BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , , , , , ,
????????3️⃣3️⃣????????
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDINE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BAN YAFE BA IDAN KON FITAR MIN DA NOVEL UBANGIJI YA SAKA MIN A KANKI CIKIN GAGAWA.
Wanan abin yasa yanzun muke shiri da Fati don ko yaushe tana dakina muna hira abu daya kullun na yadda zata shawo kan shine a gidan.
Zata shigo ta fadi nidai ina ta mata dariya indan ta gaji ta fice ta koma dakin ta, sai dai abu daya ne wanda ban yarda da shi ba.
Irin yadda take kushe maganan anty ko take sukan ta da munana kalamai marasa dadin saurare.
Don haka sai na dakatar da ita nace idan zamuyi hiran mu mubar saka sunan kowa mudai nemi mafita akan yadda zamu fito mazancen ta da sulaiman din.
Taso tai hushi alokacin amma sai tai tunanen ba ida take kai maganan ta ba tare da wani yaji ba sai gurina, sai gashi ta dawo da kanta.
Ina kwance daki sai gata ta fado min daki tana dariyan jin dadi nace halan mutumin ya shigo ne.
Tai wani far da idanuwa tace dani bai shigo ba tukun amma naji mijin anty na waya dashi wai su hadu karfe hudu nan gidan.
Nan dai mukai shawaran abinda ya dace tayi tabar dakin tana ta murna nikan fitan ta dakin na kwanta abina don ina fashin yin sallah a lokacin ban son shiga mutane.
Kamar yadda Fati ta fada hakan ne yazo gidan bayan hudu ya dan gwauta kadan yana falo da anty daya sama a falon ita da yaran ta.
Tun shigowan shi take faman sake murmushi a fuskanta kamar yadda ta saba indan sun hadu.
Ya zauna suna gaisawa da ita yace komao lafiya ko ta amsa mai da lafiya kalau muke, tace yaya aiki kuma?, ya lumshe idon shi yana cire hular kan shi .
Yace aiki muna kai wallahi yai ajiyam zuciya yace yanzu ma mijin ki ne ya kirani koda yake dama yau ina da niyar shigowa gidan naku.
Sai ga mijinki ya kirani kuma tace ka kwana biyu baka shigo nan din bane ya sake cewa wallahi yau nake da niyar shigowa don ina son in baki wani aiki ne.
Ta nisa tare dacewa tau fa, ina jinka rankaya dade,
See you nine ranka ya dade kuma ni dai kisa a hada min wanan abin don yau dashi zan tafi don ina son shi sosai wallahi.
Mikewa tayi don yaran sun shige don bude tsaraban da ya shigo masu dashi da zaizo don haka babu yaro kusa sai anty taje kirana da kanta.
Tana wucewa Fati ta fito acikin wani irin kwaliya tana kashe ido wai tana mai sannu da zuwa takai zaune a dayan kujeran falon.
Niko ina daki na kwanta wuri daya na dunkule wani iri kamar maijin sanyi idan ka ga yadda na kwanta.
Tabani, tayi tana kiran sunana a hankali, inda na bude ido na sauke a fauskanta ina mai kallonta cikin magagin barci sai naji ta tambaye ni dacewa lafiya kike kuwa kike ta barci haka ?
Na murza idona tare da cemata anty barci ne kawai ya dauke ni tun dazun tace to tashi don Allah aiki zan saka ki don wanan bakin batauren ya shigo wai fruit salad yake son aimashi.
Na sake murza idona nace to anty barin tashi yanzu zan fito ta mike don barin dakin nawa har takai kofa nace ina mike wa Fati na nan ne muyi tare.
Tace Fati ko mashiririciya may zata iya wanan don Allah fito ki hada mashi tunda har yai magana kada ya tafi ba a hada mai ba kuma.
Hankalin shi naga wayan shi baiko san tana zaune a wurin ba ita kuma sai wani gyare gyare take yi daga zaune kamar wacce ake tsunkulan ta.
Anty ne ta iso gurin tun da ta ganta ta daure fuskan ta har tazo ta zauna ba walwala a fuskan ta.
Ta zauna tare da cewa ke kuma may kike anan din kije safiya na jiranki ki kama mata aiki.
Ta juya inda yake tana murmushi tace ina jinka sakon may kake magana akai ne wai ?
Ok dama account dinki nake so inyi amfani dashi in tura ma wani kudi miliyan hamsin mun sai injin ne a gurin sa .
Sai bayan sati biyu zaa fitar da kudin kinga kenan kema zaki iya samun wani abu daga yin hakan .
Tace sulaima ba matsala gayin hakan dagowa yayi yana mata dariya yace idan da matsala ai ba zan saki a ciki ba kedai ki bayar zaki gane abinda nake nufi.
Sai ya fara mata bayani a takwaice yace ashe ke matsoraciya ne kina tsoron kada a yaudare ki ko da irin haka yawancin mutane suke dagawa ina son inga account dinki yana motsine.
Nan ta shiga dariya don ta gane mafusa arlallan business yake son sakata ciki itama nan ta shiga yi mashi godiya daga mata hannu yayi yace haba madam ya idan ban maku ba suwa zan taimakawa ?
Yace sai dai gida da fili danake son saya a Abuja ta saki baki tana kallon shi don jin irin bayani da yake mata na gida da filin da yake so.
Ta sake cewa yanzu sulaiman ga gida ga fili kake shirin saya haka yace ai wanan ba komai bane sai tai wani irin shewa.
Tace iyyye tun yanzu ashe bari mu fara shirin buki ashe,
Dariya ya fara mata yace ba a sayen gida sai za ai aure ki rufa min asiri tun dawowan mu kudin nan nake son in sai gida da fili dasu, don ina yin wani aiki acan Abujan kuma dai ina ganin anan zan zauna don nafi son zama arewa da nan din.
Tace kayi dabara wallahi shawaran da nake ba daddy su kenan ko yaushe amma naga shi ra, ayin shi baison zama arewa sam.
Yace arewan ne babu dadin zama saboda mutane yan sa ido ga abin da bai shafe su ba sai suyi tama zargin banza ba gaira ba dalili kai kana neman nakan ka amma mutane idon su na kanka.
Mijin anty ne yashigo sai suka can za firan suka fara gaisawa dashi a daidai lokacin da na fito dauke da tiren a hannu na da na shiryo mashi.
Daddy din na fara gyarwa sai shi sai daddyn yace Safiya kike ko kina gidan nan ban gani ki sai nike tsamanin ko kin koma ne ban sani ba.
Murmushi nayi kawai sai anty ne ke cewa ita wanan ai in ka ganta waje su yan biyu ne suka fitar da ita dole zaman daki baya isan ta ko yaushe tana ciki kumshe.
Na gama jerawa zan wuce sai naji tace yauwa daddy shine nace ma mutumi na ko zai fada neman Safiya ne ya tsaya yana min kwana kwana.
Don Allah ba sai yar gida gida ba kawai ga mata har gida ya samu ba niba har mijin nata wani irin kallo yai mata nidai na wuce na barsu nan.
Ina ganin sun dade a wurin sai dai ban san maganan da sukeyi ba dagani dai maganan tana da muhinmanci a gare su.
Sai can naji fitan mazan daga gidan wanda ban debe tsamani sallah suka fita yi don lokaci da yayi yan biyu ne tazo take ce min mummy su na kiran su.
Ban tsaya ba na jawo dankwali na dora a kaina muka fito tare da yarinyar da tazo kirana din .
Tana zaune tana hada wasu takardu dake saman table din gaban ta tace kinga bai ko sami tafiya dashi ba yadda yace anan suka shanye abinsu shida major.
Ina kwasan kayan nake jin yadda anty ke ta faman yabon sulaiman din har take ce min wallahi safiya idan na samu nai wanan hadin a tsakanin ku kowa naki ya huta indai Sulaiman ne don bai da matse na tare dashi balle matar shi mutum ne mai sakin aljihun shi sosai wallahi.
Nidai abinda na saba nai mata watau murmushi sai dai a raina nace kardai anty ta zamo cikin masu rufe ido ayi cuta da ita kan abin duniya.
Ni dake da lalura har take zancen hadani da wani wanda baida matsala irin nawa ni yanzu aiko mai irin matsalata banda lokacin shi balle mai lafiya in cuta mai.
Na kwashe kayan zuwa kitchen da zan fito ma ban dawo wurin ta ba sai nai hanyan dakin na don zancen ta ba abin saurare bane a wurina.