BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGAN, , , , , ,

????????1️⃣6️⃣????????

YAR UEA WANAN NOVEL DIN NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , , , ,

Yau nayi yamman yin kitso saura kadan na karasa wa wata mata kitso ta dawo daganin shi a gajiya yake lis,.
Nai mai sannu da zuwa ya amsa min ciki ciki ya shige ciki nai sauri karasa ma matan kitso na sallamayta na shiga ciki.
Na samu yana dakin shi don haka ban tsaya jiran komai ba na dauki tsintsiya na shiga gyaran gidan a gagauce ko da dai bai datti amma kaida ne nayi gyaran saubiyu nan.
Ya fito daga daki rai a bace ya wuce zuwa wurin three seater yana tsuki ya zauna nayi saurin dagowa ina duke na sake gaida shi cike da girmamawa.
Bai amsa min ba sai gyara kwanciyan da yayi rai a bace mashi yace wai ke wata irin doluwar yarinya ce .
Da mamaki nake kallon shi don basan laifin da nayi mai ba yake ce min doluwa kuma na ina kallon shi da mamaki.
Ya katse ni da cewa in ba dolewa kike ba yaushe har zaki tsaya uin wani kitso can kin san lokacin dawowa na gida yayi.
Kamar zan yi magana sai na duka naci gaba da sharana ban ce dashi uffan ba, wai ashe yin haka dana yi yaji haushi na.
Dole dama yaji haushina mana sabda tun da na dawo na hanashi shakat a gidan badai magana nake masa ba amma yana dan daga kafa ga haliyyan shi na banza a gidan.
Yau kwana uku kena da naga ya tsiri daukan zafi dani abu ba abu ba zai hauni da fada.
Kamar daga sama naji saukan mari a fuskana ina duke sai da na gigice na dago ina dafe da fuskan da har idanuwa na sun fara fitar da hawaye don zafin marin.
Fuskan shi babu annuri a cikin sa yace don ubanki ina magana zaki banza dani kici gaba da shara don kin mayar dani dan iska .
Na sake kallon fuskan shi tare da nuna razana shi kanshi sai da ya fahinci razana nawa na goge wahayen dake zubo min cikin takaici.
Nace yaya may kake son nace maka bance ba ma ka mareni har da zagin ubana balle na tsaya baka amsa.
Baiko numfasawa yake fadin na zagi ubanki ko zaki rama ne ya wani zazzaro ido waje.
Oh na zaci ai zaki rama ne yar iska kawai mara kunya banza munafuka in anyi magana kice wai ke ta Allah ce ina sanin Allah yake a nan.
Cike da tsoro nace dashi Allah ya baka hakkuri, ya buga min tsawa da fadin rufe mun baki mara kunya kawai.
Ya harare ni sama da kasa a karo na biyu kamar zai kara buguna sai dai na samu ya hakada ni gefe har ina gwauruwa da bango.
Ban sake magana ba na dadafa bango na shige kitchen ina jin shi yana dura min zagi yana fadin duk rana da ya dawo ya samay ni ina shegen kitson nan a gidan nan sai ya balbalani har da mai kitson
Ya gaji da fadan shi ya suri key din motar shi ya fita waje tare da banko min kofan gidan a fusace.
Na nisa a hankali dana ji fitar shi gidan naceai hali baya barin halin sa kwana biyu bai dake ni ba hannusa na masa kai kayi dana tanka ya samay ni yai ta jigga kamar an turo shi.
Na kamala aiki na cikin baci rai kaina namin ciwa kamar zai tsage ina ji ranan ya dawo a buge yana hauka shi ban fito ba karya hada dani.
Kwana ki muka dauka a haka a gidan yana faman daukan fushi dani a gidan da zaran ya shigo gidan zai kuna kida na tashi sama kamar kune na zai tsage.
Da zara na shigo falon idan yana ciki yanzu zai dauko taba ya kunna yana busa hayakin sama yana tashi ya gauraye falon.
Da sauri zan bar abin da nake yi na shige don jin warin nake kamar zan amaye hanjin ciki na kaina ya dinga sarawa.
Yauma bai fita ba tun safe yana gida kuma a falo yake zaune bai shiga ciki ba dole na fito hakana ina aiki na.
Na gama hada abinci na aje mashi nai wuf zan koma daki na yace ka dakata naja na tsaya.
Yana zaune yana ya mutsan fuska yana kallon abincin da na aje a gaban shi kaikace mugun abu na kawo mashi.
Ya wani harde kafa yayi kutun kutun da rai yana busa hayaki sama a zuciya ta nace dan isaka ka fada ma Allah ai.
Ina tsaye har wani lokaci a wurin amma hakan baisa ya dago ya kalle ni ba duk da cewa ni gyara tsayuwa don ya san dani a wurin tsaye.
Dole na gaji na dan yi mai magana dacewa gani yaya gani kamar bada shi nake yi ba shiru yayi yana kallon tv da ke aiki wasu fitsararu na rawa.
Na kara cewa yaya gani don Allah kafada min abinda zan wanka nake som naje nayi nai sallah don lokaci yayi.
Yayi wuf ya mike tsaye yana nunani tare da daka min tsawa ya sake nuni da hunnu yace ke yarinya baki fini sanin Allah ba don ba ke kadai bace yar musulmai.
Idan baki san abinda kike yiba nina san abinda nakeyi kada ki cika min kunnuwa da surutun ki na bashi na dakar dake inji ba.
Shiru nayi ina mamakin wanan mulkin malkan da yake min kamar ya sai boya a gidan zuwa ca na nisa nace a hankali yi hakkuri yaya.
Ya koma ya zauna yana kokarin bude abincin dake gaban shi , can ya dago yana cewa uban wa zai ci maki faten doya da rana.
Tsaye nayi kawai ina kallon shi da mamaki zuciyana yana tafarfasa zangan min uba da yake yi ba gaira ba dalili.
Yace a fusace ba tambayan ki nake ba kinyi shiru kin kyale ni, nace nafada maka bamu da koma a gidan ya kare tun kwana biyu da ya wuce..
Wani kallon sama da kasa yai min ya watsar yana cewa wanda na kawo maki kikai barna yanzu ki barnatar da wanda kika gani.
Bazan sake sayen koma a gidan nan ba sai wata ya kare don bake nake yiwa aiki ba da zaki ta cinye min kudi a banza.
Ikon Allah nace a raina amma a fili cewa nayi dashi yaya ban barnan abinci don ma karya kare ban yin dahuwar rana sai da dare nake dafawa.
Yace ke kika sani ni ba ruwa na kin dai ji abinda na fadi kuma ba zan fasa ba don haka ki bace min da gani.
Har na juya naji yace dauko min ruwa mai sanyi wanan yayi zafi ya fara cin abincin wayan shi yai kara ya dauka tare da fadin kin dawo kenan don naga nomban nigeria.
Ban san may wada yake wayan da ita ta fadi ba naga ya kalli a gogon hannun shi sai yace yau dai duk yadda za ayi zamu hadu.
Yana sauraren ta yana murmushi a fuskan shi abin da ban taba ganin yayin ba a matsayina na matar shi.
Can yace alrigt sai nazo din amma fa kada in samu baki nan ya aje wayan yana ci gaba da cin abincin sa daya gama kushewa.
Ya dago yana kallona nai kicin kicin da rai saurin dauke fuskanshi yayi ya dauki ruwan ya kora ya aje ya mike ya dauke key din shi ya fice daga gidan.
Shiru nayi ina mamaki wanan hali na shi na rashin tsoron Allah a gadarance komai yake sam bai tunawa a akwai Allah.
Kusan karfe daya dare ina kwance har nayi barci na falka naji dawowan shi gidan ya shigo yana may sai dai bai bugu sosai ba.
Don baji yana min haukashi na zagi ba ina jin yana buruntu a falo can naji ya bari nasan ya kwanta ne.
Barci bai kara dauka na ba na shiga tunanen wanan halin nashi shine giya shine taba uwa uba neman mata.
May zai je ya gayawa Allah tsiyan abin kuma baida mafadi da zai tsaya yai mashi fada da nasiha yaji.
Duk iyayyen sun watsar dasu suma suna nasu sharholiyan da muamula da yan iska ta yaya zasu gyara tarbiyan diyan su.
Gaba daya ba na gari dan dama dama yaya saadu koshi ban tabatar da halin shi ba tunda bana shedar shi.
Ina kwance naji hawaye nabin kuncina zuciya na cike da tausayin kaina ga wanan rayuwan da mahaifina ya zabar min yi .
Na tabbatar da i zuwa yanzu baba yana da labarin halin da nake ciki sai dai karfin hali ne kawai irin nasa na jajircewa.
Na nisa tare da gyara kwanciya na tsoro da fargabane ta sauka min a zuciya ta anya ko nima bazan kwashi zunibi a wanan zaman ba.
Washe gari ba abin da zan dafa mu na a gidan don komai ya kare har wurin sha daya rana can naji motsin shi yafito daga dakin shi.
Fita yayi daga gidan na dauke ya shiga gari ne zuwa wani lokaci sai gashi ya dawo da ledan take away a hannun shi.
Lokacin ina folo ina tsaka da gyaran gidan babu kunya ya samu wuri ya zauna tare da cewa in miko mashi goran ruwa.
Nabar abinda nake yi na shiga na dauko kofi tare da goran ruwan na kawo mashi daidai ya bude take away din nasa.
Tozali nayi da rabin kaza sai dan shinkafa a ciki na friderice da aka zuba yasha hadi launin kore shar.
Nan ya zauna babu tsoron Allah ta cinye tas ya wurga min roban a kasa yai zaune yana sakatan hakori da tsike yagama ya jawo taba ya aza.
Sai da na gama abinda nake yi har sha biyu ya gwauta lokacin ana neman karfe daya na rana.
Na fito saye da hijjab dina ina saka takalmi na ya juya a fusace yana fadin ina zaki ?
Ban ko numfasa ba nace neman abinda zanci tunda safe banci komai a ciki na ba yayi saurin cewa to wa ya hanaki kice barnan ki ya kaiki ga karar da abincin da na kawo maki ai.
Nace abincin da ka kawo min yaushe nake barnan shi gidan nan dudu fa kwano biyu ne na shinkafa kuma ko kazon shi baka taba gani a kasa ba.
Kwano biyun ai nayi kokari daso kikeyi na kawo maki buhu komay ai a gida ku ko kwano biyun ana cine na shinkafa.
Daya ke nan kon samu banza shine kike barnatar wa ko ta yanzu kici kuma wallahi in kika kuskura kika fita yau sai na balbala ki a gidan nan.
Alokaci guda jikina yai sanyi nace kayi ma Allah yaya kayi hakkuri in nemi abinda naci kar yunwa ya illanta ni.
Yace bazaki fita ba nace a hankali na matsa wajen shi nadan fara magana a sanyaye cikin kamala nace yaya nasan ka isa ka hana ni fita amma ka tausaya min in samo abinda naci tun da ranan jita wallahi banci komai ba a gidan nan.
Yace ke na fada maki don ba zan yarda ki rika zubar min da kima a waje ba a ganki kinje sayen abu ga hannu.
Da mamaki na dago ina kallon shi bakunya ya fadi haka kamar ince kaida ka sayo abinda kaci fa yanzu.
Nace ya kamata ka tauna maganan ka kafin ka fadi indan ban sayo naci ba may zanci a gidan nan kenan.
Yace ke kika sani gobe in na kawo abinci zaki koyi tatalin shi dakyau ya tashi ya shige dakin shi ya barni tsaye a wurin na bishi da kallon mamaki.
Ina cikin daki na idar da sallah azahar naji fitan shi daga gidan nan na fito falo na zauna sai ga makwaciyana ta shigo wurina bahausa ce akwai dan nisa a tsakanin mu.
Bayan mun gaisa take cewa dani ai tun dazu naso shigowa nasan wanan miskilin mijin naki na gida don naga motar shi a waje .
Nace yanzu ya fita bai dade da fits ba ta na bude hijjib din tace ga dan wake nayi damai da yaji nasan zaki so don nan ba arewa bane na kawo maki na karba ina godiya.
A zuciya na sai kabbara nakewa Allah da yai min mafitan abinci ts ida ban zata ba bata dade ba ta fice tare da min sallama tace tana da aiki gida.
Nai mata godiya na dan raka ta bakin kofa ts fita na koma a sukwa ne daki na hauci hannu baka hannu akushi naci sai da na cinye shi tas na kora da ruwa mai sanyi.
Nai hamdala gs Allah da ya bani abin da zanci shi mugun baiga karshe na ba na bude window dakin da sake fanka kamshin ya fita.
Bai dawo ba sai bayan karfe tara na dare yazo da ledan shi na abinci da na dan wani bussashe burodi ya wuga min daki na ya zauna nan yaci abincin shi ya koshi ya fice gidan tare kulle ni ta baya.
Bai dawo ba sai safe lis koshi don ranan aiki ne nasan zai tafi wurin aiki ya dawo da wuri don kada ya makara.
Ya fice baiko bi ta kaina ba na sauke ajiyan zuciya na mike da sauri na shirya zuwa gidan maman biyu don na samay ta gida kada ta fita office.
Nayi arziki tana shirin fita na iso gidan tana ganina ta aa Safiya yau da safe haka kika bugo sammako.
Maimakon in bata amsa sai kuka bata hanani ba ta zauna tana tare da harde hanneyen ta saman kirjin ta.
Sai da nayi mai isata ta miko min ruwa tace jeki ban daki ki wanke idon ki dashi mikewa nayi ta bini da kallo a ranta tace wake da laifi mahaifina ko mijin koko ni.
Fitowa na ya katse mata tunanen tace zauna a kawo maki abinci kici nasan baki karya ba wanan sammakon da kika bugo haka.
Mai aikin ta ta kwala wa kira tazo tace akawo min abin karyawa aka cika min gaba na da abinci fal na kasa cin komai duk da ina so din amma kincin zuciya ba zai barni naci komai a lokacin.
Ta mike zuwa ciki can ta fito ta samu ban taba komai ba daga cikin abin da aka aje min din.
Tace aa anty yan biyu bakici bama na lafiya dai zan fara kuka tace dani dakata banson yawan kukan nan ki fada min binda ke faruwa.
Dama nasan wanan mijin naka dan iska tuban mazuru yayi ba tuban Allah da annabi yayi ba.
Nace wallahi anty dama kin fada ai nace wallahi anty da yunwa yake horoa na yanzu nan na kwashe komai na fada mata .
Tace dan iska wai ashe bazan sa a kama min dan iskam mijin nan naki ba aimin maganin sa matsalan kawai mahaifin ki da idan yaji zai tsitsine ki a banza.
Anya safiya wana mijin naki kuwa yana cika sallah shi don bai abinda masu imani keyi a rayuwan su.
Nace ina fa yake cika sallah anty ibandam dai gashinan ne daga jumma, a sai jumma,a ake yinta .
Tace kin ga yanzu aiki zani bari na saka a samo maki abinda zaki ci kiyi ki koma gida don yana iya maki tako yaje ya dawo ya gani ko zaki fita.
Tace ki dai kara hakkuri mu gani indan bai daina ba wallahi ni da kaina zanyi karansa a raba wana kaddararen auren naki.
Komai aka hado min mai yawa babu abunda babu na fannin girki da ba a hada min ba niki niki na dawo gida da kayana.
Taimin alkawarin zata dinga zagayowa akai akai tana dubani nai msta godiya ina kuka tace nayi hakkuri ta kawo kudin ta kara min ta wuce zuwa wurin aikin ta.
Ban bata lokaci ba na shiga kawar da kayan kafin mugun ya dawo gidan ya tar dasu ya samu na min iya shege a kan su.
Komai na adana su tsab ba abin da na bari a fili na dawo falo na zauna can ko kamar ta san zai dawo sai gashi ya shigo gidan ina zaune a falo.
Ko kallo ban ishe shi ba ya shige dakin shi fuskan murtun kamar na yan high killer marasa imani dasu jin kadan ya fito ta sake fice wa na nisa tare da fadin macuci azzalumi kawai ta Allah bataka ba.
Kashi dai karfafa ne gashi da tsayi da saje ya kewaye masa fuska a ido kamar kamili idan ka gashi amma duka halinsa ba na saye.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button