BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , ,

????????2️⃣2️⃣????????

YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN SU PLEASE, , , , ,

A can gida sani Allah sani annabi aka samu ummi ta dawo dakin ta amma har ta dawo tana nan akan bakan ta na bata zama gidan da bata da yancin kanta balle diya.
Inda ba a san darajan mace ba da yara ake masu mulkin kama karya a gidan baka da wani tacewa sai yadda akayi dakai.
Yan uwanta kuma suka mara mata baya sai da baba ya koma yana karamin murya da sani Allah sani Annabi mahaifinta ya kara tursasamata ta dawo gidan.
Sai dai dawowan a tsatsaye ta dawo masu gidan bata shayin kowa da anmata abu yanzu ne zata maida martani akai.
Hakan ya dan saman mata sauki a gidan gashi tun bayan ni da nai aure ba wanda ta kara aure a gidan mu nima din danayi sunan nayi ne kawai.
Yanzun dai suke fitar da mazajen auren don haka kowa shirin aurar da yar shi yake yi a gidan in ka debe ummi na daga cikin wacce ke kumsan bakin cikin yarta.

* * *
Zaune nake a kasa saman dan center carpet din falon abinci a gaba na sai kira,an dana kunna ina saurare ina bi a hankali.
Nayi wani irin fari duk wanda ya ganni sai yai maganan farin dana kara cikin jikina ya turo sosai don ya girma yanzu.
Banji shigowan shi falon ba sai ganin shi nayi a tsakiyan falon yana ce min wanan wani irin abune kin ruda gida haka da karan karatu idan bi kike baki rage karan yadda zaki ji mai shigowa gidan.
Ban kula shi ba sai dai ina mamaki a raina shida yake sake kida ya kure karan kamar gidan zai tashi don kara baac mai komai ba sai ni yau da na saka kira,a gidan yake fada
Ban saure shi ba ya dauki remote ya rage karan ya juya ya shige dakin shi kai tsaye.
Kiran sallah magariba akayi don haka na mike zuwa daki na don yin sallah har na idar banji motsin shi ya fito daga dakin ba.
Don haka na mike na leka dakin kwance yake yana sharar barci ko kaya bai cire ba yadda ya saba yi indan yadawo gidan.
Muryana ya dinga ji a tsakiyar barcin shi ina tada ya tashi yau sallah bai saurare ni ba ya gyara kwanciya yaci gaba da barcin shi.
Saida yaga dama ya tashi don kanshi yai abinda zai yi ya dan fita nasan giyan shi ya je ya dirka sai dai bai bugu ba ya dawo da ledodi da yasayo abin breakfast din mu.
Na kashe wutan daki na kwanta ina jin motsin shi a falon barci ya daukeni motsin shi da naji a dakina ne ya tayar dani daga barcin da na fara yi.
Yace na kasa barcine shiyasa nazo taya ki hira namiji baida ta ido ko kadan nida yace ban iya komai ba yake fadawa wanan maganan haka.
Nidai na matsa mai ya hawo ya kwanta daf dani naji ya fara shafana a hankali.
Idona na lumshe ina maijin tsanar shi a raina don ban iya mantawa da cin fuskan da sukai min gidan shida lilliya.
Ya juyo gareni yana cewa may ye azuciyar ki may yake yawo a kwakwalwar ki gamay dani.
Nace kai dan uwa na ne na jini kuma mijin da mahaifina ya zaba min dole komai yai zafi ina tare da kai duk rintsi komai wuya komai dadi ina tare da kai a gidan nan amatsayin matar ka kar kayi tunanen daukan fansa a gare ni don kai dan uwana ne kuma mijina.
Wani iri yaji har acikin zuciyar shi don yasan ya cuta min ta ko ina harda ma inda ban sani ba sai dai kawai ayi hakkuri da juna.
Nisawa yayi tare da gyara kwanciyar shi yace to ki daiyi hakkuri da komai.
Nace hakkuri kan na yi amma yaya bazan sake irin hakkurin da nayi a baya ba amma zama kan yamin dole a gidan ka.
Shiru yayi ya kasa barci yana ta juye juye ya tsinci kansa a wani yaniyi tabbas ya san ya zulunce ni tako ina duk kokarin da nakeyi baisan may yasa ba ya gani ba.
Yarinya ba inda ta gaza dashi tsabta da girki da kula da kayan gida da kokartawa da bashi hakkin shi duk ta yanda yazo mata amma shi ya kasa daina barikin shi a zauna lafiya.
Ga saadu kanin shine na baya amma har ya fishi hangen nesa ya hanngo mai abinda bai taba tunanen hangowa ba a rayuwan shi.
Ya tashi ya yai zaune yana maici gaba da tunanen abubuwan rayuwa a ran shi.
Har barci ya fara dauka na naji matsin shi yai yawa na haska hasken tocina don in ga may yake yi a lokaci tare da cewa ba kayi barci bane ?
Yace yau na kasa barci ne ban san abinda ke damuna ba haka nace Allah ya kyauta ko may nene amma da zaka koma dakin ka ka barni zaifi min in samu barci.
Ban dauki lokaci barci mai nauyi ya dauke ni ya lumshe idon shi yana mai kare min kallo na dunkule a wuri daya ina barcina hankali kwance.
Sai wuraren asuba ya samu barci ya dauke shi bai wani dade kwarai yana barcin ba ya dinga jin murya na ina tadashi yai sallah.
Bai saure ni ba sai barcin shi yake yi nan na barshi a kwance na wuce nai wanka tare da dauro alwala har na fito bai falka ba.
Nata da sallah na harna idar sai nasari yake kwasa a cikin barci duk ya wani rudamin daki dashi.
Na idar ina addua na sake ta dashi da yaga kamar damun shi nakeyi sai ya dauki filo ya danne kanshi dashi.
Har na gama anbinda nakeyi yana nan a kwace min dirin a daki yana barci matsa mai nayi sai ya tashi.
Nan ya mike a harzuke ya hauni da masifa meye damuwan ki da rashin tashina kibarni lokacin da duk na tashi zan iya yin sallah na.
Ban samu barci da wuriba jiya da kyat na samu barcin ya dauke ni yanzu kuma kinzo zaki matsamin ki kyale ni nai barci na karki sake tasheni.
Nan nima nace a harzuke zan tashe ka dole in tashe ka ko sau nawa zaka koma barci muddin bakayi sallah ba sai na ta dakai.
Haka kawai ana sallah kana kwance kana barci katashi in kayi sallah sai ka koma ka kwanta yafi, magana da nakeyi na damay shi.
Ya mike a hasale zai koma dakin shi ya kwanta yana fama dani na daure nace yanzu kai bakajin, kunya ko tsaron Allah kaine fa yakamata ace ka data dani nayi sallah amatsayi na kaunan ka ko matan ka.
Amma ana sallah asuba kai kullun kana kwance kana barci a daidai lokacin da Allah yake sauke rahamarsa ga bayin sa.
Yana kuma yi ma bayin sa gaffara yana raba alheri ga masu rabon samu ya sa imani azuciyar masu imani, amma kai sai dai ka kwanta kawai kana barci ko yaushe.
Bai kula ni ba ya shige dakin shi ya kyaleni ina wa,azina koda ya shiga ya koma barcin shi bai damu da surutun da nai mashi ba.
Sai wajajen takwas saura ya falka yai wanka tare da yin sallah ya fito da shirin zuwa aiki a falo ya samay ni zaune.
Ina ganinya fito na mike zuwa hado mai abin karyawan shi dama na gama yana aje.
Na tsugun na gaban shi na aje tare da mashi ina kwana ya amsa min adakile, ban daga ba daga wurin ba nace dashi.
Yaya don Allah ka daure da yin ibada bai kamata ba magidanci da kai kana wasa da addinin ka, may yasa kuna diyan musulmai kuke sakaci da ibada.
Hannu ya daga min ya dakatar dani daga maganan da nakeyi yayi da hannuwa don haka naja bakina nai shiru tare da komawa gefe na zauna.
Yagama ya fice abinshi lokacin naji gidan kamar an debe min kaya da nauyi akaina na mike na shiga gyaran gida dakyat na samu na gama .

* * *
Kwana biyu banda matsalan komai da shi a gidan sai dai ba sakin fuska akaina wanan bai damay ni ba indai hat zaibar zuciya ta ta samu saida.
Ranan na samay shi zancen zuwa asibiti a duba ni don ina fama da ciwon mara idan dare yayi bana barci da dadi.
Ya kawo kudin zuwa ya bani yace na shirya ya sauke ni indan zai fita nako shirya da wuri na zauna jiran shi.
Sai da ya gama abinda yake yi ya fito muka kama hanya a can wani unguwa ya kaini wani asibiti mai kyau na kudi .
Yace idan zan dawo ga yadda zanyi ga yadda zanyi nace na gane na yanki kati nabi sahun masu ganin likita a wurin.
Can layi ya kawo kaina aka ce nai fitsari aka kuma debi jina na dan aunawa an gama na koma na zauna sai da layi ya sake kawo kaina na shiga.
Ba matsalan komai ba likita yai min yan tambayoyi irin na likita karshe sai ya rubuta min magani sai kuma yadan dubeni yace dani idan ba damuwa yana son nazo da mijina yana son ganin shi gobe.
Banji komai a raina ba nace zan fada mai ya bani wani dan note yace dashi zai zo idan zaizo din na karba nai mashi godiya na fice.
Na dawo gida a gajiye na samu bai dawo ba na kwanta na dan huta don na sayo abinda zanci a hanya da zan dawo.
Ban tashi ba sai wajajen karfe uku na tashi a gagauce nai sallah najira akai la,asar na hada nayi sai na mike na dora girki dare.
Har na gama bai dawo ba lokacin da ya saba dawowa kafin magariba na shige sallah na gama ina sauraren dawowan shi, naji shiru nan na fara tunanen ko ina ya tsaya.
Shiru bai shigo ba har nagaji na kashe kayan kallo na kwanta sai wuraren sha dayan dare naji ya shigo gidan a cikin maye.
Inna lillilahi nayi a raina ina jinshi yana ta hauragiyan shi shi kadai a falon na tashi na kargamay kofan dakina don ma kada ya shigo min dakina.
Haka na kwana ga ciwo ga bacin rai nasan mairaba shi da wanan halin sai Allah duk wani wa a zi da sauransu bai shigan shi don yayi nisa.
Gari ya waye ban fito da wuri ba sai wuraren takwas na fito ina yan aikace aikace na duk da nayi nauyi ban iya dukawa sosai yanzu.
Ya fito yana wani murzan idanu kamar wanda barci bai isheshi ba, ashe shi din ne kuwa don ya na cikin sauran maye har yanzu, .
Dan juyowa nayi na kalleshi na mayar dakaina naci gaba da abinda nakeyi nace mai ina kwana a takaice ba tare da na fuskace shi ba.
Shima yai mamakin a yadda na gaida shi don ba haka nake gaida shiba din yadai amsa min ne kawai don yasan wai fushi nakeyi ke nan.
Ya zauna yana tambaya na abin karyanwanshi na ba shi amsa dacewa dashi ban yi ba har zai yi magana sai kuma ya tuna bai sayowa ba daren jiya da zai dawo gida don a buge yake lokacin kuma masu kaya sun kwashe.
Zama ya dan yi na wani lokaci yai shiru sai can ya furzo iska daga bakin shi yana mikewa yake tambayana jiya kin samu ganin likitan ?
A takaice nace mai eh nagan shi yama bani takarda wai yana son ganin ka asibitin sai ya dago da sauri yana kallona yace.
May zanmai ba ya dubaki ba shine kuma zai ce sai na je ya ganni ni ban iya lalurar su na likitoci don Allah.
Nace to kasani ko wani abin ne yake neman ka din kamaf tai magana sai kuma ya fasa ya karbi takardan dake hannuna yana cewa idan na fita zan biya nagan shi.
Tun wanan lokacin bai kara min magana ba nice ma dana tambaye shi yake cewa yaje yace ya dinga sai min kayan karin jini ne.
Da alama yanzu ya koma ruwa sosai don sai dare yake dawowa indan kuma bai zuwa aiki ya zauna min falo yaita bakin rai a falo yana jin fada.
Zai sha abinda yaga dama a wurin da nai magana yanzu zaiyi cikina da cin mutunci da tonan asiri sai ya gaji ya kyale don kan sa.
Wata rana na tafi gaida mahaifiyar shi gwago na mun gaisa dadi dadi da ita sai kowa yai shiru zuwa can tace dani yanzu komai yai daidai tsakanin ku ko an daina jin korafin ki.
Nai mamaki dajin wanan magana nata datai min nace da ita dama ai ba korafi bane fahinta ne akan addini don akwai karancin illimin addini a kan shi.
Nan ta haye tace wai ita nake fadawa magana akan dan ta nihar yaushe aka haife ni da zan ce zan koya masu addini.
Nidai nai shiru ina sauraren ta har ta gama dama da wuya nazo gidan bamu samu matsala akan dan ta ba bata kaunar a fadi magana gamay dashi ko kadan .
Ban dade ba nai sallama dasu na juyo zuwa gida da kafa na tako nan na hadu da wata yar unguwar mu a hanya muka jera da ita muna tafe muna zuba bayeraba na amma kano aka haife ta ta iya hausa sosao don haka in taga bahaushe take matukar jin dadi a ranta.
Tafe muke muna hira tana tambaya na yaji da kuka take so nake cewa da ita ina dashi ai tazo zan bata taji dadi tana ta min godiya.
Tun daga nesa na hango motar shi nasan cewa yana gida sai dai nayi mamakin may yake yi a gida wanan lokacin haka mun dan tsaya da wata makwabciyar mu suna magana da Mujida har take ce min yanzu na yi nauyi nabar kitso ko ?
Nai dariya nake cewa da ita na daina ma don maigidan ne ya hana nai mai kitso a gida .
Ta rike baki tana mamakin halin maza tace shi bai ganin baiwa ne daga Allah na hanyan samu yai maki zai hanaki samu nan dai muka wasan ce muka wuce ita kuma ta kama gaban ta.
Mun zo kofan gidan na tura kofan yana bude sai nace ta jira ni a kofa na dauko mata don kada na shiga da ita kuma ya zama min fitina wurin shi .
Sai ta tsaya a waje tana jirana tana ce min karfa ki shiga mai gida ya rike ki ki manta dani a waje.
Kunsan yare idan yana jin hausa iya yin gare su shi sai ya nuna yafi bahaushen iya hausan ma ga kuma mutane suna kallon mu tana jin dadi.
Nidai na wuce ta ina dariyan abinda naji ta fada zuciyana cike da mamakin abinda ya dawo yi gida da ranan nan haka.
Don dama da sunan zan wuni gida gwago na tafi sai yamma zan dawo ta ban samu fuskaba do haka nai shawara indawo gida kawai in nemi abinda naci don har na fara jin yunwa ko.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button