BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/6/20, 10:18 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , ,

????????7️⃣2️⃣????

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU KU, , ,

Duk da bakunta muka zo amma bai hana uncle sheri ni ba a gaban kowa akan bukin gidan yar uwar shi da muka tafi har khadija ta fahinci bamu cikin dadin rai dashi.
Sai dai yazo ya duba dan shi yadan yiwa khadija magana ya fice dakin batare da ya kalli inda nake ba a rana ta uku yashigo duba Abba da ke kwance saman gado yana ta wasa irin na yara.
Nikuma ina wa khadija kalaba a kan ta ya shigo ina kwana khadija tayi mai ya tambaye kin tashi lafiya ta amsa mai da lafiya kalau.
Yadan yiwa yaron wasa ya juya ya fita ajiyan zuciya na sauke bayan fitan shi daga dakin har tana iya jiyo ni lokacin.
Muryanta ne ya katse ni ga dan tunanen da na fara a lokacin tana cewa wai anty mijin ki fushi yake dashi haka ne ?
Tun dan maganan fitan nan yakewa fushi haka naga ko abincin da ake aje mai baya ci haka yake fita ya bar shi anan nace a gun hajiya yake zuwa yaci ai.
Ashe haka yake da fushi anty ?
Na sake sauke numfashi nace matsalar shi ke nan wallahi khadija ni abin na damu na ko an bashi hakkuri kamar zugashi mutum ke yi.
Tap ai irin su ko wuyar zama gare su may acikin wanan dan maganan don Allah da zai rike haka kuma fa bukin yar uwar shi ai muka je.
Nace wallahi haka yake khadija sai kiga magana bai kai abin fushi ba amma sai ya saka a ranshi har ka gaji da fushin.
To kema ba sai ki koya ba idan ya hau ki hau sai ai tayi nace ban taba gwada hakan ba ina dai iya kokarina naga ya sauko daga fushin nasa ne.
Aiko ki na da aiki to wallahi bari kiji abinci ma yanzu idan an kawo mayarwa zance ayi mun koshi kuma ba zamu sake fita ko falon hajiya ba indan yayi magana in baki iya bashi amsa ni zan nashi ne.
Yaya zai kawo mu garin mutane kuma yasan din shi muka zo zai kama wullakanta ki haka a gaban kowa.
Itama mahaifiyar tashi bazatayi mai magana ba wanan abu yaki ci yaki cinyewa kamar cin kwan mahaukaciya.
Barshi haka muka saba da kan shi zai sauko ai tace wallahi sai mun gwada maza fa sai da harbi yanzu idan yana takama dashi ne aikema kina takama da kimar ki ta mata don Allah ki kwantar wa kanki yanci .
Idan ya hau kifishi hawa aga wa zai wahala ko dakin shi kada ko koma zuwa idan nashi ya nemoki ba.
Ni wai auren Ahmed ya mai dake haka ko may ko dama haka kike han sani ba don wayau na baikai in gane bane.
Nifa yanzu ko a kidan mu na koyi abubuwan zaman aure da dama wallahi zan iya zama cikin mata uku in tashi tsaf dasu.
Dariya ta bani har nakai mata dan gwara a kai tare da fadin na raba ki mata uku wasane kin kuwa san kishin yanzu khadija.
Tace tsab kuwa wallahi na miji idan baka wana shi sai ka koma shata, lalaganshi a gaban kowa yana iya muzanta ka ji fa jiya gaban su anty suwaiba ya disga ki.
Nace ai shi bahagon mutum ne ga dadin zama ga wuyan zama dadin shi kawai idan yana cikin dadin rai da kai idan kuma ya hau abin ba dadi duk nakan tsawala ne wallahi.
Kowa ya mashi darasi aike ma mutunce kamar kowa kina da inda kike da ranan ki bawai kudine zai ba mutum abinda yake so ba ko yaushe.
Ni ba don kudin shi na aure shi ba don rifin asirin kaina da samun inda zan fake ne tace sai kuma akace bazaka san darahan na tare da kai ba nace kai khadija ummi ke nan .
Tace ban son abin haushi ne wallahi shi daga ma kin rufa mai asiri ya tsufa ko kwai baka aje ba ka samu mata yarinya ke idan lafiyan ki kalau yadda kike nan ba sai kin darje kin samu miji ba na zaba.
Ji yadda kika koma kamar wata matar gwauna can dake kin yi wani kiba kinyi jajir duk inda kika shiga abin kallo ne ga mutane baki da inda za a raina ki in ba wurin ilimi ba.
Dangwara na kara kai mata nace badai ina da na zuwa lahira ba ashe ko ina da ilimi don may yafi kana da karatun ka na Allah dadi.
Nifa abin da yasa kika ga ban wani damuwa da karatun ba khadija na ga dai har guda nawa duniyan take a yanzu dai ban rasa komai ba nasan kuma idan karatun zan yi shi zaita hada mu fada kishin shi.
Don haka ne kawai na rungumi aure na na zauna dakina tunda ban rasa ci da sha ba da sutura tace ai shine na gani tunda a lokacin kowa gani yake mutuwa zaki yi amma yanzu gashi har ana mantawa ma da akwai wani matsala a tare daku.
Shi wanan ma bai ishe shi ba har sai yayi wani fushi kana cikin irin hali haka na ubangiji.
Sai naji maganan ta na shiga dama mun je gaida baaba da safe tun lokacin bamu kar fita daga part din ba akwai drink’s da su kayan tea a wurin mu da dabun nama shi muka yini ci don ko da aka kawo abincin rana sai nace a mayar abawa mutane mun gode a koshe muke mu.
Ga na dare ma haka nace a maida kar ya baci mun koshi ina gama sallah ishai muka rufe dakin mu anan dakina wirin khadija na kwanta.
Ya dawo sai mahaifiyar tashi ke fadin yau ko matar ka lafiya suke daga ita har kaunar ta dake zuwa wurin yaran nan hira ba wanda ya leko mu tun safe.
Abinci ma ankai masu suka ce a dawo dashi sun koshi ban san may sukaci ba ka bincika min su don Allah.
Koda ya shigo part din mukan har munyi nisa da barci a lokacin a zaton shi ina dakin shi kwace don wutan ko ina a kunne yake.
Ya kashe wutan ya ya shige yana waigen kofan dakin mu don yasan yanzu khadija tayi barci ko ba daman ganin yaron shi.
Yana shiga dakin duhu ya ziyarci idon shi da kyat ya nemi makunnin wuta ya kuna haske ya gauraye dakin lokaci guda yakai duban shi saman gado don a cike ya shigo ya sauke min fada rashin kashe wutan falo da ban yi ba na kwanta abin namu kuma ya karu.
Har ya na shirin shi yana yi yana kallon kofan daki har ya gama ya kwanta ban shigo dakin ba har ya kwanta yana faman juye juye saman gado don bai saba kwana shi kadai ba sai tare dani.
Yau kuma ya rasa dalilin kaurace mai gaba daya danayi ga hajiya tace tun safe bamu ci abincin gidan da masu aikinta ke girkawa ba a gidan gaba daya.
Nikan ina dakina mun baje a gado sai sharar barcin mu mukeyi duk da hankalina kafin inyi barci yana gun shi.
Da safe ma da muka tashi ban shiga wurin shi ba har ya shirya zai fita komay ya gani sai gashi dakin namu.
Kwace nake kishingide sai Abba dake wasa kusa da cheast dina saman gado yana gwalanniya iri ta yara yana faman har ba kafafuwan shi sama dayan yatsan shi na rike a hannun na .
Khadija na gefe saman gadon tana kallo a wayan ta jin sallaman shi yasa ta dan dago tana kallon shi tare da fadin yaya ina kwana ta mayar da kanta ga kallo kafin ma ya amsa.
Ina kwana nima nace mai daga inda nake kwance rigingine ban tashi ba kamar ba zai amsa min ba sai naji ya amsa a wani irin yanayi.
Ban kawar da idona gare shi ba yadan yiwa Abba din wasa sai ya juya kamar zai wuce sai kuma ya juyo yana cewa dani jimana.
Sai ya fara tafiya zuwa falo anan na samay shi tsaye kamar mai nazari nace gani fuska a daure babu fara a gare ni.
Ba a kawo abin karyawa bane daga wurin hajiya nace an kawo yace ina yake nace an koma dashi don babu maici idan an aje a nan din.
Kamar yaya ba maici ku baku ci ne nace akoshe muke mu wani kallo ya watso min naji tsoron kallin amma na dake na bar tsoron a raina.
Kina nufin baku iyacin abincin gidan nan ne komay ?
Akan may bamu iya ci agidan mu akwai irin sane kawai de banjin cin komai ne ai idan zaci ba bakuwar hajiya nake ba sai naje can in diba kai kuma naga ba a nan kake ci ba shiyasa.
Hannu ya daga min alaman dakatar dani yana fadin ya isa haka ban tambaye ki dogon shirhi ba na fahince ki yanzu.
Akan may fa ?
Na tambaya cikin dakewa kamar zaiyi magana sai kuma ya sakai ya fita daga dakin na juya na koma daki na nima.
Ya isa wirin hajiya ta ga yana cika yana batsewa kamar zai fashe tace dashi ina son ka da hakkuri kada ka dauko yar mutane uwar duniya kazo nan kana cuta mata akan dan abu kadan.
Hajiya kyale wanan yarinyar rainin wayo take son kawo min idan ma ta kawo ma raini ba mijin ta kake ba ?
Ka tsaya ku fahinci juna da ita yanzu haka ba wani matsala bane amma kai ka dauke shi babba haka kada fa ka koya ma wanan yariyar halin da ba nata ba.
Don ba zai maka dadi gaba ba gashi kun fara tara zuria da ita kowa na murnan haka ni banga wani matsalan da take dashi ba.
Bai iya magana ba sai faman tura abincin da yake yi a bakin shi murya ta daga ta kira yarinya guda tazo tace jeki part din su kikira min matar shi yanzu.
Yarinyar ta fita zuwa part din taci gaba da mashi nasiha a kusan tare muka shigo falon na hajiya da yar aiken.
Ina saye da hijjabin sallah na ajikina na shigo da sallama na sai da na kara gaida ita na samu wuri na zauna a kasa gefen kujera.
Dan shiru ya biyo a falon sai faman shan ferfesu take ba tare da ya daga idon shi ba balle ma yasan na shigo falon a lokacin.
Safiya ta kira sunana da sauri nadan dago kaina dake kasa na kalle ta tare da fadin naam hajiya.
Tace may ke faruwa ne tsakanin ku da mijin ki kunzo min lafiya yanzu kuma sai na fahinci akwai abinda ke wakana a tsakanin ku dukkan ku ku biyu don ba haka kuka zo min ba nan.
Shiru nayi ban dago kaina ba sai da ta kara maimaita maganan ta tace kada ki boye min idan wani abu ke faruwa ni uwa ce ga dukkan ku.
Kai na kara saddawa kasa nayi shiru sai tayi murmushi tace bai fada min kinyi mai wani abuba sai dai na fahinci kwana biyun nan da yana zuwa nan cin abinci.
Kuma ke idan an aika maku sai kice a dawo min dashi ko an barshi acan babu mai ci yaya zaku zo min bakunta gidana kuma ku tsiru min wani hali na daban ?
Haba safiya ki fada min idan wani abu ke faruwa na sani tun baku koma haka a dunkule ba kin ga sai in zama uwar banza gare ku.
Sai lokacin na dan dago kaina nace ba haka na bane hajiya ba komai wallahi ta katse ni da fadin akwai komay idan babu may kuke ci keda yar uwar ki data rako ki kuma ?
Hajiya nima ban san may nayi mai ba tun ranan da muka je gun bukin gidan su Aisha yake wanan fushin dani kuma ya daina zama yaci abincin a can ko nayi mai magana baya amsa min sai dai yayi ta fushi.
Wanda ni ban san dalilin yin hakan da yake min ba na bashi hakuri da fada mai tare da yan uwa muka tafi ba zan dawo na barsu can ba tunda tare muka tafi dasu.
Tana cewa kwarai kuwa shi kuma yana fadin karya kike yi ai kin san bana son yawo amma kika tafi kika zauna sai da kika kwaso ma yaron nan zazzabi da ya wahala.
Sokike ki, , , , , ,
Ya isa haka baba ya isa nace maka ko yace hajiya could you belief wai har tana iya fushi akan na dauki mataki akan abinda tayi min.
Kai baba karage wanan zuciyar naka ina ce ka daina jin ku shiru danayi ashe kai har yanzu halin naka nan maka ?
Bukin yar uwakar fa taje tare da yan uwan ka kuma ashe kai wanan ba abin farin ciki bane gare ka yau ga iyalin ka cikin yan uwan ka anayi dasu.
Ciwo koma da yaro yayi ai canjin ruwa ne yara dawa haka na faruwa dasu idan anje sabon wuri da basu saba da yanayin shi ba.
Kaiwa yarinyar nan adalci mana haba yanzu cikin wanan magana may ye na zafi haka a cikin shi don Allah kai ka hau ita ta hau kaga abin bai yi kyau gani ba wallahi.
Shi fa mutum mai hakkuri ba a son a kure shi idan yake an kure shi abin bai kyau yanzu gashi kace wai tana fushi da kai ?
Ta gaji ne da baka hakkuri ta kyale ka hakana tunda kai ba a iyaka ina da labarin zaman ku sarai a kunne na yarinyar tsoron ka take ji kada ka kaita makura ta koma ma kamar sauran mataku na bariki.
Ke kuma ba a gajiya da hakkuri tun dai ga miji zaman takewan aure da hakkuri ake cin riban shi ba zaki biye mai ba har ku kai ga sabon Allah don haka na kashe wanan magana.
Tashi ki koma dakin ki wanan magana kuma ya mutu a nan kada in kara jin irin shi don Allah na dago tare da fadin baaba na gode.
Na mike na fita tace ku samu abinda kukaci ke da yar uwar ki kada ku zauna da yun wa haka ba a bakun ta da yunwa ko ai fushi da abinci.
Ina sa takalmina a kofa naji tana fashi fada sosai irin na da mahaifi ni dai na wuce part din don ko fada ta yi mai kan shi da yanzu sai yiwa wasu fadan haka kuma ahi din yake yin haka a gidan shi.
Ko da na koma Khadija tana nan tana kallon ta a waya shigowa na yasa ta dago kan ta tana fadin may akayi anty ?
Nace kila kara na yakai gun baaba ban sani ba ta dai yi muna magana ne akan abinda ke faruwa tace ai yanzu kiga ya gyara nace kila ba.
Wai kina ma da hakkuri nace in ban yi hakkuri ba khadija may kike son inyi a nan ai hakkuri ya zama min dole tunda haka halin sa yake cikin ma wai ya rage ke nan fa.
Falo muka dawo muna kallo har anty suwaiba tazo a gurguje ta leko mu tana fadin sauri takeyi ta kawo ma hajiyan su sako ne.
Na dan rakata zuwa part din baaba din na dawo ban dade da zama ba sai gashi ya dawo gidan sannu da zuwa muka mai cikin rashin sakewa tare da mu.
Kallon khadija yayi yace khadija har dake ake fushin da ni ko ?
Tace a a yaya wane ni shiga tsakanin miji da mata ai kun fi kusa ni ba ruwana da maganan ku yana zama yace ban yarda dake ba.
Idan ita bataci abinci ba ke may ke hana ki cin abinci tace kasan ni ba damuwa nayi da cin abinci ba dama.
Yace ban sani ba don ban je gidan ki ba koda yake naga alaman kamar yan bauchi zasu sake samun karuwa don naji ance kin yi saurayi a nan ko.
Maganan da yake yi ne yasa nasan ya sauko daga fushin da ba dalili da yake yi din na mike na barsu nan suna ba,a da ita dining naje na hada mai abincin ranan da aka kawo muna part din mu.
Ga abinci can uncle na fada yace cikin sakin fuska kamar ba shi ba barin dan shiga in fito kafin in zauna ci.
Ya juya ya shige tana jin karan rufe kofan shi ta juyo tana kallo na tace aina fada maki irin su sai da saiti wallahi nace ai naga alama.
Ya dan jima ya fito daga dakin ya sauya kayan jikin shi don zafin da ake a gare direct dining ya nufa don haka na tashi naje don zuba mai abincin har lokacin ba wani walwala a fuska.
Har na zuba mai na juya zan wuce yace yaya haka ku kunci abuncin ne halan ?
Nace mun ci tun dazu yace ta ki zauna na gama kin san ban son a bani abinci a wuce dole na dawo na zauna ina dakilan wayana can naji yace ki shirya da dare zamu tafi gidan su babffa mu gaida su.
Allah ya kai mu na bashi amsa har ya gama ina kokari kawar da kayan ne naji yace naso zuwa Abuja gobe in dawo jibi amma sai abin da hali yayi goben.
Allah ya kaimu na bashi amsa tare da cewa wani abune zaka je naga saura yan kwanaki mu koma can din ai.
Zan tafi duba wasu kayane da suka iso Saadu ya bugo min waya wai kayan basu cika ba kuma ba irin wanda mukayi oda aka kawo muna ba.
Goben dai zaka tafi ke nan na sake tambayashi ya mike saman kujera daga zaune ya balance da kafafuwan shi yace ai dole in je in gani da ido na kada su cuce mu kafin a bude don ban son abinda zai kashe muna kasuwan mu.
Allah ya kaimu nace dashi tare da ci gaba da abinda nake a wayana wanda hankalina yana a kai.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button