BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

* * *
Faiza na shiga dakin anty tace ta samu wuri ta zauna sai da ta kai zaune tace da ita yanzu yaran nan ke fada min abinda ya faru da bana nan.
Shi nake son ki fada min komai nan ta fara fadi yaran na tuna mata wani abin har ta kai karshen zancen ta.
Tace wanan yarinyar sai na fito mata ta bayan gida zamu zauna lafiya bata kara furta wani abin ba sai faiza da ta mike ta fice daga dakin tana masu yan biyu wasa.
Hankalina yanzu akwace yake babu abinda ke damuna araina Fati ce kawai matsalata ban kuma kulata bayan gaisuwa da yama kamar na dole a tsakanin mu babu abinda ke hada mu da ita.
Nayi wani haske na kara kyau sakamakon mayuyukan da Anty ta sayo min in dinga amfani dasu a maimakon vesiline da nake shafawa da.
Wanda ko vaseline din ban damu da shafawa da don oilyskine din da nake dashi sai dai ina da dry face amma haka nake barinsa ba gyara.
Nan ko anty ta maysa min son ita yar son kwaliyane taki jinin taga mace bata gyara fuska ba ko jikin ta tun ban iya ba dole na kowa duk kowa da ba inda nake zuwa daga gida sai gida.
Duk wanan halin da nake ciki nakan tuna da halin da rayuwa na yake ciki zamana kenan ba karatu ba aure tare da ni.
Duk da anty na iya bakin kokarin ta wajen ko dayaushe takan muna nasiha da gargadin mai kyau da nagarta .
Babu irin wanda batai muna badon komai ba ba sai don jin tsoron Allah takance ku kama kan ku daga duk wani nauin shiga tarkon shedan
Takance duk kanku amma kuke a wurina don haka ba zan yi sakaci da tarbiyan ku ba don baku gaban iyayyen ku.
Ta kuwa sa a don duk kan mu babu wanda baya daukan nasihan ta dan dama Fati wani lokaci sukan kwasa wajen saka tufafi sai taso tace zata saka irin na kabilu nan sukan kwasa da yar nata.
Bayan ita bata da wani matsala da kowan mu gashi yanzu zuwa na zatafi hankalin ta kwace don tasan yaran ta zasu samu kulawan da ya dace ko bata gida.
Don ni dama haka nake dayara kona waye sai kaga atake yaro ya lake min a jiki bai damu da uwarsa ba koda na zauna gida akwai yar makwaciyar mu data lake mun duk safe da an mata wanka zata zo gidan mu sai da yamma indan dare yayi zan maida ita gida.
Amma naiyyanar ciwon dake jikina sai uwar ta hana yarinyar zuwa wanda nasan aikin Inna ne don dama tana jin haushin hurdana da matar.
Dadine gashinan sai abinda mutum bai so a gidan anty mijin ta kuma baya kasan tun zuwa na wai yaje US wani aikin suna sojoji amma kwanan nan naji antyn tana maganan dawowan shi kasan.
Don haka muke yi yadda muka ga dama a gidan babu mai takura muna amma naji Faiza na fadin yanzu yaya zai dawo gidan zai koma ba dadi don in yana nan babu wali a gare mu.
Ni dai dama ba sanin shi nayi ba don haka ban damu ba don koda yana nan ba ruwa na sai in fake ma daki inda har yana gida baiko ganin giccina a gidan nace a raina.
Muna zaune falo da anty take cewa wani sati maigidan zai dawo kuma tana ganin shida sulaiman zasu dawo.
Faiza tai saurin cewa harda shi zai dawo anty tace ba dole ba yana zuwa ya zauna a kasar mutane gashi arzikin shi sai kara habbaka yake yi yanzu ai gara dai ya dawo gida asan abin yi kan case din shi.
Kamar yadda anty ta fada hakane satin da muka shiga bamu da hutu a gidan don shirye shiryen taron maigidan da kanin sa da zasu dawo kasan.
Kusan aikin nice a gaba don banda kasala akan aiki duk yadda yake kuwa kafin wani lokaci mun hada komai yadda ya kamata muyi.
Sai a wanan lokacin naga Fati na rawan kafa don har takan dan saka hannun ta ga aikin da mukeyi ayi tare da ita.
Tai ta faman murna tace ance harda Uncle sulaiman zai dawo ashe gidan namu zai cika ke nan kwanan nan.
Da yake ba hira muka saba yi da ita ba babu wanda ke kulata har tayi ta gama sukiburutsun ta ta bar wurin.
Don ba sabawa tayi da irin haka ba don haka bata da jimirin dade wa tare damu a falon ranan da zasu dawo kuwa tun safe muke murzan aiki sai yamma muka gama kowa yaje yai wanka kafin shigowan shi.
Tun da nai wanka na jawo dogon rigata na saka a jikina na koma nabi gado na haye don dama a gajiye nake don mun sha aiki sosai.
Ban fito ba ina jin ana ta hayaniya a gidan nasan matafiyan namu sun iso kenan zuwa dare anty ta leko daki na tana cewa najiki shiru ga bakin mu sun iso gida lafiya har sunci abinci baki fito ba ke .
Nai murmushi nace sun iso lafiya anty tace kalau suka iso nace da safe indan sun huta mu gaisa dasu ai wani kallo tai min.
Tace amma Safiya baki ko kyau ta min ba in kin ce sai gobe mutum ya kwaso gajiya na mike zubur nace tuba nake anty ta dan harare ni tace ke kika sani ai.
Tace ai har uncle din yara ya tafi abishi don shi dama bai son yawan magana na fita da zumbulelen hijabina yana shirin tashi sai gani shi kadai na gani a wurin sai anty da yaran ta har kasa na kai ina cewa daddy barka da dawowa.
Ya juyo da sauri tare da amsawa yana kallo na yace Safiyar taki ke nan ashe ma karamar yarinya ce haka yace mun samay ku lafiya nace lafiya kalau.
To yaya hakkurin abinda ya faru aita hakkuri haka duniya yake dama ba komai ne ke zuwa wa mutun daidai ba a sanyayye nace nagode a huta gajiya don har idona ya kawo kwalla ko.
Na juya zan tafi naji anty tace dani Safiya a rage kayan nan daga wurin nan na juyo na fara kwasan kayan ida ba wani cin abincin sukayi ba sosai dan tabawa sukayi suka barshi duk uban wahalan da mukaci na aikin yin shi.
Na saka na fridge a cikin sauran kuma na adana su inda ya dace a jiye su san nan na koma dakina na rufo Asuba ta gari indan tunane ya barni nai barci yadda ya kamata

Yar uwa ina zaki da hakki a kan ki na mutane ance ba a yafe ba baki barin turawa kina daukan nauyi a kan ki,
Karatun nan fa ba dole bane kiba kanki lafiya mana da daukan nauyi don neman suna kike turawa ko don kina ganin haka ba komai bane.
To nace Allah yai min gagawan isa ga mai fitar min da novel waje .

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,

????????3️⃣2️⃣????????

YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,

Washegari muka hade a falo duk kan mu sai anty dake wurin mijin ta Fati sai faman murna take yi uncle Sulaiman ya dawo,
Hararan gefen ido Faiza tabita dashi tace wai kina ta murnan dawowan Sulaiman wanan dan bakin rai jiya kin ga ya dubemu ne ma.
Kai wallahi turai ya karbeshi kin ko ga yadda ya kara girma yai wani fresh dashi kamar bashi ba don Allah.
Faiza ta watsa mata dan harara tace yanzu ai kanki ake ji shi baki ko isheshi kallo ba, ta bata rai tana fadin oho dai ko bai san ina yi ba wata rana zai sani ai.
Mako uku cur da dawon su amma sau biyu naga daddy a gidan haka wanda Fati ke maganan shi ko yaushe ban taba ganin shi ba kuma sunce yakan shigo gidan wani lokaci amma Allah bai taba sawa mun hadu da shi ba.
Yau ya shigo gidan anty tai mai tayin abinci yace bai jin cin komai a lokacin kai ta girgiza tace wai kai har yanzu kana nufin baka fitar da zancan Samira a rayuwan ka bane ?
Yai murmushi yace kai samiran may can ai ni yanzu in ba lokaci ba ban faye kawo ta a raina ba sai dai ai kin san yazama dole ba zan taba mantawa da ita bane.
Anty ta nisa tacd dashi Allah ya sauwaka amma don Allah ka rage yawan tunane ka koma alamarin ka kamar kowa ita fa har naji ance tayi wani aure ko.
Yace nima haka naji gun wani dan uwan su can.
Ta dade tana dan kallon shi sanan ta gyara zama tace na cewa dashi ya kamata ka manta da komai hakana ka samu wata wace kake zuwa wurin ta ku shirya.
Sai yaneme ya katse zancen sai ta hana shi samun damar yin hakan tace kyale ni har in gama tukun yanzu sulaiman da hankalinka da ilimin ka da komai kaifa ka iya sa wani agaba kai mai fada idan kaga zai kauce irin haka.
To yaya za a ce kai da kan ka ke irin haka kuma.
Kar fa ka manta Allah yana sane da komai na bawan sa shekara biyar kenan ka kasa cire hafsat a ranka sau kace ba musulmi ba ?
Haba sulaiman shi fa musulmi da tawali,u aka san shi saboda hadisi ne ingantacce daya tabatar muna da hakan imanin dayan ku baya kammala har sai yayi imani da kaddara mai kyau da kuma akasin hakan.
To what come over you ?
Sulaiman
Da zaka manta da duk wanan a ranka ?
Gaba da daya lamannin shi suka sauya a lokaci guda ciwon da dade yana cin zurciulyar shi ya dawo mashi sabo fil, wanan dalilin ne yasa dama yake gudun gida don kowa na shakkun fada mai zancen aure.
Ko ita kanta anty sai daga baya taji dama bata dauko mai zancen ba don kawai ganin yadda ya sauya alokaci guda.
Ta kalle shi a sanyayye tace sulaiman ban dauko wanan maganar ba don in tayar maka da hankali amma kayi hakkuri kayi tunane akai.
Kar kaga na dauko ma maganan da kowa yake gudun fada maka nayi hakane amatsayi na wacce muka shaku dakai don zaman ka a haka yana damun kowa.
Ya mike don bai son maganan yai nisa yace zan fita sai na dawo sai dai ba lalle ne in dawo kusa ba don ina son in leka bauchi kwanan nan.
Ba damuwa haka na da kyau ai aje gida adubasu yafi amma kayi tunane aka magana na don Allah shi yafi.
Ya sauke ajiyan zuciya tare da karfin halin fidda murmushi a fuskan shi yace zan diba madam ni zan tafi tace aiko danafi kowa jin dadi wallahi.
Ta sake cewa yau dai kaki taba abincin gidan na mu ya dan yi murmushi yace mata yau bana jin yunwa ne shiyasa.
Ya fice a sanyayye tabishi da kallo tausaya mashi daidai lokacin Fati tashigo get din gidan bai ko kalli inda take tana gaidashi ba yaja motar shi zuwa wurin da ake masa aiki.
Ta shi go da yar fara an ta a fuskan ta tana cewa ashe uncle yazo gidan sai dai kuma bai dade ba ya wuce kuma ?
Anty ta kalle ta fuska daure tace ke Fati ki saurare ni dakyau kiji may zan fada maki naga kina wani rawan kai tun zuwan Sulaima.
To ki kama kan ki don sulaiman ba ajinki bane ya wauce sanin ki ki tsaya a matsayin ki idan kina son mu rabu lafiya dake ke ina ma kika ga haka zai yuyu dube ki ki dubeshi ina zaki hada kan ki dashi.
Kuma ni ina auren dan uwan shi ina kika taba ganin an yi hakan sai ta turi baki gaba tana cewa damay yafini kuma ni ba mace bane halan ?
Ta shige tana kumkumi ta bita da harara har ta bace mata dagani tana sauke ajiyan zuciya ina fitowa daga daki na.
Nace anty ashe kina zaune nan ban sani ba dana fito na taya ki hira ai tun dazu.
Ta kara sauke ajiyan zuciya tace ai bani kadai bane nida uncle din yara ne yanzu ya fita daga nan .
Nace ayya aiko da na ganshi kullun muna samun sabani sai ya tafi nake fitowa har yau ban sanshi ba .
Tace aikuwa da kinga shi yaro mai taken zamani don Sulaiman abin son a san shine bari rana da ya shigo zan kiraki ku gaisa don yace zai tafi gida ya duba su ya dade rabon shi da gida.
Nace Allah sarki dan uwanki ne anty ?
Tace a a dan uwan mai gidan ne iyayyen su guda sai dai tasu tazo daya da manjor ne kawai sai muke dasawa da shi sosai.
Bai iya boye min komai nasa nima haka shiyasa nake son shi da komai nasa don shawaran shi baya wuce ni shima.
Nan muka zauna tana ta bani labari da irin arzikin da yan gidan su daddy ke dashi da sauran su har Faiza tafito ta samay mu anan itama ta zauna.
Fati bata fito ba sai da yamma lis ta fito tana jan kamshi Faiza ne tace yau may ke faruwa da yar mulki ne naga tun dazun take fushi a gidan ?
Anty ta ja tsaki tace rabu da mara wayau kawai bata san abinda take yi bane shiya sa sai gata ta fito a fusace tana fada wai waya shiga dakin ta da batanan ya dauko mata hand dryer din ta.
Faiza tace itace don Safiya ta karbi nawa kuma bata bude kofa ba lokacin shiya sa na dauko naki din.
Nan ko ta shiga fada ta inda take shiga ba nan take fita ba sai da anty ta dakatar da ita da cewa.
Ke Fati kin ishe ni wallahi haba ke kika saye shi ko ni da zaki saka mutane a gaba kina masu fada haifan su kikayi komay ?
Don haka ki shirya kayan ki gida zan maida ke nagaji wallahi duk naji abinda kikewa Safiya tun zuwan ta garin nan ido kawai nasa maki inga gudun ki.
Tun farko ina sai da na hada ku nai maku nasiha amma kika shure magana kina yadda ran ki yaso dasu a gidan nan.
Wai halan kikai Faiza matsayi ne agidan da zaki dinga hura ma mutane hanci yadda kike so ya zama dole in mai dake gida don ban iya zama da wanan iskacin naki haka .
Jin anty na ambato gida yasa ta sausauta maganan ta ita ko faiza kai ya fasu jin ance tafi kowa matsayi a cikin mu sai wani budawa take yi.
Nan dai anty ta kafe akan lallai ta shirya ta maida ta gida sai na shiga ba anty hakkuri tana ta faman fada da ita.
Ds kyat na samu ta hakkura da zance sai dai tace wallahi ta shiga hankali ta don ta gaji da ita a gidan
Tun wanan lokacin ta shiga hankalin ta da kowa dama ba mai shiga tsabgan ta cikin mu don haka bamu damu da ita ba.
Da anty zata dawo ranan sai ta sayo min nawa in huta da aron nasu da nakeyi tare da yan sayayyen kayan makeup dina.
Zama na a gidan yasa yanzu zaka ga komai a gidan tsab don kai aiki iyakan ta girki nice ke tsabatace gida kafin duk su tashi na gama komai har in kama mata yin girkin kuma.
Wanan abinda nakeyi shiya na kara shiga ran anty sosai tana tausaya ma halin da nake ciki takan kaini amsan magani secretly ba tare da kowa ya sani ba a gidan.
Kuma ban taba jin wani ko ganin an kyan kyankyamayni ba a gidan zama suke dani ba wani nuna rashin yarda dani gashi bata rage ni da komai ba na fannin rayuwa kuma.
Sati uku da maganan mu ina daki kwance yan biyu ta tashigo da gudu tace wai inji mummy su inzo .
Na dauki dan kwalina dake saman gado nai rolling din kaina dashi tare da dan gyara fuskana kartai min kwankwami rashin gyara.
Na fito su biyu na samu a fali sai dai may shi ya hada baya ban iya ganin fuskan shi a lokacin.
Gasu yan biyu sun na wasa da hannuwan shi sai dai mai shi fari ne soll da ganin shi yan biyu tana ta jan yatsun hannun shi na iso wurin tace yauwa Safiya ga uncle yau a gidan.
Sai ya juyo da sauri yana kallon wace akace ma safiya din don bai taba jin sunan a gidan ba sai yanzu.
Juyo wan shi mukai ido biyu dashi sai da gabana ya fadi don ban taba ganin namiji hadade irin shi ba nan dai na gaisheshi ciki kunya kunya.
Ya amsa min da lafiya lau kawai ya juya yaci gaba da wasa da yaran dake damun shi nace anty gani.
Tace shike nan dama kiran ki nayi ku gaisa da uncle din yara da baki sani ba sai nai murmushi na juya na barsu wurin daya fahinci na wuce.
Sai yace ita kuma wanan din wacece ita anan gidan take itama da zama ?
Tace budurwan da nai maka kamay ke nan yace kai haba madam kikan fara maganan ki don ki koreni ko.
Tace daga maganan mace zan koreka wai ko sai mun kaika mararaba mun ma wanka ne zaka daina tsaron mata.
Yace kai don Allah bari wanan ma ta gama secondry ne tace tun yau she ta kare Allah da gaske nake yi inda kana ciki sai in kama ma kawai musha buki.
Take ya daure fuskan shi alaman ba wasa a tare da shi tace kai ke nan da an maganan aure sai ka bata rai may kake nufi ne wai ?
Bai bata amsa ba sai ci gaba da yayi da hira da yaran dake gaban shi sai da ta kawo mai zancen aikin da akeyi mai ta samu ya sake fuskan shi.
Ni ko tunda na juya na wuce ina ta mamakin haduwan wanan mutumin da anty tace dan uwan daddy ne mijin ta kuma wai may kudi naji anty na cewa.
Na gaji da tunane na watsar da zancen na kama sha anin gabana daya damay ni kwai sai ga fati ta shigo dakina abinda ban taba gani ba tun zuwa na gidan.
Tana shigowa ta fada saman gadon dakin nawa da yasha gyara sai kamshi ke tashi a dakin tako ina na dakin.
Safiya kin san kowa yau ina cikin farin ciki ga uncle can a falo yazo tun dazun yazo yana falo na dade dakina ina leken shi ta fada saman gadon tana wani irin dariya.
Nikan kallon mamaki kawai nake binta dashi don abin ya daure mun kai sosai tace wai kin san wani abune safiya na gyara zama tare da cewa aa.
Tace wallahi anty tana kawo min kubsawa don sam bata son zance da guy din nan ni kuwa duk yadda zanyi in ga yaso ni sai nayi kin san abinka da yan uba.
Sai nai saurin kallon ta don jin kalamin ta gamay da anty duk wanan halarcin da take mata amma wai tana kiranta da yan uba.
Ta kara lumshe ido tana ce min guy din ya hadu ne sai ma in kin ganshi wallahi yanzu tashi zan yi in dake kawai in je mu gaisa dashi ko bata so ni ban damu in dai bukatana zai biya.
Nace haka za a yi kije ku gaisa ko ki samu shiga ai ba a bori da sanyin gwiwa tace ai shi na gani wallahi.
Ta mike tana wani juye juye tace yaya kika gani na hadu ko da gyara nace cikin daga kai komai tsab wallahi.
Ta fice daga dakin na bita da kallon mamaki nace oho zamani ina zaki damu mata cusa kai ga maza haka ?
Acan falo tun da anty taga ta tun karo wurin su tace kin ga Fati kira min safiya ta hada ma uncle fruit salad wai abinda yake so ke nan.
Tace anty bagani ba zan iya hada mashi ai tace don Allah ki raba ni da shirmay ki ranan da ta hada masu bacewa kikayi ke baki iyaba.
Sai tace ai naga yadda ta hada din kin ga kira min Safiya nace don Allah ban son shirmay ki hakan nan.
Ta wuce tana mai jin haushi yar uwar nata data kwabsa mata a gaban shi sai gata dakina tana cika tana batsewa tace tana kiran ki .
Niko ina cewa yaya anyi nasara dai ko kin samu magana dashi tace ina yar bakin cikin zata bari ai komawa zanyi ko bata so.
Nace antyn ne yar bakin ciki tace to in ba bakin ciki ba ko zama bata bari nayi ba ta koreni da karfi da yaji ban san abinda take nufi da hakan ba.
Mikewa nayi zuwa amsa kiran anty na je da sallama na ce anty ance kina kirana tace eh kin ga don Allah wanan gwauron zaki hada ma fruit salad wai yake son sha yau.
Ban tsaya ba na juya zuwa kitchen din ya dan kalle ni ta witsiyar ido a ranshi yace ba laifi yarinyan sai dai akwai shamaki a tsakanin mu.
Ban dauki wani lokaci ba wurin hadawa don akwai komai na bukata kankara na jefa yadda zai yi saurin yin sanyi bayan na hada din.
Na nufo dashi nan na tsikayi Fati zaune tare da su tana wani kwarkwasa yar nata nata hararan ta bata damu ba nazo gaban shi na aje yace dani thanks kawai na juya zan wuce..
Anty tace dan tsaya ki zuba mashi nima ki zubo min karya shanye ba sha ba nan na juya na sake dukawa gaban shi ina diban mata kamshin turaren madina dana shafa ya dokan hancin shi sai lumshe ido yake yi cikin sytle.
Na diba na bata na dago muka hada ido da Fati sai naga tana harara na ni dai na wuce abina ban kara juyowa ba.
Sai gata dakin ban bari tayi magana ba nace kai amma Fati kunyi balain dacewa da wanan mutumin gaskiya.
Da da fushi ta shigo amma jin abinda nace yasa ta washe baki tana fadin gaski Safiya nace kwarai kuwa kiyi kokari anty tafahinci ki .
Tace haka za ayi ai don haka sai na zauna ki fada min ta inda zamu bullo mata nace niwa aini yar kauye ce ban san komai ba wallahi..
Da yamma muna falo gaba dayan mu Faiza ke cewa wai ni yaushe Yaya sulaiman ya wuce dazu ne ?
Kafin anty ta bada amsa Fati tai carab tace ai kedai yau ya dade gidan nan sai anty ta balla mata harara tace ke aka tambaya ko kin san wucewar shine.
Wai ke may yasa baki da hankali ne Fati sai tai wani turo baki kamar karamar yarinya nace anty kin sani ko za ayi yar gida ne.
Tai saurin cewa haba Safiya don Allah kibar wanan zance ki kyale ta da shirmay ta can so take mukai ga yadda ba a so.
Ita ke haukan ta nan shi yana da wace zai aura ko ina ma zai kai ki haka kazama dake sai tai fushi ta daga wurin Faiza tace da gaske anty ya samu mata.
Tace insha Allahu muna fatan hakan amma sai komai ya kankama zamu je ayi magana don ba yar kasan nan bace yace.
Nan ta hau murna don jin dan uwan nata ya samu wace zai aura ashe maganan ya fada kunnen Fati dake wuce wa.
Sai da na dawo daki ta samay ni da maganan nace tayi kokarin cusa kan ta dai in Allah yayi ai ba wanda ya isa ya hana ta sauke ajiyan zuciya tace shiyasa nake son ki wallahi don fadin gaskiya.
Ni dai na samu ta fita na rufe kofa na asuba ta gari sai kuma in Allah ya kaimu lafiya muji da wace zata zo min kuma a gidan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button