BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

* * *
Yau na tashi jikin ba dadi ga damuwa dana sawa raina ga kuma halin maigidan ba sauki akan komai.
Kwace nake a falo saman dogon kujera nayi da daya da kafana ko zan ji dadi jikina misalin karfe biyar na yamma.
Can na fara barci naji dawowan shi gidan yana gauran kofan shigowa gidan gabana ne ya fadi don ganin shi a murtuke da fuska.
Innalillah wa,inna ilaihi rajiun Allahuma Ajirni min musibati waakhimi min kharir minha na anbato a raina.
Ya shigo yana ta faman kalle kalle har ya kai zaune saman kujera tsoro ya kamani don ban an damay ya shigo ba.
Na dago cike da natsuwa da girmamawa na furta sannu da dawowa bai amsa min ba sai taba da ya ciro cikin aljihun shi yana kokarin kunawa warin taban ya gauraye falon lokaci guda.
Na mike da sauri zan bar falon sai lokacin yai magana yace ke mayye haka kuma ?
Ina kokarin tare aman da yazo min a baki nace zan zan zan sai na mike da gudu na fada dakina direct makewayi na shiga nai ta shega amai aciki.
Bina yayi da kallon mamaki bai yarda dani ba, ya mike ya bini yana tsaye nake ta aman sai da nagama na mike zan fito naganshi a tsaye ya rike kugun shi.
Gabana ya sake faduwa yana min wani irin kallo na tuhuma mai kama da bai yarda dani ba yace ke mai ke samun ki ke amai haka.
Na amsa dakyat da cewa ban da lafiyane .
May ke damun ki koma may nene ke kika sani don ni banda lokacin ki ya juya har ya fara tafiya ya juyo yana ce mun ki sani ban son kazanta a gidana.
Na yamutsa fuska nace kona bata ma aini ke gyarawa ba wani ba ya juyo yace may kika ce ne ?
Nace bada kai nake ba ai yace shgiya naga randa bakin nan naki zai mutu da bakar magana dibi yadda kika murje kikai wani bulbul dake duk abincina kike cinyewa ga banza.
Yafice na sauke ajiyan zuciya na zauna nadan huta na fito kai tsaye kitchen na fada don girka abinci don nasan a gida zai kai dare tunda ya dawo da wuri.
Na gama aiki da kyat na shiga na watsa ruwa don lokacin sallah ya gabato ina zaune ina lazimi naji ya kwala min kira.
Na taso dagani sai yar doguwar rigan da anty ta bani ranan da naje gurin ta tace ta gani ne dataje sayayya ta sayo min shi.
Na fito abincin da na aje mai yana bude na sauke idanuwana akan abincin dake gaban shi din.
Ya watso min harara yana cewa wani irin abinci kika dafa haka nace shi kadai ya saura muna a gidan shiyasa na dafa taliya ne nai jelop din shi.
A fusace yace what, what are you saying ?
Kina nufin har abincin da na sayo yakare komay ?
Na girgiza kai nace yaushe rabon da ka sayo abinci a gidan nan wanda ka sayo din ai shi na dafa lokacin da bakada lafiya masu jiyan ka suka cinye.
Ya dakatar dani da hannu yana fadin ya isa haka maganan ya isheni sai ki zauna ki cinye dama haka kike so ai.
Ya dauke makulin motar shi dake saman tabur yabar gidan yana faman huci.
Sai da muka share kwana uku cur ban da lafiya kuma ba a girka komai a gidan.
Ina kwance daki ina fama da kai na nidai kamar kar maman biyu ta ambaci cikin nan wahala ya soma zuwa min.
Sai kawai gashi ya shigo min daki misalin goma na dare don rashin imani irin nashi sai ji nayi ya afka min .
Na soma kuka ya gama ya daga yana cewa may ye haka tsiyan azo wurin ki kenan walahi ki damu mutum da munafukin kukan ki.
Na dago ina cewa azo min haka kamar wata karya ni kadai nasan abinda nake ji a jiki na yanzu haka ji nake kamar baya na zai tsage san nan ban ci komai ba tun safe ga yunwa na damuna.
Yakai kofa ya juyo yana cewa ai sai ki samu abinda kikaci ko kije asibiti adubaki nace da nawa zan tafi asibitin yace ke kika sani.
Washe gari ma da ciwon na tashi don da dare banyi barci ba ciwon mara ya hanani shakat a rayuwa na.
Ban fito ba har ya gama shirin shi zai fita komay ya gani sai ya leka dakin nawa.
Ina kwance ina faman murde murde a saman gado ni kadai a dakin ya leko yadan dade tsaye akaina sai ya karaso bakin gadon yana cewa.
Wai ke may ke damuwan ki ne haka kike faman murde mude a gado ke kadai a dakin ?
Da kyat na bude bakina nace cikina ke ciwo sai kaina dake sarawa kamar zai balle min nake ji.
Ya fita da zai dawo sai gashi da magani da maltina da peak milk mai sanyi a leda da kayan abinci ya sayo.
Ya samay ni a falo na yi laga laga dani ya miko min maganin da maltina yana cewa ga magani ki sha.
Nai mamaki ganin magani harda maltina ya sayo min babu kunya babu alamanta ya zauna yana cemin tashi ki sha.
Da taimakon shi na hadiye maganin sannan ya hada min maltina da madara yace in shanye kafin ya fito.
Bayan kaman minti shirin sai gashi ya fito ya dubeni yace yanzu ya fada maki ko yana nan ?
Nayi ajiyan zuciya nace ya fada min nace na gode yace na taimaka maki ne don nima kin taimaka min da banda lafiya don haka arama ma kura aniyan ta.
Na ciza baki na yunkura ina cewa aiko kura ta gode in don Allah akai mata.
Ya harare ni yace gunma ki wartsake don ba zan dauki nadewa a gado ba tunda kun hanani hurda da yan mata na yanzu.
Na saurin kallon shi ina cewa wa ya isa ya hanaka da abinka muka ganka mu mun isa wanan sai Allah daya hallice ka ai.
Sai kawai naji ya kyalkyale da dariya sai nai saurin dago kai na kalle shi cike da mamaki yau shike dariya haka kamar ba shi ba.
Yace ashe kun san da haka da baki wahalan hada baki da matar sojs tashigo abin da bai shafe ta ba.
Ya fice ban sake jin duriyan shi ba sai dare sai gashi ya dawo min a cikin maye yana ta tsuki burutsun shi a gidan.
Ina daki ya samay ni a haka na dan dago ina kallon shi naga ya nufo ni gadan gadan sai na fashe mai da kuka don na san halin fitinar shi sarai ba imani ne dashi ba.
Yace a cikin maye ke ke may nene haka ?
Na yun kura na tashi da kyat ina cewa don Allah yaya kayi hakkuri wallahi ban iyawa banda lafiya ne.
Na gaya maki zan maki wani abune kawai kawai yana inda inda ya kasa fadin abinda zai fada din ya juya yana suruntun abinda banji ba ya fice dakin.
Na lumshe idanuwa na a hankali ina sauke ajiyan zuciya ganin ya fita natashi na rufe kofan dakin nawa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,
????????1️⃣9️⃣????????
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDINE IDAN BAKI BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE.
Kwanaki goma sha uku da aukuwan wanan lamari yana zaune a falo ya harde kafa yana shan ruwan kwalba da sigari yana sha yana yamutsan fuska kamar an sashi dole ya sha.
Na fito daga daki rike da cup a hannu na ban san yana zaune wurin ba sai ganin shi nayi yana korawa.
Da sauri na wulkita zan juya dakin da nafito ganin haka yasa shi mike a ida yake zaune din ya nuna ni da hannu.
Ke ban san sau nawa zan fada maki cewa idan ina zaune kika gani ki daina gudu kamar wata mara gaskiya dake.
Nikan ban masan yana yi ba don na dafe bakina da hannu daya kar amai danake ji ya fito mun a falon.
Ganin yanayin da nake ya dakatar dashi ga fadan da yakeyi din ya kafa min idanu yana kallona a cikin zargi.
Yace Safiya ciki gare ki ne ko may ban sani ba don tun ga kwanaki naga kina wanan aman na tsiya.
Nikan ban ma san yanayi ba ina tsugune na dafe kaina sai kakarin amai da nakeyi a ban dakin .
Hakkali a tashe ya sake magana da cewa kefa nake tambaya na dago da kyat ina cewa cikin yanayin ciwo warin taban nan ne ke wahal dani.
Ya ja tsuki ya juya yabar wurin dakin shi ya shige da bacin rai bai fito ba haka nima ban fito ba na kara dunkulewa cikin dakina.
Kwana biyu baya gidan ban san ina ya shiga ba ga komai ya kare min don haka na shirya zuwa gidan maman biyu.
Yanayi na kawai ta kalla tasan ban jin dadin jikina yace wai ko kunje asibiti kaina girgizamata kawai alaman a a.
Safiya kamata yayi ki fito ki sanar dashi zancen cikin nan amma ba wai ki boye ba don ba zai yuyu kibar ciwo a jikin ki ba don ciki ciwone.
Nace to Anti shidin ne almarin shi har yanzu ba canji kin ga tun kwanaki ya gane bana jin dadin jikina amma don rashi imani yau kwana biyu kenan baya gidan kuma ban san ida ya shiga ba.
Idan ma yana nan ba wai kyaleni zai ba don banda lafiya haka zai afka min kamar dabba don rashi imani irin nasa.
Tace ke Safiya kar in sake jin kalman dabban nan a bakin ki, karki manta shifa mijin ki ne na sunna.
Nace anty ai ba fadina bane, Annabi nefa ya siffanta duk mai irin wanan dabian da daba, sannan sai kinga irin wahalan da yake bani abin har da mugun ta yake hadawa.
Wai in mun hana shi bin mata banza waje ni zanji a jikina tunda nace ina iyawa.
Sai na soma mata kuka tai saurin cewa may ye haka kuma safiya ko so kike ki tada min hankali ?
Ina kuka nace wallahi anty ba haka bane wallahi ni kadai nasan abinda nake ji ajikina yanzu haka idan indan ina tafiya jire nake gani marana kuma kamar zai tsage min biyu nake jinsa sanan na kasa sa komai a baki na komai naci sai ya dawo min.
Tace ya zama dole ki dada masa idan bai dauki wani mataki ba ki zo kifada min kina jina ko don ba a zama a duhu haka kina jina ko.
Nace naji zandan kwanta kozan samu barci yanzu haka jiri nake gani tace inshiga daga ciki don kar a dameni nan falo na kasa barci.
Na samu nayi barci sosai sai wajen uku na rana na farka daga barcin naji dadin jikina matuka don naji kaina yabar sarawa.
Nai sallah naci abinci sannan na fara shirin komawa gida ta harhado min komai da zan bukata zakace ko uwatace ko wata yar uwana ta jini abinda take min.
Kusan karfe hudu da rabi na dawo gidan na danji saukin jikina ko banza nadan samu warwarewan zuciya na dana dan samu idan da na tsiyaye.
Har na dawo na dan gyara gida tunda na samu karfin jikina bayan nai sallah ishai ina kwace saman carpet ina kallo ya dawo gidan.
Kai tsaye dakin shi ya wuce bai fito ba yan yai wanka ya fito saye da guntun wando da singlet sai taba a hannun shi.
Bai same ni a falo ba yayi zaton ina dakin girki ne sai da ya saurara sannan yajiyo kakarin amai daga daki na ina cikin ban daki.
Ya mike da sauri zai bini sai gani na fito ina tafiya kamar wacce tayi makwanni cikin ciwo ya dinga sata kallona har na dawo inda na tashi saman carpet na kara kwantawa.
Na daure na dago kai a hankali nace dazun ka dawo ina gaisheka baka amsa min ba ido kawai ya tsura min baiyi magana ba.
Sai cewa yayi tashi muje chemist a duba min ke ban yarda wanan uban amai da kike min haka ba cikin gida in an yi magana kice babu komai.
Ban mussaba na yunkura na tashi daki na shiga na dauko hijjab dina na fito ya kulle gidan muka wuce chemist din da yace.
Sai daya bata lokaci sosai yana dudubani don har fitsari yasa nayi ya auna ni ga dan karen tambayoyi da yake min har na gaji da amsawa daga karshe dai ya bashi tabbacin ina da ciki wata hudu da kwanaki.
Ya bani magunguna da zanyi amfani dasu don taimaka min wurin rage aman da nakeyi don acewa mai chemist din yawan kakarin da nakeyi yasa cikina kullewa .
Amma ba ciwo bane mai tsanani don haka mu kwantar da hankali mu tunda ya fara magana yake gum baiyi magana ba sai mur din da yasha.
Hakan da yayi yasa nasan akwai magana fan a zuciyar shi dama kuma abinda nake gudu ke nan ban yi saurin fada mashi ba.
Ya sallami mai shagon muka kamo hanyan gida har lokacin yana gum da bakin shi sai da muka shiga gida na yi hanyan daki na sai kawai naji ya shakoni ta baya.
Idanuwa suka firfito waje kamar zan shude yace a hasale uban wa yai maki cikin da kike dauke dashi nace .
A lokacin da yasan bakin cikin da nake ciki nafi bukatan ya kashe ni in huta da wanna rayuwan wahala da na samu kaina a cikin sa.
Jin kaifin shakan yai yawa nace uban da yake matseni duk dare yai min dole ka taba kwana dani a cikin yarda nane a gidan nan.
Ya kara shako ni yana fadin yar iska sai ki san yadda zakiyi da cikin nan inba haka ba na lahira sai ya fiki jin dadi.
Nace cikin karfin hali amma kadai san ba yar iska ka samay ni ba ko bantaba kwana da wani namiji ba bayan kai a rayuwa na da zakai min wanan tambayan yan iska.
Yace good sai ki san yarda zakiyi da cikin nan a gidan nan don ni ban shirya haihuwa ba yanzu
yara su hanani shakat a rayuwa na.
Ras naji gabana ya fadi nace wata sabuwa kenan kuma inji yan caca wani sabon fitina kuma zai kawo min yanzu.
Hakana mukai ta jidali a gidab dagani sai shi daga karshe dai ya kaini kara wurin ma haifiyar shi akan lalelale sai na zubar da cikin nan in ina son a zauna lafiya.
Babu kunya ta kirani nazo gidan ta ta tare ni da maganan cikin har tana cewa nafison in cika gida da yara miji baida wadata.
Nace Allah daya bani shi zai dubeni da abinda ke cikin cikin nawa don haka na san zunubin da ke ga wanda yai kashin kai ni ba zan zubar ba.
Tace tunda haka kiks zaba duk abinda yai maki ke kika jiyo baruwa na karma kice kin sanni.
Ranan ban kwana ba sai da yai min dan karen dukan tsiya har ya barni kwace da kyat na lalaba naja jikina zuwa dakina.
Washe gari jikin yai min tsami na lalaba nai wanka na lalubo sauran magani na hade na koma na dun kule.
Waya naji yana yi da wani likita akan zubar da cikin koda ya leko dakina na lafe kamar mai barci sai ya fice gidan.
Ina nan ina sake zuci sai sallaman maman biyu naji gidan don tun ranan da suka samu matsala akan lilliya bata dawo gidan ba.
Yau tazo taji yadda mukayi dashi ne akan zancen cikin na tare da murna na abinka da wanda ta rigaka kwana sai ya rigaka tashi.
A take ta gane yanayin da nake ciki na bugun da yai min a daren jiya kan naki yarda a zubar da cikin cikin sauki.
Tace dani kunyi halin naku ko, ?
Kin sha dukan ko badai duk akan cikin bane wannan dukan haka ?
Idana sun ciko da hawayen na dama nace anty cewa yayi wai a zubar da cikin shi bai shirya haihuwa yanzu ba.
Tace a cikin mama what ?
Na hade wasu yawun bakin ciki nace har da maman shi abinda tace dani kenan wai idan ban zubar ba duk abinda ya samay ni ba ruwan ta.
Kai ta dafe tai shiru na wani lokaci can tace wai wa yan nan mutane kuwa musulmai ne kuwa ?
Na murmusa nace wai musulmai ne kuwa anty babu dai tauhidi a zukatan su ne kawai.
Ta mike ta fice gidan kai tsaye ashe wurin aikin su ta tafi don ta bincika tasan komai akan shi.
Can ta samay shi tace su hadu gidan shi yanzu sanin halin shi da tayi yasa baiyi gardama ba ta riga shi isa gidan ya samu tana jiran shi.
Yana shigowa tace zauna shagon mata don ka zama shagon mata baka da aiki sai dukan mace macen ma karamar alhaki irin wannan.
Dadin may kake ji cikin dukan da kake mata ne wai, kai bama wanan ba cikin dake jikin ta waye mata shi ?
Ya dago ya kalle ta don jin abinda ta fada tace eh ina son inji ko ba naka bane don musan abin yi.
Yace kin gane madam nasan ciki nawa ne to amma ni gaskiya ban shirya, , , ,
Sai yai shuru tace, go on, baka shirya may ba dama ka auro tane kawai don ka more rayuwan ka da ita ko may ?
Tace tirr da hali irin naka tirr da rayuwan kafiran farko kai acikin su ma kana kasa da fir,auna.
Ashe kai ba abin farin ciki ne ya samay ka ba maimakon ka godewa Allah da baiwan da yai maka sai kawai kai halin ku na yan duniya.
Ba a haihuwa kai aka haife ka, dama kenan ka auro tane don kawai kaji dadin rayuwa da ita ko may tun wuri ka gyara halin ka tun duniya nayi dakai.
Tai mashi kaca kaca yana saurare ta kamar wani salihi can dashi ni nasan jin ta kawai yake yi badon nasihan ta shige shi ba.
Ta nisa tace dashi haba dai kamar wanda baida tausayi katuna fa kaima kana da kanai kuma haihuwa zakayi indan anyiwa taka haka yaya zakaji.
Sannan ina son ka sani idan wani abu ya samay ta, ko cikin dake jiki ta sai nasa an daure kowa naka a duk inda suke a garin nan sai antona man su.
Kuma ka tabbatar da kana bata abincin daya dace mace mai ciki taci dan lafiyan jikin ta dana baby dake cikin ta.
Duk ta baibaye shi ta ko ina baida halin motsawa ta mike tana gyara gyalen jikin ta, ta wuce ko kallona batayi ba ina kuka da mahaifina da ya jefani wanan halin.
Ya dinga sintiri a cikin falo yaje ya dawo har na wani lokaci ya dawo inda nake rakube yace ke ki fada min may ye hadin ki da wanan matar.
Nai shiru ya kara daka min tsawa yace ba zaki fada min ba, nace yar uwan mahaifiyata ce na fada maka tun farko sai ya ja tsuki ya fice gidan.
Tun wanan lokacin bai ce min ban ce mai zaman doya da manja muke yi dashi a gidan sai ya kwashe kwanaki bai gidan sai yaga dama zai dawo bai dadewa kuma ya fice.
Nima haka ya fiye min dadi don ba matsi ba tsagwama ba warin taba da giya sai in yini falo gidan hankalina kwance.
Abinci dai da maman biyu tasa mai doka ina samu sai dai bamai dadi ba amma ina ci in koshi ko ba dadi yafi babu.
Ranan ina zaune a falo ina kallo sai gashi da liliya yana gaba tana binshi a baya da katon akwatin ta, suna kokarin shigowa dashi.
Wai ashe auren bariki sukayi, yan giya yan uwan su suka daura masu aure acan mashaya su.
Ko kallona basuyi ba suna kokarin shigewa da kayan nata, ina zaune ina kallon ikon Allah, suka shige dakin shi da kayan can sai gata ta fito ta bude munafukin gyalen da ta rufe fuskan ta dashi tace.
Ke wa kike da suna ina son fada maki ban son ganin ki a falon nan indan maigidan na gida in ba kiran ki akayi ba.
Nace ke kuma a suwa dan wake a hotel, tace ni a su matar gidan, inda ance min karuwa yanzu na zama matar gidan sai
a nemi wani suna a canza min.
Ya wuce a kiraki da kilaki ko mai dadiro don sunan da ya dace dake kena don kin fi cancan ta dashi.
Shine ya fito yana cewa baby na fada maki bani son kina shiga tsabgan yarinyar nan, da ita da babu duk daya a gare ni tana zaman cikin ta ne da tace taji ta gani dashi.
Kema kin san wanan ba ajina bace kawai dai matsala aka samu aka aura min ita amma wanan abar ai da gidan aiki ya kamata ta a danganta ta.
Nace andai ji kunya wallahi tunda dadiro aka fake aiko anci baya wallahi ya balla min harara da jajayen idon shi.
Yaja ta suka shige ina jin suna dariya dariyen su a dakin ga kida na tashi ina daga dakina bakin ciki ya cika ni.
Haka dai muke zaune a gidan ba ruwan shi dani ina kallo zasu sayo abu su zauna a falo su baje suci inya rage a zubar ga abin shara.
Ko ta dafa da kanta a gidan kanshi yana tashi gidan haka zanta juye da cikina su gama su cinye su hana min ina kallon su ko kallo ban ishe su ba.
Ranan suna zaune suna ta shakiyancin su a falo na samay shi a falon suna gani na, ta wani shige mai jiki .
Shi kuma sai ya daure fuska murtuk nace dashi yaya abincin da ka saya min ya kare tun kwana biyu da ya wuce.
Sai cewa yayi kije gidan ku a baki don ni ba dole bane sai na baki tunda baki jin magana na.
Ita kuma ta dago kai ta wani harareni tace ke bana fada maki kada ki kara kula min miji in yana nan ba shine don maita irin naki kikai mai magana yanzu wai manyar ina ce halan.
Nace ke tsohuwar kilaki rufe min bakin ki da ke nakeyi balle ki samun baki ga zance na.
Tsawa ya daka min yace duk ranan da na sake jin kin kira min mata da kilaki sai na halaka ki a gidan nan.
Kallon mamaki nabi shi dashi ina cewa ai akwai Allah yana sane da komai da ka ke yi shi zai saka min.
Ban karasa ba ya buge min baki gau da mari sai da wani wuta ya gittamin gaba na.