BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

* * *
Acan gida bayan baba ya kare fadan shi ya kare da cewa zai hada kudin mota da zaran sun cika bani kara kwana mashi gidan shi.
Bayan fitan shi ne gwagon ummi ta rarashe ni da mama na samu na danci abinci da aka aje mun sai dai ban iya cin komai ba ruwan kunu kawai na iya sha.
Dana dan gyagije namike naje nai wanka na fito har lokacin gwago tana nan zaune na sa kaya a jikina,
Sai lokacin na fara ciro masu tsaraban da nazo dashi da wanda na sara ina gwadawa mahaifiya ta nan dai muka cire ma kowa tsaraban shi.
Na fitar wa aka fitar ana tallata min ne diban ma maman Amina kawata aka kai mata take tambayan nazo ne yaron ke fada mata cewa nazo tun jiya ina nan gidan mu.
Nan da nan aka saye kayan don na sake su da sauki sai gulma ya fara tashi a gidan mu daga dakin inna suke fadin ai gwai dama sun san cewa yaran gwago ba su da kamun kai.
Sundai yi shiru ne naje na dan dano ai maganin mu kenan uwa cikin ukuba diya ma haka ai kadan muka gani.
Na dan samu sukuni don har na fara maida jikina da haske naje na gaida maman Amina kawata mun dade muna hira da ita na dawo gida kada baba ya dawo bai samay ni a gida ba don satan hanya nayi nazo gidan su.
Wai duk da halin da nadawo gidan mu ciki Inna sai da tai bakin ciki da gani na haka na kodan dan kayan da na saro ne ake saida min ban sani ba.
Wani lokaci taimin gori akan rashin dace miji wana sain kuma ai min habaici wai ina wa mutane takama natafi birni na waye.
Don dan kayan da nake sai daiwa yasa mutane na ribibin zuwa sayan unders na yara da yan dogon riga na mata nashan iska da sauran tarkace.
Shine dalilin da inna ta rasa sukuni a cikin zuciyar ta tace wai ai gara na koma akarasa ni can ko yaushe cikin ba babana mugun shawara take a gida.
Ina da sati uku da zuwa gida ne safiyan wata asabar sai ga gwago ta sauka a garin direct gidan mu ta yo sun tare ta kamar yadda suka saba mata idan tazo har da ummi na bata nuna mata komai ba a zuciyar ta.
Hakan yasa gwagon dan sake jiki bayan sun gama gaisawa da mama sai gwago tace dada wanan yaron haka yaje yai muna, ya dauko kaunan shi ya zoda ita gida bada sanin mu ba.
Sai mama din tai murmushi tace muma haka dai muka gansu kwatsan a gari sai dai a gaskiya abin baiyi dadi yadda suka zo muna da labari .
Anyi abu don dadin rai kuma sai abu nason ya koma tsiya haka don ma malam daya tare maganan ya hana kowa ya fadi yace yana tara kudin mota ne , ta koma dakin ta.
Gwago taji sanyi a ranta sai dai taji mama tace a gaskiya dake har wanan yaron baku rike amana ba sam abin baiyi dadi ba wallahi don ma dai anyi kawaici andubi baya .
Gwago tace to ai dada yanzu dai kuyi hakkuri kamai aka ce munyi mun dauka sai dai muba da hakkuri kawai.
Mama ta sake cewa ki sani diyar malam diyar ki ce ba sai an fada ba don in anyi laakari da irin diyaucin da ya nuna tun daga kan auren har kawo yanzu amma sai ga labari mara dadin ji ya samay mu kuma mun ga alama don ga shedan bugu nan da tazo muna.
Yadda duk akeyi mama tayi don ta fadi gaskiya yadda ya dace har da zancen kudin da suka bar ma gwago ta ja min jari sukayi tace wai mijina ya karbi kudin
Amma zatai mai magana ya dawo min da kudina na dinga juyawa da kaina zaifi tana ta ban hakkuri can dai ta tashi zuwa dakin mama ne tayo mata rakiya wurin ummina.
Nan ma hakkuri ta bayar suna cikin dakin ne baba ya shigo gidan wanda inna ta aika a kira shi yazo wai ga gwago tazo.
Yana shigowa yai dakin mama aka ce suna dakin ummi sai ya kama fada yin may ina ruwan ta da ita aiba ita taba ki dayin ba.
Nan dai yake ta sababi irin na maza da iyalin su basu da tacewa sai su kaida ke kafa dokan su a gidan yadda ransu yaso.
Bai tsaya sauren ta ba yace binta kinzo dama ina son zuwa wani sati in mayar maki da yarinyanan .
Sai hakkuri yake bata abin ya bani mamaki naidai tuna yadda take zama ta kare mashi zagi da yankar kauna .
Amma shi yana nufanta da alheri ya kuma bata go ahead akaina yace tana da iko akaina ta tsawa ta min ba sai nazo gida ba.
Hannu na sa akai ina ihu baba yace indan ban rufe masu baki ba yanzu zai debe min albarka dole mama tasani yin shiru mama tana fadin adai tsaya abin abin a sannu ba a hakana,
Tsawa ya daka ma mama tare da cewa indan bata kama mashi baki ba yanzu zai da ita dani mu bar mashi gidan shi.
Duk yadda akeyi mama tayi amma ita inna cewa tayi indan ma na zauna gidan may zan yi ai kawai gara na koma daki na, na zauna shiyafi.
Baba ka taimake ni karka mayar dani idan ka mayar dani kashe ni zasuyi wallahi wayyo baba ka taimake ni yace idan ban isa gare ki ba sai dai kibi duniya.
Ummi na saboda kawai ci kala bata ce dashi ba amma zuciyar ta kamar zai tsage take jin shi ansa rana, ranan labara zamu tafi.
Don gwago zatai dan sayayya da zata tafi dashi na sana an ta can sai wani nan nan dani takeyi don ganin idon mahaifana.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,

????????1️⃣3️⃣????????

IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON WANAN NOVEL DIN KUDI NE.

Ummina dake barci ta falka cikin matsanacin firgici daga barcin da takeyi wanda kwana uku kenan a jare ta mafalki dani.
Kuma mafalki mara dadin takeyi a gamay dani din wani lokaci sai taga na gwauce zan fada rami ko tagan ni a ruwa mai zurfi ina iyo.
Ina gudu ana bina zaa kashe ni da wani guduma a hannun mai shi ire iren wanan mafalkin takeyi koda yaushe hakan ya tayar mata da hankali.
Ta shiga cikin damuwa sosai ta dan saka abin a ranta don haka yau ta kudiri aniyar fadawa baba na idan ya dawo dakin ta.
Haka akayi sai da yagama sauren ta kaf yaji abinda take fada bai bari takai aya ga zancen ta ba ya ko hauta da sababi har yana daga murya sauran mutanen gidan suna jin shi.
Mama ce da taji fadan yayi yawa hakana ta tako zuwa kofan dakin tana cewa haba malam ayi hakkuri koma may nene tunda ka taba fada ai ya isa ko.
Yace a hasale bari matar nan da abin haushi auren yariyar take son kashe wa don rashin sanin ciwon kai.
Yariya na gidan mijin ta zaune lafiya hankali kwance zaki tsiro da wani tsurku wai kila ba lafiya take ba ke kina yawan mafalkin ta ke kila wani abu zai samu yar ki.
To Wallahi ahir din ki da zancen Safiya a gidan nan idan ba haka ba rayuka zasu baci sosai akan haka don sam ba zan lamunta ba.
Har yayi ya kare bata ce dashi uffan ba da safiya kuma ya tusa jidali inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Sai inna ce ta sa mashi baki tana fadin ai kasan dan tallaka bai iya samun wuri ba in bashi ba abin farin ciki yar ki na can lagas tana aure amma ke bakin ciki ya hanaki ki gane haka ki kwantar da kai kici arziki.
Mutum mai bakin ciki da hassada ai har kanshi yake yi saboda mugun hassada daya huda jiki na sheri, har taci ta sude ummi bata tankasu ba sai share su da tayi tana aikin ta a cikin gida.
Kwana biyu hakana suke da baba sama sama sai da taga ya dan fara mantawa da zance ta roki fita unguwa gidan gwagon ta.
Bai hana ta ba illa cewa da yayi a gaishe ta ta gama abinda takeyi ta shirya ta tafi gidan nasu kamar yadda muke kiran gidan gwagon nasu.
Bayan sun gaisa da gwago tana tambayan ta yara da sauran muta ne gidan take cewa gwago dama nazo in fada maki ne kwanan duk na kwanta barci farkin yar nan nake yi ba dadi wallahi.
Nan de ta kwashe yadda take mafalkin ta fada ma ta shiru gwagon nata tayi sai zuwa can tace wuri ne bakusa ba in ba haka ba da sai a shirya aje a gane ta.
Sai dai addua duk inda take Allah ya tsare muna ita kawai zamuce wanan shawara na gwago ta dauka har tadan ji saukin abinda take ji gamay da ni a zuciyar ta.
A hanya tana dawowa tafe take tana tunanen ko a wani hali nake sai Allah kawai ya sani don yanzu kusan shekara daya ke nan da tafiya na amma babu wanda ke da labarin halin da nake ciki.
Yaya sani zaune yake gaishe ta amma bataji shi ba har sau uku yana mata magana tayi nisa a cikin tunane.
Sai da ya kara kiran sunanta da karfi taji shi ta sauke wani ajiyan zuciya da karfi take amsa mashi gaisuwan da yake mata din.
Yake tambayan ta lafiya dai na ganki a cikin damuwa tai murmushi kamar kada ta fada mai sai take cewa babu komai.
Yace wani matsalane kuma ya taso ki fada min, sai ta fara haye take fada mai yawan ma falkin da take yi dani ta kara da fadin gashi tun tafiyan ta babu wanda ya ji labarin su itama gwagon naku ta bar zuwa yanzu kamar da datake zuwa akai akai.
Shiru yayi yana tunane sai can yace lafiya take ummi mafalkine kawai ke zuwa haka na amma bari nayi maki alkwarin zan bincika inji.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button