fi sauki a gare ni nan dai yabawa Amina tausayi tabashi addresen gida yai mata godiya ta tafi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button