BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , , ,

????????1️⃣5️⃣????????

YAR UWA WANAN NOVEL NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , , ,

Kamar yadda baba yace haka din ne ya faru gwago ta daukeni zuwa lagos ita kadai kamar mara gata ta, tafi dani.
Mama ta ance an samu wacce ta raka ni muka tafi tare amma sam baba yaki yarda da hakan yace wai ai gwago uwata kuma gwago na.
Su yaya sani sun so siyi ma baba dan banga banga amma yaki yarda yai masu tijaran tsakar gida.
Wanan abin shiya tunzura ummina tabar gidan baba yan uwanta kuma suka kama mata suna cewa su dai basu ga amfanin auren da babu yanci cikin sa ba.
Da farko baba bai damu da tafiyan ta ba sai daga baya ya damu a kan yara don yanzu dole ya bada komai na anfanin su.
Wanan abin ne ya fara damun shi taje bikon ummi mahaifinta yace badai gida shi ba yaje yayi iko da yar shi shi kuma yai iko da tashi don da baifi daba amma ummi ta gama auren gidan shi.
Ya dauka wasane sai da yaga yannen ta sun kaishi kara kotu akan ya bata takardan sakin ta yasan da gaske suke wanan karon.
Aka shiga kotu suka kora wa alkali halin da yake mata da rashin bata yancin ta alkali yace zai daure shi don sai ya fadi gaskiya indan ba sayar dani yayi ga gwago na ba yake kamay kamay.
Yai ta rantsuwa akan wallahi bai sayar dani ba zumunci dai ne tsakanin shi da gwago na Alkali yace zumuncin zamanin nan zakai wa haka.
Daga Allah ya taimake ka yar ka ta dawo gida wurin ka lafiya ba tare da wata matsala mai karfi ba don rashin sanin zafin kai zaka maida ta gidan wahala watau taje a kashe ta da kurciyan ta ko.
Yace ba haka na bane alkali yace haka ne mana sai ta zama mara anfamni zaka dawo uwar ta da ita ko yana dai ta bada hakkuri alkali yace ya basu sati biyu su shirya in ba shiri tazo ta karbi takardan ta.
Da haka suka wuce aka rabu baran baran baba hankalin shi yai matukar tashi mama tace na fada maka kabi abin nan sannu kaki .
Safiya ba irin sauran yara bane yarinya ne mai biyayya da sanin ya kama ta amma har kaga ta kasa hakkuri a wanan halin ta akwai magana da anyi bincike tare da kafa hujja mai kar fi.
Amma kaki tsayawa ai komai a hankali ka dauki yarinya kamayar da ita ba wani binciki kwakwara yanzu duk abin da ya faru da ita sai ka kuka da kan ka.
Nan suka taru da shi da Inna suka mai mama caa a kai wai tana dai su agoya mani baya ne in kashe aure yasa take fadan haka amma wani wahala nake ciki.
Nan dai itama tai masu nasu borin ta ce aidon ba diyar Inna bane a wanan halin da duk gari kowa ya gama jin wanan zancen ko.

* * *
Daga ni sai gwago da wasu mutane a bayan babban motar traller da zasu kai kaya kurmi don son mallaha ta kasa biya muna dubu hudu zuwa lagos.
Ina rakube a wuri daya a cikin mota duk inda mota ta tsaya sai ta sai abin kwalam taci bata ko kallona ni ko ta bani baya gama na ina tunanen halin da na baro ummi na ciki.
Sai wani awara data saye tun a arewa taci ta raga yai tsami ta jehomani kaina girgiza mata alamar a a bana ci har muka kai sai ruwa da nasha ina da muka sauka mukai sallah.
Anan na kulla ko sallah ba bata yi daidai irin sallah yan kasuwan kauye ne a gagauce ake yin sa ba cikawa.
Mun sauka lagos da dayan rana don motar bata sauri maimakon mu tafi gidan ta ta hada mu tai muns fada sai kawai tace a kaimu gida na bata ko shiga ba ta saukemin kayana tana ta masifa wai ban da kama jiki.
Ni dai na fita suka ja mota suka tafi suka barni nan tsaye ina mamakin ta a raina sai da motar ta bace na juyo ina kallon gida tare da sauke ajiyan zuciya na fara takawa zuciya na fal da mamaki gwago da alaman sam bata da digon amana a rayuwan ta.
A hankali na tura kofan gidan ga mamakina sai naga gidan a bude na shiga da addua na ga baki da alama akwai mutum gidan.
Warin taba da tsamin giya ne sukai min maraba ga hanci na take wani irin bakin ciki ya lulube ni na rintse idanuwa na don takai ci.
Dakina na nufa da buhun kayana ina ja don ba zan iya dauka ba don nauyi saboda nayo yan sare sare a arewa na je da shi.
Dakin yana nan kamar yadda na barshi babu sauyin komai a cikin sai dai kuran da yayi kawai na rashin mutum a cikin sa.
Zama nayi nai tagumi hannu bibiyu idanuwa na suna fitar da hawaye takaici don gwago takai katuntumar yar cin amna.
Koda yake bata da laifi duk wullancin da na gani mahaifina ne ya ja min shi don jajircewa shi a kan gwago wai shi zumunci .
Ina ga motsi suka ji ya fito kofan gidan a bude yake sai kuma ya kalli kofan dakina shima a bude yake dakin.
Da sauri ya tako zuwa kofa ya daga labulen dakin ina zaune shabe shabe sai hawayen da nake zubarwa a idanuwa na.
Kamar daga sama naji shigowan shi dakin babu annuri fuskanshi ko kadan sai dai ya dan nuna mamakin gani na a wanan lokacin.
A take na razana yayin da nai kwali dashi tsaye kofan dakin ya rike labulen dakin.
Fara takowa yayi zuwa inda nake zaune gabana ya fara faduwa da tsoro yazo daidai kaina ya tsaya na cewa.
Ciki buga tsawa yace dani tun yaushe kika dawo gidan nan ban sani ba yana ma dakin yan dube dube can ya juyo ya tsare ni da idanuwan shin jajjaye.
Ya sake maimata tambayan shi gare ni da yaushe kika dawo nace ?
Na dan kalle shi nace yanzun gwago ta sauke ni ta wuce sai ya watso min mugun kallo kamar zai make ni, yace waye ya baki izzinin wucewa garin ku.
Ban bashi amsa ba sai ma kawar da kai danayi daga kallon shi don wani irin tsanan shi nake ji da haushi yana shigata da zaran na ganshi.
Ya harare ni yana cewa wanan ya zama maki na farko da na karshe a gidan nan don ba zaki maishe ni yaro ba .
Banko san yana tsaye ba haushi da takaici sun cikani na shi caraf na jiyo muryan mace na magana daga falo ya juya da sauri ya fita zuwa falon .
Daidai wanan lokacin naja tsaki tare da fadin ai guma yaro da halin ka Allah dai ya sauwa ka gashi dai mutum a ido amma a ina halin shi na kamala baikai ba.
Can naji sun fice daga gidan na fito na kalli gidan a kazance da kyama hawaye ya zobo min na takaici da bakin ciki suka rufe min zuciya.
Yanzu ni haka zan zauna a mara gata kamar wata mara asali in zauna da mijin da bai san tsoron Allah ba a zuciyar shi.
Bazan iya zama cikin wanan jassabab in yi ibada dole na shiga aikin gidan duk da gajiyan da na dibo din a motar.
Kafin wani lakaci na gama gyaran gidan na dora girki abincin da zanci na shiga wanka daidai lokacin da na fito bandakin ne sai gashi ya dawo gidan da ledoji niki niki kamar da gaske.
Tsaye yake a tsakar falo yana kwala min kira da ke wai kina inna ne nake kira baki karba min yazo ya bankado labulen dakin ina ciki ina sallah sai ya juya yakoma dakin shi.
Sai da na idar nafito falon baya nan na taka zuwa kofan dakin nashi na tsaya daga kofa don tun ranan da yace karna kara shiga mai daki ban sake ko taka kofan shi ba.
Nace mai gani daga kofan har ya tube ya kuna taba ga kida na tashi daga cikin dakin nai magana naga kamar bai jiba na juya abina zan shige ne ga kayan da ya shigo dasu gidan.
Nasan kiran da yake min kenan don haka na tsaya ina duba kayan, kayan miya ne sai maclean da sabulun wanka dana wanki sai madara da ovaltine da sugar.
Ina duke ina cire komai ina kaiwa inda muke ajewa ya fito falon daga shi sai gajeren wando jikin shi ba rika sai hayaki da yake busawa.
Take falon ya karade da warin taban ba dadin ji, ya zama min dole na mika al, amura gaba daya ga Allah don shine kawai zaimin mafita saboda yadda naje gida baba ya wulkantani a gaban yan uwa na da su inna ummi na tana kumsan bakin ciki gaba daya naji duniyan ta fice min a rai duk kuwa da shedan da yaya sani yayi dakuma wanda suka gani a jiki na baisa baba ya sassauta min ba ga halin da nake ciki .
Ko gaida shi nayi da kwana baya karba min itama ummi na abin ya shafe ta.
Yanzu dai gani na dawo a turke na mai cabo haka zan daure in ta hakkuri don kada fushin iyayyena na hau kaina.
Dama ance sabo turken wawa inda sabo ai yanzu na saba da wahalan gidan shi musamman idan yana jin fitanan shi anan falo zai min shaye shayen shi.
Haka kuma idan yaga dama ya afka min duk rokon da zan mai bai sai ya kyale ni, har sai ya ji ya samu yadda yake so da kansa.
Na nisa tare da fadin akwai Allah sai naji yana fadin in akwai sauran abinda ban sayo ba ki fada kada kuma kice na barki da yunwa.
Dajin haka nasan ya tafi gidan gwago ta kwashe karya da gaskiya ta fada mashi kenan shine yazo da wanan sayayyan.
A sanyaya na bashi amsa da sai man miya ba a sayo ba man miya ki saye mana iyakar kudina kenan na kashe.
Na dago ina kallonshi nai karfin halin fadin ai ba hakki na bane saye da sai in saye din.
Yaci gaba da busar taban shi bai tanka min ba can naji yace tsiyan ki kenan ke ba ai maki daidai .
Na dago zanyi magana naga yana min wani irin kallo kamar tsohun maye sai nabar maganan da zan yi a lokacin na gagauta kawar da kayan don bai mashi wuya ya afka min a nan wurin mutum kamar hariji bai gajiya da kwana da mata.
Ranan dai bai barni ba tun karfe takwas da na sallame sallah insha,i yana nan yana sintiri a falon.
Ina addua ya shigo min daki muryan shi naji a tsakiyan kunne yana cewa yau ki tabbatar da cewa zaki biya bashin kwanakin da kika dauka agida .
Na dago kai na dan kalle shi naga idanuwan shi jajaye akaina babu ko alaman kuya a tare dashi nace banci bashi kowa a kaina ba don ma ko nace ai akwai masu biya da suka fini daraja da kima.
Ban gama rufe baki ba nagan shi a gaba na dauka daya yai min sai saman gadon dakin nawa .
Ba bata lokaci ya shiga kiciniyar cire min hijjabin da nai sallah ya rake daga ni sai zani Allah ya tai make ni tun da na fito daga wanka na dan kintsa jikina.
Ba ta lokaci ya shiga sinsina na wuya na da na shafe da hummura da alama yaji dadin kan shi naga yana wani shakan ko ina daga bisani ya shiga watsa min kiss irin nasu na yan duniya.
Yakai tsawon minti uku yana abu guda ajikina zuwa bakina ina kokarin janyewa ne daga gare ya da kata daga abinda yake yi yace.
Wanan abinda kike yi shi ke yawan bata min rai dake a koda yaushe mutum zaizo gare ki sai anyi rigima.
Ba tare da jin tsoron shi ba nace dole ayi rigima don ba a zuwa ma mutum ta tsigar da ya dace sai a cikin may ko najasa.
Shiru yayi na wani dan lokaci yana kallona ido da ido yace nine najasan ke nan ma ko.
Gabana ya fadi naga yadda idanuwan shi suka kara kadawa sukai ja jawur dasu a lokaci daya nai saurin dauke idona gare shi.
Yayi amfani da hannushi ya sake juyo fuskana muna fuskantan juna yace come on so nake ki kalli idanuwa ki gayamin cewa wani najasa kike magana ko ysushe.
Na dai gane yau yana son mutunci ne don ko magana da yake yi a cikin karamin murya yake yin sa tankar yana tsoron wani yaji mu ne.
Kawai sai ji nayi hawaye sun soma cika min idona na cije fatar bakina sai can nace yaya ka bani daman in fada maka abinda ke zuciyana tsakani da Allah.
Sai na ji yace ke nake saurare ai gaba daya ya tsare ni da idanuwan shi sai na dan yi shiru zuwa wani lokaci.
Sai na soma magana da cewa yaya ka yarda dani tun da nazo gidan ka na zo da shirin maka bibyaya a duk yadda kake.
Amma sai ka dauke ni daukar mace biya a gare ka yau koda ace sayoni kayi a matsayin boya baka san asalina ba ban cancanci irin abinda kake min ba.
Kadoke ni, ka zagi iyayyena, ka dauko min karuwan ka har gida uwa uba ka zauna kayi shaye shayen ka har mai na gyara wurin duk ina hakkuri da hakan don biyayya ga iyayye.
Amma hakan bai maka ba sai ka yi kokarin tozar tani a gaban karuwan ka akan dole nai mata abin karyawa.
Yaya ina zaka da wanan alhakin a kan ka kai kadai bafa ban iya dauka mataki bane ina dai hakkuri ne don daraja aure dana iyayye amma duk wana bai isa ba sai ka , , , ,
Kuka ne yaci karfina na kasa karasa abinda zan, fada mashi din , irin rikon da naji yayi min shiya tabbatar da magana na yadan shige shi a lokacin.
Anan nayi kokarin kwace jikina daga ga gare shi amma sai naji ya kara matse ni daga jikin shi, ya shiga yin wasu irin magan gannu wanda na kasa fahintar may maganan nashi ke nufi don acikin harshen turanci irin nasu na wayyayu yake yi.
Acikin wani irin yanayi naji yana kokarin shiga na a lokacin fadi nake don Allah yaya ka barni amma bai kulani ba.
Naci gaba da magiya ba tare da yasan ina yi ba har sai da yacin ma manufan sa gare ni.
Ya gama ya mike kamar wanda aka tsikara yana mai daukan wando shi yt a bar dakin ina kukan takaici na bishi da kallo har ya bace min.
Nan naci kuka na ya isheni na tashi nai wanka ina tausayin kaina ni kadai a dakin .
Washe gari koda na tashi duk jikina yai tsami haka na daure na sama muna abin karyawa na gama na jera mashi a taburi.
Kwana biyu zaka ce ya daina halin shi ne don da yadawo aiki yana gida sai dai shan giya yabar yi a falo amma taba kan sai abinda ya karu.
Na shiri ranan wani jumma a na tafi gidan maman biyu tayi mamaki kwarai data ganni take tambaya na yaushe na dawo .
Na koro mata labari duk yadda zuwana gida ya kaya da kuma dawona da gwago nan garin sai da ta gama saurare na ta nisa tana cewa.
A gaskiya mahaifin ki yana da taurin rai Safiya ya kuma tafka babban kuskure da bai tsaya binke ba ya dauki mataki yadda ya dace.
Sai ya koro ki babu wani bincike da yayi wai duk karan zumunci yake yi alhalin yanzu zamani ya canza mutane basu da gaskiya ko kadan kowa nasa ya sani.
Takare da cewa babu komai yadda kikayi kin kyauta Safiya kibar wa Allah alamarin sa Allah yana tare da mai gaskiya.
Nan take tambaya da na dawo yaya halin nasa ya sauya ko kuwa yana nan kamar kullun nake cewa da ita ya sauya halin shan giya a falo kuma tun ranan da na dawo na samay shi da mace har yau banga ya dauko wata a gidan ba.
Tace Allah yasa ya daina indai ba tuban mazuru bane yai maki amma ga yadda na fahinta yana san son ki iskan cin dai ne ya sha gaban shi.
An sauko jumma a nai shirin komawa gida ta dan hado min dan abinda ta saba yi min tasa driver gidan su ya kawoni gida.
Sanin halin shi da nayi yasa nace drivern ya sauke ni tun a farkon layin mu na karasa da kafa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button