BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , ,

????????????????????

NAGODE DA KUWALAWAN KU GARENI YAN UWA DA BAZAR KU MUKE RAWA

IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH KARKI KARANTA YAR UWA DON A KWAI NAUYI A KANKI.

Nazama sha tikan duk dare yaje yawon shi ya dawo, acikin maye zai nemay ni idan nakiya kuma zai min mugun bugu ya biya bukatan shi.
Gari kuma ya waye in tashi in girka mashi abinda zai ci don ciki ya kwakware mai da ruwan giya.
Daya tashi babu abin da yake nema sai abinci mai dan nauyi da zai cika ciki dashi idan ya gama wani bi ya kara nema na koda karfin tsiya ya biya bukatan shi.
Acikin irin haka na ranan yana tsaka da buguna, sai ga yaya saadu ya shigo gidan namu yayi sallama har ya gaji amma yana jiwo ihuna daga ciki.
Kai tsaye ya fado cikin gidan ya samu ya danne ni ya ta bugu a kasa da karfi ya tire shi samana daga ni sai underwear a jikina.
Ya na ganin na haka nan ya juya baya da saurin shi shiko gogan sai mazurai yake da idon yana mai mai da numfashi .
Sai ya hau zage zage yana fadin sai ya halakani a gidan nan wani tsawa saadun ya daka ma wan nashi daidai na samu na daura zani a jikina ta dawo ciki yana cewa .
Amma bros baka kyauta ba wallahi ina yarinyar ga taga karfin ka da zaka dinga dukanta haka yace dakata mallam kada kazo min gida kace zakai min nasiha kan wanan bazan yarinyar mara mutunci.
Yace haba bros matar kace fa ta sunna kake zagi haka ya kamata ace yanzu ka daina abubuwa da daba ka kama kanka.
Ya juya wurin ina ta faman kuka yace kin ga Safiya ya isa haka shiga ciki ki kitsa kan ki kizo haka bakyau wallahi.
Nasamu naja kafana zuwa daki wanda da kyat nake dagata don wallah ina shiga naji yana cewa dan uwan nashi wanan abin baiyi ba wallahi.
Na dawo sadiya ke fada min irin sherin da habiba ta kulla mata wurin mummy a gaskiya abinda kuke yi baku rike amana ba.
Yace wani amana can dama waya ce yana son ta ko waya nemota sai dan uwan yace mummy kuma hakan da akai maka bakaji dadi ba yanzu ji yadda ka koma kaima kasan akwai banbanci da yadda ke da a watse.
Ashe ko aure dadi gare shi ko ba a fada ba yarinyan nan tana fa da hakkuri har yakai ka kure hakkurin nata ta soma mayar maka da martani kana babban kanka.
Nan dai yake cewa yarinyar baza ne kana ganin ta wurin nan munafukane ta kware bata da kunya sai na gwada mata ba irin mu akewa haka ba a tashi lafiya.
Yaya saadun yace baka ko kyauta ba wata mace zaka samu ta zauna tana hakkurin da irin halin ka nan dai sukai ta kwasan dashi.
Daga karshe ya shige dakin shi ya barshi a zaune a wurin ya kwala min kira na fito ina kuka ina share hawaye da habar zani na.
Nazp na durkusa kasa gefen kujera ina cewa gani yaya ya dago yana cewa a haba dai hau kujera ki zauna mana na girgiza kaina nace nan ma yayi min.
Yace Safiya msi yasa bakiyi wa mijin ki biyayya har kika bari yana dukan ki haka kamar wata mara gata eyeh.
Kuka yaki tsaya min nace yaya bana mashi komai haka dai ya daukan wa ran shi yai ta dukana do ban da daraja a idon shi.
Don kawai yana ikirarin da cewa bashi ni akayi ya tare ni da cewa a haba kibar fadin haka mana ke fa kaunar shine ko banza.
Yadai bani hakkuri ya lalashe ni da kuma nasiha har zuciya na tayi sanyi da zai tafi ya kawo duba goma ya ce na rike a hannuna zan samu na kashi.
Nai mai godiya ya taka har kofan dakin shi yana fadin bros ni zan tafi sai na saike lekowa kenan sai ya amsa mashi daga ciki da yaushe zaka koma.
Yace ina nan har kwana biyu sai yace sai mun hadu ke nan ya saadin yace don Allah aita hakuri yace is ok ai.
Ina shiga daki na raba kudin da yaya Saadu ya bani biyu na boye rabi kamar nasan zai karba sai ko gashi ya shigo yana ce min .
Ke bani kudin da saadu ya baki nan ashe wurin rabawa ban raba daidai ba bakwai din na boye na bashi ukun sai ya kalla yai tsaki yace munafuka kawai.
Ya fice gidan na harare shi ina cewa a fili mugu kawai ashe baiyi nisa ba ya juyo yana fadin may kika ce nace ni badakai nakeyi ba.
Yafice yana kutawa tare da gaura kofar gidan da karfi na sauke ajiyan zuciya ina mai kallon jikina inda na ji ciwo tare da dan tabawa.
Fitowa nayi na kara gyara wurin da ya bata nagama nai wanka na gyara jikina ina shirin dan kwatawa na mike naji nocking din kofan gida.
Na fito don ina ga kowa nene akofan sai ganin yarinyar aikin gwago da tai alkawarin zuwa kitso wurina a kofan nai mata sanu da zuwa tare da sake mata fuska tashigo ciki.
Baya mun gaisa da itane take cewa dani kitso tazo in mata na ji dadin koba komai zandan sake yau a gidan a wurin ta nike jin wasu halaiyan shi da ban sani ba da farko take cewa amma ke ba yar uwar su hajiya bane.
Nace may kika gani tace gani nayi dai bata kaunar ki koda yake hajiya ai da kowa zata kwasa indan ya taba mata dan lelenta.
Murmushi nayi mata kawai tace tana masifan son shi cikin yaran ta gashi dai yana aiki kuma yana samu amma bata jin kyashin kashe mai kudi.
Nace aidon su take nema ko tace wallahi yana da hanyan samu sosai amma yan matan shi basu bari ko wanan gidan da mota da ya saya sai da dabara ya saye su.
Na dauka da yai aure zai daina amma da yake dan duniya sai abin da yai gaba ga abinda yake yi.
Nan nake ji wai ai da dawata yake zaune a gidan sai da hajiyan tayi da kyat ta raba su da kamar sun rabu yanzu kuma sun dawo sun dinke wuri guda da ita.
Nan tashiga bani hiran abokiyar shashan shi din da irin rayuwan da sukayi a baya dama wanda suke yi yanzu din har nagama mata kitsa tana min hiran shi ne.
Mun gama ta ciro kudi ta bani ban karba nace ta barshi sai idan ta sake dawowa tace a, a karba wallahi idan kika soma da haka zakita aikin banzane wa mutane nan garin neman kudine ba a wasa da neman kudi.
Naimata godiya taimin alkwarin zata sake dawo idan an kwana biyu na rakata ta tafi sai da ta wuce na duba kudin nayi mamaki don har dubu daya tabani.
Ina ta murna na shiga daki naje hadawa da wanda na boye sai naga ashe dubu uku na bashi na boye bakwai.
Yanzu ga shi taban daya sun tashi takwas taban shawara na sayo kayan yin kitso don akwai wa yanda zata turo min.
Tun ranan da tazo kamar ta buda min hanyane na yin kitson na dinga samun customers mssu zuwa ganin haka ina yi a boye sai na sheda mashi don karya zo ya sani ya hauni da jidali.
Baice komai ba sai ke kika sani kardai ki bata min gidana kan wani kitso naki na banza can.
Don haka idan sun zo muke fita ta waje muyi kitson basai mace ta shigo gidana ba mun bata mai gida.
Wata rana wata mace tazo da diyan ta sai suna neman ruwa sai da aka tafi wani gu aka sayo mata sai take ban shawara na dinga saida abin sanyi mana.
Wanan shawaran yai min dadi sosai tun wanan ranan na fara sayar da ruwa sai nai shawaran ko na dinga zobo sai inayi dashi da wasu yan kakanan drinks ina sayar wa.
Aiko sai abin ya karbe ni matan hausawa harda kumshi nake masu mai zane take sunana ya fara dagawa.
Hankalina ya dan fara kwantawa koba komai dai ina samun abokan hira har ina dariya sai dai in sun tafi na koma dip.
Wata rana na gama kitso na gyara gida na dora girki gap da zan gama na shiga wanka koda nafito abinci yayi na kwashe.
Ina zaune a falo ina cin abinci sai gashi ya shigo ina gaida shi da dawowa ya amsa ciki ciki ya wuce dakin shi.
Ya fito ya zauna kenan wayan shi yai kara ya dauka zaune nake a takure a falon ina gudun in daga yace min munafuka.
Sai na dake na zauna a takure a yadda na fahinci wayan da yake da mace yake magana amma ko yaji darr dan ina zaune a wurin.
Daji lalashinta yake yi don a yadda suke magana hakkuri yake bata ita kuma sai masifa take mai a wayan.
Zuwa can ya mike zai fita sai na sasauta murya na nake cewa kayan miya sun kare a gidan na gobe ya rage kawai da zanyi.
Ya juyo a wullakance ya dube ni yana cewa ina kudin da kike samu a wurin kitson naki ki fitar ki saya mana.
Ya fice ya barni ina mai binshi da kallon mamaki don tunda kayan da nazo gidan na sama ya kare idan nai mashi magana sai ya hauni da fada.
Gashi kuma ance kudi yake samu sosai a wurin aikin shi amma baya nuna yana dashi sai yaga dama yayi.
Nidai na fahinci anyi sallah na mike zuwa yin sallah nabar falon ban fito ba ina shirin kwaciya ne naji dawo wan shi gidan.
Na dan tsaya inga da may ya dawo min a cikin mayen ne ko a birkice naji shigowan shi na mike na fito falon inda yake sai naga yana shigowa yana dariya.
A zatona waya yake yi sai naga ashe ba waya bane yana magana ne da wata da suka shigo gidan tare.
Yana dago kai ya ganin ya hade fuska tare da cewa a fusace ke kuma may kikeyi anan baki kwanta ba ?
Yarinyar da suka shigo da ita gidan tana wani taunan chewgun kas kas tana harare hararen ko ina na gidan.
Naji tace wanan ne dama matar taka ashe karamar yarinyace haka no warder kake gudun mutane yanzu
Ta kalle ni sama da kasa sai tace dashi muje don Allah karma ta kwanta mana ita ta sani tai gaba ya juya ya bita a baya.
Suka barni tsaye a wurin imani ya kashe ni may yake nufi kenan karuwa ya dauko min a gidan ko may ?
Jin sun rufo kofan daki ne nadan zabura na dawo cikin hankalina dakyat naja kafana na koma daki.
Tunane nakeyi wanan wani irin bariki ne haka karuwa har cikin gidan tazo ta wuce ni ta shige daki ita da mijina ina tsaye.
Da kyat naga safe don banyi barcin kirkiba a gidan da safe ban fitoba don haka ban dora girki ba a gida ko gyaran gida ban fito nayi ba.
Sai zuwa can ya kwala min kira daga falo saida ya kirani sau uku na amsa mai na fito falon ina saye da hijjab dina har kasa.
Ya kalle ni a wullakance yace dani ina abin karyawan mu banga kin aje min ba nace a sanyaye banyi ba.
What ya fadi da karfi nace banyi na sake fada mai saboda may zaki ce baki dafa min abinda zanci ba.
Cikin dakewa nace ita wanda ta kwana gidan bata dafa maka bane koba mace bace da baza ta dafa ma ba.
Ban san ya iso inda nake tsaye ba sai ji nayi ya buge min baki kub da nashi basan lokacin da na dafe wurin ba.
Ya daga hannu zai kara kai min wani marin sai ga ta ta fito daure da tawul a jikin ta iya cinya tace a, a marta koma ta dafa ba iya ci zanyi ba wanan kazaman yarinyar ba zan iya cin girkin ta ba.
Ta jashi zuwa cikin daki tana wani kariraya tana kwanta mai ajiki suka rufe kofa dakin garam ina wurin a tsaye.
Na sauke ajiyan zuciya a raina nace lalle yau na ga iyakar barikin da nake ji ana fada anayi a lagos na ganshi a wurin wanan bawa shine giya shine taba gashi kuma ya buga ga dauko karuwa kwana a gidan mu na sunna.
Ina jin sun gama watse war su suka fice a gidan da ihuce ihucen su da tafawa a tsakanin su.
Nace shashu banza kawai a haka zaka kare ba aga farar ka a gida ba sai gun matan bazan za suna fita sai ga yaya saadu ya shigo gida.
Natare shi da mutunci muka gaisa dashi yake tambaya na yaya gidan na amsa mai da lafiya kalau.
Sai yake tambaya na yanzu abubuwa sun yi sauki a tsakanin mu ko sai nai murmushi kawai nake cewa dashi babu komai yaya.
Ya ce a, a Safiya kada ki biye min komai ni dan uwanki ne nasan kuma halin mijin ki sarai da rashin mutunci do haka in baki fada min ba wa zaki fadawa.
Sai idanuwa na suka ciko da hawaye a lokaci guda nace yaya komai na nan a yadda ka san shi saima abinda ya karu.
Yau ma da wata mace suka kwana gidan a gaban ta yai min rashin mutunci don naki dafa masu abin karyawa.
Hakkuri ya bani ya dade yana mun na siha ina ta fada mai irin matsalolin da muke samu dashi a gidan.
Yana bani hakkuri tare da fadin sai na hada dayi mashi addua don addua baibar komai ba in kuma yi kokari in kawar da idona ga abin da yake yin don ko na ce zan fada wa iyayyen mu ba yarda zasuyi da ni ba.
Da zai tafi yakawo kudi ya bani yana cewa na rika in dinga sayen abinda zanci basai na tambaye shiba kar yaita duka na a banza.
Nace mai akwai kudi wanda na tara do yanzu kitso nake ina samun kudi yace tona kara kawai dasu.
Yai min alkawarin zai saya min fridge don sana,an zobon da nakeyi ya bunkasa sosai naji dadi ina ta zuba mai godiya mukai sallama ya wace.
Da ya tafi na kirga kudin sai naga har sha biyar ne cif din su banyi sanyi a kafa ba na shirya na shiga yar kasuwar uguwar mu na sai kayan amfani na dasu da abinda zan dan rika ci da rana.
Ashe da yabar gidan gidan su ya koma wurin mahaifiyar su ya ke fada mata duk irin abubuwan da dan uwan nashi yake min.
Sai ko ta hau fada da cewa dama tsiyan dan tallaka keman bai iya samun wuri ba ta tsamoni cikin wahala tasani ga rigan mutunci ina bidan in tona masu asiri.
Da nake cewa yana sha, shan ya hana ya kyautata min ne duka kuma in banyi mashi laifi ba ai ba zai duke ni ba , a gidan mu wani irin wahala ne bana sha nazo nan a saka ni cikin rigar mutunci shi zai ma danta sheri.
Yace mummy yarinya ga fa diyan dan uwanki ne halal malan aka dauka aka baki badon taso ba ko uwar ta taso ai kama yayi ki tsawata mashi yadaina shigo mata da maye da matan banza baki goyi bayan shi ba haka.
In tana ahan wuya a gidan su nan ai aurene ya kawo ta kamata yayi ta samu sayin rawa ta huta ba wahala irin haka ba.
Tace to ubana dama ai ka saba min fada sai kayi ita kuma ta zuba ruwa a kasa tasha tunda ta hada ni da diyana fada.
Sadiya dake gefe tana saurare tace mummy ai gaskiya yaya ya fada gaskiya abinda yayan ke wa Safiya baya kyautawa idan mu akaiwa haka bafa zaki ji dadi ba.
Harara ta watsawa Sadiya din tana cewa ai duk kuna da bakuson dan uwan ku da alheri daga yarinya taimai kake kun dauka kun haye ke nan kun yarda da abinda ta fada.
Saadun yace mainene daga ciki kake wanda ba halinsa ba cikin abinda ta fada din ina duk halin da ta fada kin sani yana yin su sarai.
Nan dai yaran suka barta tana ta fada tana fadin ai zata je gidan zamu hadu gobe bazan kara fadawa wani sirin mijina ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button