BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , , ,
????????3️⃣5️⃣????????
YAR UWA NOVEL DIN NAN NA KUDI NE IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA DON BA A YAFE MAKI BA HAKKIN KARANTAWA BA BIYA.
Tunda nake ban taba zuwa wuri irin wannan ba a rayuwa na sai dai ban nuna ba saboda natsuwan da Allah yai min.
Sune a gaba ina binsu baya a hankali anty tace mu diba mu gani sai ban tafiba nabi bayan anty din wasu jakka da ta kalma take dubawa bata san ina bayanta ba.
Sai nace kai anty wanan kayan zaiwa su yan biyu kyawo sosai ta juyo da sauri tana cemin har kin duba ne?
Jin nai shiru yasa ta juyowa tana fuskanta tana tare da cewa mai kika zaba ne nace ban dauki komai ba kai ta girgiza kawai taci gaba da daukan abinda take so.
Tafiya takeyi tana fadin sai ki zabar ma diyan naki kayan a tare mukaje wurin kayan yara na fara duba masu sai kuma na gaza itace tai ta zama musu kalloli masu kyau.
Batai min magana ba sai wucewa da tayi layin riguna ina biye da ita can ma zaban taitayi tare da atamfofi.
Ni dai har muka gama a shagon banga sulaiman din ba sai nai zaton ya ajemu ya tafi ne to wa zai mai damu gida daren nan haka.
Acan wurin biyan kudi muka hade dashi bai sai komai ba sai turare guda biyu ya dauka bazaka ce tare muke dashi ba yadda ya nuna a wurin.
Ni dai kafana ya gaji da tsayawa sai na fita daga shago na samu bayan wani mota na jigina jikina dashi.
Sun gama suka kwaso kaya niki niki suka fito zuwa motar na tako inda suke na samay su ta dago tana ceman yayi da ake sakayan a both din motan da muka zo dashi.
May yasa kika fito daga ciki nace na zata magana zasuyi ai shine na basu wuri tsaki taja kwai tana bude kofan motan muma muka nufu motar muna budewa.
Har muka iso gida ba wanda yai magana a tsakanin ni da Faiza sai da motar ta tsaya ne muka fito nan muka fara jidan kayan zuwa ciki dasu sai a lokacin naga ashe ba karamin sayaya mukayi ba .
Dakin anty muka nufa dan kai kayan can amma sai tace mu zube su a falo na ta zauna tare da jawo wani laida sai naga ashe nama ne gadade suka saya a wurin .
Tana fitar da kayan tana cin nama hankali kwance ta miko min wani laida shake da kaya tana cewa ungo naki matsoraciya kawai ta kuma mika min wani karamin laida da kayan sanyi da naman ciki faiza kuma ta dauki nata zuwa dakin su kowa ya shige muka kashe wuta muka watse wurin.
Da safe kowan mu ya makara don haka bamu fito da wuri ba ni dai ina kwance bayan nayi sallah sai na koma barci.
Banyi nisa da barcin ba sai ga anty ta shigo daki da hijjab din ta tayar dani tayi na mike zaune tare da gaisheta da kwana takalleni tace safiya kinyi sallah kuwa ?
A girmamay nace nayi sallah anty tun dazun sai tace madalla tashi mu fita gidan nan tun yan bakin nan basu tashi ba mu fita daga gidan nan maza ki tayar min da wa yan nan sarakunan barcin yanzu mu tafi.
Har muka gama muka fice daga gidan basu sani ba wurin gyaran gashi suka tafi don har dani anyi mawa ina ban so amma sai da anty tasa akaimin gyaran na koma kamar bani ba.
Ni kaina nasan gyaran ya fitar min da kyaun surar fuskana don ban taba gyara irin haka ba bamu dawo gida ba sai shabiyu da rabi muka shigo gidan.
Mun samu sun cika fam sai dai ba mai iya yin magana a cikin su dole kuma suke gyashe mu da dawowa .
Nan muka zube a falo tare da muna neman abinci ina yawan mamakin yadda sam anty bata kyaman mu,amula dani kamar yadda gidan mu suke gwada min.
Sai da muka gama ne sai Faiza ta kula da gyaran gashin da akai mun din tace wai dama anty wurin gyaran kai kuka tafi ba tare da muba.
Tace fuska gimtse eh idan kun shirya driver yana waje sai ya kai ku kuma bata da daman da zatai mata wani korafi ba.
Sai harare harare suke aikamin a fakaice bandai kula suba anty ta shige dakin ta sai lokacin Faiza ta samu yi min magana akan fitan mu nace nine nace zan bita da zata fita tace idan kun tashi zaku tafi.
Fitowan anty ne ya hana maganan yayi nisa sosai ta fito tana cewa da au baku tashi kun shirya bane ke kuma Safiya tashi zakiyi ki sallah sai mu fara hada kayan gift din nan tun ba ai yawa ba ki kira funke ta taimaka maki hadawa.
Su idan sun dawo sai su karasa a inda kuka tsaya din don takwas za a fara program din ban son a samu matsala a wurin mu ko kadan.
Mikewa nayi din zuwa sallah nake cewa da su idan sun wuce sai sun dawo ni zan shiga in sallah faiza ne kawai ta amsa min ciki ciki na shige abina.
Sallah nayi na fito anty bata falo don haka na bita dakin ta a inda na samay ta zaune a kasa inda ta idar da sallah tace yauwa Safiya kin ga dauko wancan buhun ki miko min.
Koma da yake ai shi uban gayyan yace ba zai gayyaci mutane dayawa ba a gurin sai nine ma na gayyato mai abokaina da mazan su sai abokan mai gidan da suke garin nan.
Nace haka nake ganin sa kamar baida rigima ai tace haka yake sai kuma wanan kaddara da samay shi ya kara sawa yana gudun mutane yanzu.
Kamar ince wani kaddarane anty sai naga ni may ya shafe ni kuma da zan je wani tambayan abinda bai shafe ni ba can.
Na miko mata inda na aje a gabanta sai tace ai ma mu tafi falo kwaso su duka ki fito min dasu tamike tana cewa ko dai in tai maka maki ne da kwasa.
Ida da sauri nace haba anty barshi kawai zan iya ai basu da wani yawa ta fice inda na fara kin kimo wa zuwa falon inda har ta zauna ko kasa saman center carpet.
Na dauko sauran na samu sufi na farkon nauyi haka dai na ta kwasowa zuwa falon har na gama.
Ba bata lokaci muka fara hadawa dani da funke tana directing din mu ina mamaki a raina wai bukin bude gida da company akewa wanan gift din kamar na wani buki can da ya shahara nace kai masu kudi na shagalin su.
Anty ne ke fadin ko basu yi ba a kara ne safiya naga abin bai wani cika ido ba sosai nace wai anty duk wanan za a ace bai cika ido ba tace kin ko san wa yanda muka gaiyata a wurin ne.
Jakka ne dan na tafiya sai towel da sabule da turare da man shafi da su drinks da snack muke zubawa ako wani bag.
Tsab muka shirya komai yadda ya dace sai tace funke tai ta kwasa zuwa mota inda driver da ya kai su faiza yadawo yana waje sai da aka gama kwasa ta ce in fito mu tafi inda za a kai.
Na gaji amma babu halin in nuna mata gajiya na don ban so ta fahinci hakan daga gare ni a tare muka fito inda yaran har sun fice waje ko.
Nan mu ka kama hanya sai wani unguwa mai nisa tsarin unguwar yafi na su anty haduwa sosai don ginane sai kace a kasan turai mutum yake ga ba yawan hayani ya a wurin ko wani gida a rufe yake.
Wani tsararen gida muka shiga da motan mu tace bude ido da kyau kiga gidan da sulaiman ya kera dan dawowan nan nasu kai kudi suna aiki wallahi.
Nai mamakin jin kalaman anty tace wallahi sulaiman mutum ne dake tsaya ga neman na kasa yaro ne wanda tun farko bai tsaya jiran sai ambashi ba haka ya taso da neman na kansa.
Gashi maraya ne bai tashi da mahaifin shi ba don tun yana matakin karatun shi na farko mahaifin shi ya rasu sanadiyan hatsarin mota.
Dan dukiyan da aka raba masu ne a wanan lokacin ya fara juyawa shine Allah yasa masa albarka har yakai haka yanzu sai dai ya taba aure duka duka watan su shida suka rabu da matar.
Motan mu ne ya tsaya a ciki gidan koma suna tsaye a waje da wasu abokan shi shi ya dakatar da labarin shi da take bani a motan .
Shi da kansa ne yazo ya bude mata motar muka firfito nan abokan shi suka shiga gaida ita wanda da gani sun san ta dama.
Ciki muka shiga nikan ba boyo dama bakauya nake nan ko nai ta zuba kauyan ci wurin kalle kallen gidan.
Nayi mamaki wai wanan dai sulaiman din ne mai wanan gidan haka dana gani mun shiga mun fita ko ina sai faman yaba mai anty keyi.
Niko duk na takura a wurin don ban saba hurda da maza irin hakaba don yawan kalon da suke min din yayi wa a gani na.
Nuna mata nayi na gaji sai tace inje in zauna a mamakeken falon in jira su a nan tare da twins din ta muka zauna a falon nan na ci gaba da ba ido abinci don in samu na karaswa.
Wayana ne yai tsuwa na dako da sauri inda naga ummi na ce ke kirana a lokacin nace Allah sarki ummi taji shiru yau shine ta kira ni don kaida ne a rana sai na kirasu kusan sau biyu ko uku inji lafiyan su.
Nan nake fada mata bamu lagos mun zo Abuja ne da anty wurin bukin bude company kanin mijin ta da za a yi yau tace shi gidan harda wani buki ake mai kuma ?
Dariya ummi ta bani ban san lokacin da na bude baki ina kwasan dariya ba a daidai nan suka fito daga daki shine agaba sauran na bin shi a baya.
Nan nai saurin gimtsewa kamar bani bace mai yin dariyan a farko muna ta magana da ummi inda suka zauna sai na kasa sakewa a wurin.
Karshe dai don in fitar da zargi sai nace wa anty ga ummina su gaisa da ita ta karbi wayan tana murmushi nan suka gaisa ina jin anty nace mata gata nan ina ta bata wahala bamu zauna ba yau tun safe ai Safiya tana da kokari wallahi naji dadin zama da ita sosai ummi.
Sun gama gaisawa ta bani wayan nai mata sallama tare da kashe wayan nawa nan na zauna a takure a cikin su inda anty ta umurce ni da in bude jaka guda suga yadda muka hada kayan ciki.
Mikewa nayi ina gyara gulyalena dake zamewa akaina na dauko jakka guda tare da bude masu sai naji sulaiman din yace kai basuyi kadan ba.
Ban san lokacin da na dago na dan kalle shi ba sai naji anty din tace gata nan ai nace a kara don nasan halinka tace wai ya isa hakana.
Yace No if possible don Allah a kara mana why not na mata a saka zanuwa a cikin sa na maza ku saka masu shadda a ciki kai hamza kaje ka dauko su a cikin dakin nan a zuba.
Daga haka suka fice aka barmu nan muka ci gaba da aikin kara kayan bamu dawo ba sai shida na yamma don mu shirya.
Mun dawo mun samu su Fati na gida itakan anty dakin ta shige tana cewa mu shirya bakwai zamu bar gidan.
A kusan tare suke tambaya na ina muka tafi haka nace mun je inda za ai event din ne don hada wurin sai ita Fati tai tsaki tace to mu wai may ya kawo mune tunda ba a yi damu.
Faiza ne tace a a zaki iya wanan jigilan da Safiya keyi haka ba gajiya tace wane ni kuwa sai fatin tace wai mun ga sulaiman a wurin nace a a bamu ganshi ba ai.
Tace ai gara ma da ban tafi ba don ni shi kadai nake son gani dama ban damu da wasu can ba.
Sai faizan ta harare ta tace hum,umm ashe kina da aiki indai wanan miskilin ne mai yi kamar yana jin warin mata tace wasu matan ba.
Ni dai ban zauna ba shiga nayi sai na samu kaina da dan kwantawa don a gajiye nake so sai yaran ne da suka shigo na tashi dole na fara shirya su.
Ina cikin shirya sune anty ta leko tace da ni aa kunanan da mutanen naki kuna ta fama yauwa safiya sannu da kokari kiyi ki gama sai kema ki shirya.
Tace karbi nan nasan ki da sin dogon riga shiyasa na sayo maki ban baki bane don wa yan nan yan sa idon kada su damay ni da korafin banza.
Na amsa hannu bibiyu ina godiya tace kin ga don Allah ni kuyi sauri bamu da lokaci ban so ma in kai yanzu ba a nan bamu tafi ba.
Nan tafita ta barni ina duba kyawon rigan data bani rigan yakai riga wurin haduwa sosai na ce a raina wai na ko gode ashe idan na koma gida inna sai bakin ciki ya kashe ta.
Tsab muka fito bani ba ba yaran ba ban bari anty ta jiramu ba don a gagauce na shirya simple makeup nayi a fuska na duk da hakan ba karamin kyau nayi ba sosai.
Duk sun fito nice karshen fito wa a tare da su yan biyu muka fito kowan mu in ka gan mu basai an fada ma cewa ga inda zamu ba a lokacin.
Nan ko su Fati aka sako min ido take kowan su ya daure fuskan su, don basu san da rigan da na saba na gani amma nai kamar ban gan su ba.
Nan dai babu tsatsayawa muka fice gidan har da funke gaba dayan mu ba a bar kowa a gidan ba mota biyu mukai tafiya dasu inda nida yara da fati muka shiga mota guda sai anty da faiza da funke a dayar motar.
Da kamar ba za tai min magana ba sai naji tace wai yaya kika ga shiga na ne Safiya na fito kuwa ?
Nace kai ai duk kin fimu haduwa wallahi kin ko ga yadda ki ke wani haskawa wurin nan ashe akwai wanda zai kai ki haduwa a wurin.
Taji dadi ta washe baki tace ina yinki safiya wancan yar bakin cikin cewa tayi wai in saka dayan rigan nan don ta san baikai wanan din haduwa don ta fini fitowa.
Nace ke kyale ta don Allah ita Faiza bata taba fadawa mutum gaskiya ai tace da sauri ashe kema kin gane ta yanzu ni shiya bani shiga harkanta .
Mun isa wurin ba kowa sai anty damu muka karasa duba aikin da akayi bayan wuce wan mu nan muka shige wani daki muka kara gyarawa kafin a fara.
Ni dai kwance nake sai su ke ta heleke su da gwale junan su kamar wasu kishiyoyi can nidai murmushi kawai nake ta masu sai anty ne ta shigo dakin take cewa ai an bude wurin yanzu za a fara don Allah tana son kowan mu ya natsu muyi abu a hankali kada mu bada ita.
Bamu fito ba sai da taro yai taro muka fito muna mara ma anty baya tare da wasu yan uwan su da suka zo daga bauchi sai yanzu na gansu.
Sulaiman din ya fito tare da abokan nan nashi na dazu wanda na fahinci sune dai abokan shi na shakiki na kusa.
Mun fito wurin ya dauki tafi don mc na bayani akan Sulaiman din da dalilin haduwan a nan wurin ni dai biye kawai nake dasu kamar ace in sheka in ruga da gudu.
Don yawan mutanen dake wurin naga anty ba abinda ya damay ta sai walwala take tana ta gaisawa da mutanen wurinta saka wasu matarial sai walkiya take yi a gurin.
Ana ta bayanai akan ki shi din wanene tare da manufar shi na bude company da yayi nan wuri ya dauki tafi rafrafraf .
Sulalewa nayi na fice daga dakin taron na fita waje wani iska mai sanyi ya dake ni na shaka sai naji ina son in dan kadaice ni kadai a wuri daya.
Wani dakali na hango a gefen don haka na nufi wurin na zauna ina kallon masu shige da ficen wurin.
Nace a raina idan mutum na cikin wayan nan har sai ya manta da halin da yake ciki ya shagala da rudin duniya dan dai ma ita anty mace ce mai kula da addinin ta.