BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGO, , , , , , , ,
???????? 1️⃣4️⃣ ????????
YAR UWA WANAN NOVEL NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,
Tafiyan dare mukayi sai wajajen sha daya da wani abu na rana muka isa garin mu duk jikin yai min tsami dama yaya jikin yake balle an tabashi kuma.
Mun sauka yaya ya nema muna mashin muka hau zuwa gidan mu tare da kaya na niki niki shi yai wahalan daukan kayan da kansa.
Suna hada hadan su na safe sai jin sallama na kawai sukayi yara suka dauka ga Safiya ga safiya tazo.
Da gudu kanena suka sheko suka rungumay ni suko su mama sun fito da mamaki suna kallona mama ne tace safiya kuna tafe ashe ke daya ne take sai idanuwa suka ciko da kwalla.
Na shige dakin mu ina kuka shigowan yaya Sani da kayana niki niki ya na kokuwa dashi yasa aka samu masu taimaka mashi daukowa.
Kowa sai mamaki yakeyi sunyi tsaye cirko cirko suna mamaki Inna tace babu lafiya kan gaskiya.
Wanan tafiya da gani bana dadin rai bane sai aka fara lekowa don gulma wai ana gaishe ni da zuwa sai a fita ana dariya waje don sheri.
Inna ta koma kan yaya sani wanda ya gama aje kaya a wahalce dashi ta tsare shi da idanuwan ta tana cewa daga ina ka tsinto Safiya kai kuma.
Baiyi magana ba sai samun wuri da yayi ya zauna yana neman ruwan sha yana jin inna ta matsa tambayan shi saida ya gama kwakwadan ruwan shi ya sauke numfashi.
Ya dago kan shi yana fadan can lagos mana inna sai ya mayar da kan shi a kwanon da yake shan ruwan.
Cikin mamaki da dafe kirjin ta tace har lagos katafi ka dauko ta dakin mijin ta kana ko da hankali kuwa.
Sunyi tsaye akanshi cirko cirko suna sauraren shi maimakon ya yi magana sai ya mike kawai ya fita daga gida batare da ya tankasu ba.
Can waje ya samu yan uwanshi su yaya Nura yana basu labarin rashin mutuncinn da ya samu mijin nawakeyi don haka ya hade kan su akan suyi wa baba tawaye ga zancen.
Don gulma baba har ya fita kasuwa sai inna ta tura yaro ya kirashi a kasuwan don tasan bazasu ji komai a wurin yaya Sani din ba.
Tun shiga na dakin ummi kuka nake yi ban iya magana ba har da ruwa da kunun da ta aje mun ban iya shan ko daya ba a ciki.
Kanina ta tura ya kira mata gwagonta da sauri a gidan su don tasan ba lafiya ba wanan zuwan nawa kan.
Ta fita ta kira su mama da inna kafin gwago din ta zo nan suka sakani gaba da tambaya amma basu samu amsa komai ba ban da aukin kuka da nakeyi.
Gwago ta taso hankali a tashe tazo gidan namu cikin tashin hankali da son ganina kamar karta shigo na kara sautin kuka na ina fadin ban komawa wallahi gwago kasheni zai yi kinga duka,
Na shiga bude jikina ina nuna mashu ga tabo nan ko ina a jikin nawa ba iya ka take ummina ta fashe da kuka inna ne kawai batai kuka a wurin .
Sai ga baba da yaron da ya tafi kiranshi sun dawo tun a kofan yake fadin ina Safiyan take ne lafiya ko tare suke da mijin nata
Nan take gidan yai tsi kowa na sauraren abinda zai fito bakin na amma sai kara sautin kuka na da nakeyi kawai.
Tsawa ya dakamin tare da tambaya na dacewa ke ki ba mutane amsa kin tsaya sai kuka kike zubawa mutane, kukan ne zai fishe ki.
Daga kofa suka tsinkayo muryan yaya Nura da yaya sani suna cewa baba mijin nan ta dan iska ne wallahi da ce anan arewa yake zaune ba abinda zai hana mu casa shi wallahi.
Baba ya daka may tsawa da kai rufe muna baki don Allah yanzun dai may ya kawo nan a wani dalili tazo .
Yaya Sani ya karbe zance cikin dakewa yace a dalili na tazo don ni naje har lagos na dauko ta na zo da ita gida kar ya kashe ta ga banza kar mara galihu da gata .
Wani kallo baba yake mashi ya ci gaba da cewa diba baba ka gani yadda duka ya mayar da yariyan ga duk ta koma kamar wata ta baba wallahi.
Baba ya daka mai tsawa da kai dakata kaina ubanta ko kaine uwar ta ya girgiza kai alaman a a baba yace to kada hurumin dauko ta ka dawo gida ita .
Baba ta yaya zanje na samu yana dukanta da zagi akan taki dafa masu abinci shida karuwan shi ya doke ta yana zagi na fitan arziki.
Ina ruwan ka baba ya firfito da indo waje ya sake cewa nace ina na ruwan ka wa ya aike ka zuwa dauko ta idan ya ga dama ya kashe ta mana ai mijinta ne kuma dan uwantw.
Gwagon Ummi tace a a malam wanan ba hujja bane gaskiya kace fa ya kashe idan yaga dama da yar uwar shi ce aiba zai mata wanan tsinanen duka haka ba.
Baba yace cikin daure fuskan karki saka bakinki ga zancen nan don ba maganan ki bace diya dai diyatace kuma dan yar uwana na bawa ita.
Don haka ko yanka ta yake yi gunduwa gunduwa sai ta koma gidan nan shidin da yaje ya dauko ta shi zai mai da ita dakin ta ta zauna ai kowa hakkuri yake a dakin shi.
Mama tace bako da duka ba har da su tarmashe da sauran su sai dai wani abin kadai tsaya ai bincike kada a dauki yarinya a mayar wani abu yaje ya samay ta ta halaka fa.
Baba ya amshe zancen nata da cewa idan ta halaka aure ya halaka ta nace aure ya halakata sai ummi na ta fashe da kukan bakin ciki yace sai kiyi amma komawa sai ta koma wanan gidan ba fashi .
Ya juya ya fice gidan da banbami shiko yaya sani fadi yake yi ba inda zan tafi wallahi abar shi yaje ya kashe ta din ba shike nan ba ai yar shi ne yace.
Wanan kalamai na yaya sani suka tayar min da hankali ina ihu ina fadin yaya Sani kataimake ni bana komawa gidan nan kashe ni zaiyi wallahi.
* * *
A can lagos din bayan tafiya na bai tafi gidan su ba har tsawon kwana biyar yana hadiyan bacin rai shi kadai.
Da farko ya dauka wasa ne yana cewa in tafi mana ya huta da wahala da yar kauye maganganu dai na batacin yake fada gamay da ni din.
Sai yazo ina dan ya dawo zaiga gidan yai mashi girma ga wani irin duhu ba gyara shi kuma bashi da time din zama yai gyaran.
Don haka ya bugo waya gidan su kannen shi suje su gyara mai gida basu so zuwa ba suka tafi dole.
Sun dawo suna kwarara amai da zubar da miyau na kazantan da suka gani a gidan amai ne ragowan giya ne kai komai sun gani a gidan.
Suna fadawa uwar su kan cewa basu kara zuwa gyara mai gida sai ta hausu da fada inda take shiga ba nan take fita ba.
Idan ya rasa kudi babu mai bashi yadda yake samu ya amshe dan kudin da nake samu ga maman biyu ko wurin kitso.
Yanzu babu inda yake samu sai dai ya arro ko kuma asai mai giyan kyata don mashaya akwai su da wanan kara.
Sai ya kara sanin ashe ba karamin karya nake mashi a gidan ba gaskiya ne da aka ce mutum dan adam yana da rana.
Ga yariyar da ya raina yaga ranan ta tun ba, aje ko ina ba gashi yasan muhinmacina a gidan yasan ina hakkuri dashi to amma kuma shidin ya kasa kyautata min ne bai san dalili ba.
Ina da matukar mahinmaci sai yanzu da ban gidan ya gane hakan duk da bakwa yake dani ba sai ya ga dama amma sai tafiya ya zamay mashi yashin hankali da rashin kwaciyan hankali , ya rasa may ke kawo mai jin yawan tsana na a rashi.
Kodon yawan zagina da mahaifiyan shi keyi ne a gaban take fadin kwadayin mahaifina ya jawo min haka yana gani ita sakarai ne don kawai ya bata diya sai ta bude mashi bakin aljihun ta na kashe mai kudin ta, ba dai a kan wanan diyar tashi ba dai.
Wani yammaci sai gashi yazo gidan su dayamma nan mahaifiyar ta tare shi da zance na tana zagi tana aibanta ni tare da zagin iyayye na kamar yadda ta saba yi idan yazo.
Yai shiru yana sauraren ta sai can da abin ya isheshi yace mummy zuwa zakiyi fa, ki dawo da ita don ba zan sake taba .
Uwar dago cikin mamaki tace haka zaka ce ni ina ganin bata dace da kai ba sam,
Yace mummy idan ba ita ba da iyayyen ta wata mace ne zatai hakkuri damu gaba daya duk abinda muke mata tana zaune tana hakkuri sai zuwan dan uwata ya gudu da ita.
Ke kanki kin san cewa indan yar ki akewa hakan bazaki taba lamunta haka ba .
Don haka ki kama hanya zuwa arewa ki dauko ta kidawo da ita nan shine saukin mu bai kamata ace don ki aka dauki yarinya nan aka bani ita.
Don kwai ina danki ace baki kaunan ta ai gaskiya saadu ne da yake fadi da taimakon ki muke wani abin.
Duk ke ke kara lalatamu muke abin da muka ga dama abin da bai dace ba idan munyi sai baki iya hana mu , sai muga cewa shine daidai don bamu da masu yi muna fada a rayuwan mu.
Shi wanan tsohon ya na shagamu can yake sha a nin shi bai damu ba da halin da muke ciki a garin na babu ci babu shan shi.
Nan dai ya takewa uwa gidan wuta akan sai taje ta dawo mashi da matar shi ya zube mata kudin mota anan ya fice yabarta tana tunane akai.
Yaushe yaran nan ya fara son Safiya hakan nan ban sani ba kodai shima sun magance shine yadda suka magance yaya a gidan shi.
Yanzi ni idan naje da wani ido zan kalli mahaifin yarinya nan dashi nace na rike mai ya amana ko mai.