BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINABU IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,
????????2️⃣4️⃣????????
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , , , , , ,
Mun isa garin mu garin mu an shiga sallah magariba kafan mutane ya dauke sosai mota ya tsaya dani kofan gidan gwagon ummi na.
A nan aka sauke min kayana kaf sai faman tabayana takeyi lafiya kuwa nakai ma driver ruwa nan dai na fada mata tsaye muka wuce gidan mu.
Nan aka karasa sauke min kayana nai sallama da drever na shiga gida tunda yaran gidan suka kyala ido suka ganni suka ce ga Safiya nan da nan na cikin daki suka firfito waje suna min sannu da zuwa.
Dakin Ummina na nufa yayin da aka shigo min da kayan da nazo dashi ciki yar jakar kayana da tsaraban da nazo masu dashi.
Ni bani sanin cewa na sake masu amma su suna ganin wai na zama wata yar birni dani take inna wani kishi ya tarsu a zuciyar ta na yadda na canza.
Lafiya kalau suka tare ni sabanin ummina da ta shiga zargin zuwana gani da juna biyu a jikina kuma.
Mama tazao muka gaisa take tambaya na kowa nace duk suna lafiya take cewa ashe da sai dai muji haihuwan ki kawai don bamu ma san kina da ciki ba.
Murmushi nai mata kawai muka gaisa ta fita daga dakin ta koma ta aiko min da abinci daga wurin mama din.
Ban iya cin komai ba sai kunu da na nema don ummina bata rasa kunu a dakin ta.
Baba ya shigo gida daga masallaci yara suka tare shi da cewa safiya tazo baba cikin mamaki yake tambaya da cewa Safiya ?
Ya nufi daki Ummi yana tambayana nazo lafiya nace Alhamdullahi sai da ya tambayi kowa har Ahmed din da kan nesa.
Sai kuma ya dakatar yana tabmbaya na da lafiya dai na ganki ke kadai ina mijin naki yake ne?
Ban ji tsoro shi ba nace dashi yana gida baba ni kadai nazo, kamar zaiyi magana sai ya juya ya fice dakin na mu.
Yan gidan mu suna baibaiye dani har wani lokaci sannan suka dauke kafan su.
Nasan ba komai yasa sukai min haka sai tsaraban da nazo masu dashi wancan zuwa da ni tare da yaya sani.
Har lokacin da suka barni dakin ummina na min kallon zargi sai dai batai min magana ba sai da na dan kimtsa na samu wuri na kwanta don a gajiye nake sosai.
Ban falka ba sai cikin dare na falka da tunane a raina barkatai na yadda zamu kwashe da mahaifina gashi daga zuwa ba abinda ya fara tambayana sai Ahmed din da mahaifiyar shi.
Na dade a haka ina tunane sai zuwa asuba wani barcin ya dauke ni kuma har na makara da sallah sai da ummi na ta ta tadani.
Nayi sallah na fito na gaida iyayyena na koma daki don baba bai shigowa gida sai hantsi ya fito yake dawowa daga masallaci.
Ummi na samu tayi zaune tana tunane ita kadai a dakin na samu wuri na zauna sai tace min yar nan lafiya kika zo gida a haka yadda kike nan ?
Kuma ba a samu wani ya biyo ki ba kika biyo hanya ke kadai haka gari ba kusa ba ?
Kafinta gama maganan ta hawaye ne ya cika min ido na cikin kuka nace mata ummi saki na yayi yau kwana hudu kenan yace na bar mashi gidan shi .
Salati ta saka tare da dafe gaban ta tace yasake ki ka ce fa za tai magana sai kuma naga ta mike kawai ta fita dakin.
Na bita da kallon tausayi har ta bace min ashe dakin mama ta tafi ta kirata sai gasu sun dawo dakin cikin rudewa.
Mama a rude take tambayana Safiya may ke faruwa ne wai ni dama tun jiya da kika zo nake zargin wani abu.
Ban boye masu komai ba duk yadda mukayi na kwashe na fada masu da abinda gwagona tai min duk ban boye masu ba.
Salati mama ta saka itako ummi na sai kuka takeyi ba tsagai tawa mama ne ta samu bakin cewa amma in haka Asiya tai muna taci amanan zumunci wallahi sai Allah ya saka maki.
Inna da yarta ta fadawa taji ummi na kuka kuma mama na dakin mu ta kasa gidin zama taje ta dawo a tsakar gida don taji may akeyi.
Mama ne ta kirata sai ko gata tazo nan suke fada mata abinda ya faru dani ummi dai bats samu bakin magana ba sai inna ne tace adai binkita aji gaskiyan maganan.
Tunda naji ta fadi haka nasan zata iya zuga baba a kan maganan don ta wuce nan kadan ne daga cikin sherin ta.
Shigowan baba gidan yasa suka fito daga dakin mu dakin Inna yake ta bishi dakin ko may ta fada mashi sai gashi ya fito yana cewa ina Safiyan take.
Nan ya fado dakin mu ya samay mu da ummi na a dakin yace ki fada min gaskiya may ke faruwa dake ?
Yadda na fada masu mama haka na mayar mashi da maganan tiryan tiryan yana saurare na har na gama fada mashi komai.
Yace cikin tsawa ke safiya badai gidan nan ba ai na fada maki tun farko kada ki dawo min gida.
Sai lokacin ummi tai magana tace idan bata dawo ba duniya kake son ta shiga ya koreta akan karuwa tabar mai gida ina yake son ta tafi garin mutane kai bakai tunanen haka ba baka gode ma Allah da ya kawo muna ita gida lafiya ba.
Ke Rabi kifita a idona tun muna sheda juna nida ke ke tsaya kiji bazaki zauna min a gida ba muddin kika kashe auren nan kiji na fada maki.
Ya tashi ya fita yana fada yaya sani ne yashigo gidan yace yaji ance nazo jiya da dare sai kuma ya samu labarin abinda ke faruwa.
Nan yace ai dama nasan haka zai faru ko ta koma da idona fa na samu ya dauko karuwa a gidan kuma yaiwa safiya dan banzan duka.
Amma baba ya hana aiyi magana to ai ga irints nan yanzu cikin kuka nace yaya Sani wanan ba wacce ka sani bane nan na shiga basu labarin abinda suke mun yaya sani yace kai ina wallahi bai yuyuwa gaskiya.
Dole baba ya canza maganan shi na komawa n ki gidan nan sai dai in yasa yaci kudin sune yake kamay kamay.
Daganan Inna ta kirashi dakin da yazo, to to ita kuma Inna zata fara abinta kenan baije ba saida ta sake daga murya ta kirashi ya tafi.
Fada tai mai sosai akan ya canza hali yafita batuna da uwana don ba ysn goyo muke ba yace ni Inna baruwa na da harkanku na kishi, ni kaunata nake tausayawa.
Fita yayi ya tara kan yan uwan baba suka hada mai mitin din kashi akan ya fada masu gaskiya in ya karbe kudi wurin gwagona ne yasa bai iya raba aure na da Ahmed.
Nan baba ya kara yin fushi ranshi ya baci sosai ya kumbura sosai yahau yace diyar su ko diyar shi da zasu tsure shi akaina.
Yamike yana fadin yau yau din nan zan bar shi gidan shi in koma gidan mijina ko mu bashi gidan shi nida uwata.
Allah ya taimake ni yazo gida sai ga su yaya sani sun shigo yace infito da kaya na inbar mashi gidan shi in kuma ban komawa gidan mijina mu fita mai gida dani da ummi.
Fitina ya tashi si yaya sani suka ce mu zauna kada muje ko ina ya shigo har dakin mu zai doke ni mama da ummi suka taso mai sukace idan ka dake ta da tsoho ciki haka wani abu ya samay ta sai an daure ka a garin nan.
Sai jikin shi yai sanyi ya dauki kayana dake gefe yafita dasu waje gidan ya watsar yaya Nura ya kwaso ya dawo dashi ciki yace haba baba wai kodai Safiya ba diya cikin ka bane ?
Yaringa fa tun tasowan ta bata da gata a cikin gidan nan kamar kowa kun tsane ta ita da uwar ta may yasa baba kake mata haka kai kayi su İnna suyi ?
Sai jikin shi yai sanyi yabi yaranda da kallon mamaki Yaya Sani ya karasa kwaso min kayan ya shigo dasu gida.
Ya rasa abinda zai yi ya fice yana fadin sai sun bar min gida yau ita da uwar ta kowa yai mata tsaye a garin nan.
Nan ne gidan ubanta basu zuwa ko ina inji yaya sani haka kawai ka bayar da yarinya ana mata wullakancin da aka ga dama amma kamar bakai ka haifeta ba.
Sai ga yan uwan shi sun shigo maza da mata nan suka taru sukai mai tas a kan mu suka ce sai sunyi karan shi ga hukuma idan ya kore mu ni da ummi gidan nan ai ba kaina aka fara aure ya mutu ba.
Nan ya fice gidab yana banbami kowa na mai tirda halin shi itako ummi ta hada kaya wai zata bargidan aka taru har gwagon ta da ta shigo akace ina zata tabar yar ta da tsohon ciki haka ?
İna waje tsugune a ina kuka mama ta fito tace a hasale tashi ki shiga ciki kin zauna waje kina kuka ba inda zaki tafi.
İnna sai wani kallon banza take min ita da diyan ta don ba haka suka so ba sun so baba ya kora mu ne yadda yai niya.
Muna sauraren dawo wan baba muji may zaice sai muka ga ya dawo bai ce komai ba ashe maigari ya samu labari ne yai mashi tas gwagon ummina ta kai karan shi wurin shi.
Sai dai bana fitowa waje in kuma gari ya waye na gaida shi da kwana baya amsa min sai ya kawar da kanshi yaki kulani wanan abin ya matukar tayar min da hankali a gida.
İnna ta shiga sake maganganu a gidan wai sai bakin ciki na ya kashe masu miji inda basuyi hankali ba.
Sai yarta ta karbe da cewa wallahi sai dai ta kashe uwarta ba mahaifin mu ba ita da ta hana ta zaman aure, ai da har wani jin kai ake muna an auri dan birni za a tafi birni.
Ban saurare su ba don ina sharan kofan mune mama ce tace sai ko makiyin Allah bai fadin haka ga Rabi.
Don kowa yasan yadda ta nuna kin ta ga auren nan abu dai ne in an fi karfin ka baka da yadda zakayi sai hakkuri amma zancen ta wa mutane hawan kai karya ne.
Nan dai fada ya kaure a tsakanin su koma sai da suka dauki lokaci suna yi suka dakatar don kan su.