BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,

????????3️⃣7️⃣????????

INA ROKON ALLAH DA YA SADA MU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN WATA MAI ALBARKA YAN UWA, YASA MUNA CIKIN YANTATTUN BAYIN SHI, , ,

Bayan komawa yan bauchine gida sai muka fara shirin tafi muma don sam ba mu san zamuyi wanan kwanakin haka ba a abujan.
Har lokacin Fati bata sake min fuska ba cikin ma bataji kan maganan sosai ba don dukkan su basu kusa dan haka basu ji maganan da akayi da kyau ba rana.
Mun fara shirin komawa lagos sai dai har lokacin bamuga Sulaiman din a cewan anty tafiya ya kama shi ya tafi gida.
Shiri sosai mukeyi dole a mota mukai tafiyan don kayan da muka loda na amfanin gida a Abujan dama wasu tarkace can.
Mun dawo da kwana biyu mun warwale gajiya a jikin mu yau anty ta fita aiki Fati tafita zuwa makaranta sai Ni da Faiza kawai a gida.
Na gaji da kwaciya dan haka na fito falo muyi hira da Funke sai na samu Faiza ta rigani fitowa tana gani na take cewa kema kin fito shiru yai yawa a gidan.
Nan na zauna muna hira har funke din sai dai matasalan Faiza shine son ayi da wani a bayan shi wanda ni kuma ban lamunci haka ba sam.
Take fadi wai dama tana son mu samu lokaci ne ta fada min Fati fa ta fara zargina akan ina shishiwa don in fi kowa gun anty dama haka muke da bin bokaye ai duk inda bakauye yake ya san inda bokan kwarai yake ko malam.
Murmushi nayi nace aiko ba boka da malam idan ka gyara alakarka da mutane sai a soka ita tasan wanan don haka take zargin kowa da wanan halin.
Duk hiran da ta dauko sai in kawar dashi don mafi munin sabo shine giba amma ita shine sana,anta yi da wani idan baya kusa.
Munyi gyaran gidan nida Funke kamar ba tafiya muka yi ba munn maida gidan tsab gwanin ban shaawa na koma daki na kwanta ban falka ba sai da maigidan ta dawo ta turo yaran su kirani.
Ckin barci naji suna tadani wai mummy su na kira na, mika kawai nayii na sauko muka fice dakin zuwa falo tana tsaye a tsakar falon da waya a hannun ta.
Wuri na samu naja na tsaya ina jiran ta gama sai na zo na fahinci sa mijinta take waya sai da ta gama ne ta kashe wayan ta maida hankali gare ni..
Anty sannu da dawo wa nai mata ta amsa tare daga mun hannu tace yawa safiya zozozo nan kin ji tana mika hannu wai in zo kusa da ita haka take yi idan abu ya dan ruda ta ko ya bata mata rai.
Banyi nawa wurin karasawa inda take ba ta riko hannu bibiyu tana cewa Safiya kiji min daddy da rigima wai bai fada min zai fito ruwa ba mu shirya mai sai yazu da suka fito wai yake sanar dani sun fito.
Jimun daddy da neman rigima fa safiya ni kaina ma ya kulle ban san may nake ciki ba wallahi yanzu in an gama masu clearing za a kawo shi gida.
Nace anty ba daddy yafi son tuwo ba tace shi ne ai safiya nace akwai komai hade tuwon kawai zan tuka bani minti ashirin yanzu sai inyi warming din biya don dama jiya na hada su.
Tace kai Safiya sai ta rungumoni zuwa jikin ta tana cewa yarinyar nan basan godiyan da zan maki ba amma dai bari komai nake dabban zan fitar maki in daddy ya dawo.
Haka take dason abin ban dariya sai dai kuma indan ta tashi daure fuska ba mai gane kanta kuma sai taga daman saukowa dan kanta da kanta.
Kafin daddy ya iso gida mun hada mai table lafiyayyen abincin irin wanda yake so namu na gargaji na shirya mai tuwon semo sai miyar kubewa danya sai stwee din cow tail dashi zai hada ya ci simple.
Sai abin sha suma na jera su yadda ya kamata da kunun samiya da yake son sha sai kamshi kayan yaji yake yi.
Wanka na shige ina ciki naji jiniyan su ta aiki ta shigo gidan haka yasani sanin ya dawo take gida ya rude da murna don shima daddy kamar matar shi yake bai da matsala ko kadan da kowa a gidan.
Matsala daya ne ba a ganin shi sosai kullon yana ruwa kasancewa shi na sojan ruwa indan ma yana tudu aikin gaban shi ya shamai kai.
Ban fito ba sai da na shirya mai kawai na shafa na zura rigana na fito tari yan shi na samu kowa a falo security din shi na ta shige da fice nace aifa bissimillahi a raina yanzu zamu fara ganin kattan sojoji a gidan ba da dare ba rana.
Can na hango shi yana ta yanka loman tuwo yana kaiwa baki na karasa da sauri ina fadin daddy sannu da zuwa ya dago yana kokarin hade loman tuwon da ya cusa a baki yace.
Yace yanzu nake tambayan ki naga kowa ban ganki ba na dauka kin koma gida ne sai anty dake gefen shi tace ai yau da ta wuce da bakaci wanan tuwon ba aiki ta tsaya yi sai ta shiga wanka kafin ka iso.
Nan dai na gaida shi nai mashi sannu da zuwa da yaya aiki da hanya ya amsa a takaice yana mai ci gaba da cin tuwon dake gaban shi alama ya nuna yana jun dadin kasancewan shi a gida.
Tunda suka shige bai kara fitowa ba daga shi har matar nasa su yan biyun su suna tare dani ranan a wurina suka kwana basu koma dakin su ba.
Duk da daddy ya dawo bai hana anty fita aiki ba da safe sai da daddy ya tashi yai breakfast shi kadai nace a raina mijin ma,aikaciya kenan.
Bai fita ko ina ba muke ta fama da dauwainiyar shi a gida har zuwa lokacin da ta dawo don bata dade a wurin aikin ba ranan.
Da yamma aka fitar da tsaraban da yazo dashi wanda tufafi ne sai kayan ciye ciye irin na kasa shen ketara yazo dasu wannan kan an zube su ne kowa ya ci ya sha iya shan shi da ci.
Daki na koma ina kallon tsaraban ina mamaki dan zuwa na gidan su na karu da abubuwa da dama na rayuwa.
Na tuna da iyayyena da yan uwana dake zaman ukuba saboda talauci kullun ana ganin laifin juna a tsakanin zama tausayin halin da gidan mu ke ciki ya kamani.
Na wani fitina nan har da talauci ke kawo shi ma in kowa na dashi ai ba mai kallon halin da dan uwa ke ciki kowa tashi ta isheshi ma.
Daddy ne ya tsure anty a daki yana tambayan ta game da hadin daya samu labari tana batun hadawa a tsakani na da sulaiman.
Kin fi kowa sanin halin da yaron nan yake ciki amma shine zaki dauki yar mutane ki hadata dashi don kwadayi komai yaushe kika fara wanan halin na marasa imani ban sani ba.
Idan yarinyar ta gane an cuce ta kina ganin ba zatayi kuka dake ba kai har ma da mu duk abin zai iya shafa nan gaba.
Haba dai daddy may zai sa da hankalina nayi irin haka ga yar mutane may tai min yarinyar nan ai in babu godiya to kuma babu fallasa.
Ta sauke ajiyan zuciya tana cewa dashi matsalar su daya da sulaiman domin ita ma Safiya postive ce da sauri yace may ne ?
Tace wallahi kamar yadda shima ya samu ta sanidan aure haka itama ta samu gun mijin da aka aura mata dan uwanta nan dai ta shiga bashi labarina yana fadin subbahanallah.
Yanzu wanan yarinyar mai hankali haka aka dauka akabawa mashayi ya cutawa rayuwanta subbahanallahi wallahi dai ana cuta a duniyan nan.
Yana kada kai yana fadin wallahi ta ban tausayi gaske nake ganin ta shiru shiru ashe da abinda ke damunta a rayuwan ta.
Ya kara nisa yace yanzu na fahunce ki idan kinyi hankan kin taimaka masu sosai don sulaiman idan a biye masa baiki ya zauna a haka ba ba aure.
Tace ai shi na gani don haka kamar yadda kowa bai san da halin da suke ciki ba sai muyi rufa rufa a daura kawai ta tare an wuce wurin Allah kadai yasan gawan fari tsakanin mu da su.
Nan dai suka kara tatauna yadda zasu fitowa zance don kada a samu matsala a wani bangaren a taru a rufawa juna asiri.
Mako shi kusan uku tun a abuja daya bar mu ya tafi bai zo gidan ba wai ashe tafiya ta kamashi ya ketara waje sai yanzu ya samu kan shi ya dawo nigeria din.
Ranan jumma daidai an sauko daga sallah sai gashi gidan ya shigo babu kowa a falon gidan sai nauran kallo da yake aiki shi kadai a falon.
Goran ruwa yaje da kansa ya dauko a fridge ya dawo ya zauna yana sha sai ga funke ta fito ta ganshi a zaune da sauri ta gaida shi don tana son zuwan shi don dan abinda yake bayarwa a bamu bayan tafiyan shi.
Ta juya bayan ta gaida shi zuwa kiran Anty a sama dakin ta sai gata da saurin ta tana fadin oyoyo da karamin mai gida.
Yace ai nayi fushi tun yaushe nake nan zaune sai ni da kaina na dauko ruwan da zansha gaskiya gidan nan yana bukatan kari don gidan yai maki girma ke kadai dole yaya ya kara wata.
Tai wani dafe kirji tana cewa waini dakaina kawa Allah ka huce ina ni ina amarya yanzu a gidan nan.
Nan fa nabar su Faiza ashe duk sun shige subar falin ba kowa a wurin wane ni in kyale ka haka koda yake zuwa bazata kai ma kai muna ai yaudin.
Yace kuma hakane fa to na dai huce tunda anfini gaskiya ya nisa yana gyara zama dakyau yace wallahi nima dai haka tafiyan ya kama ni gashi tun a abuja bamu hadu ba sai naga ban kyauta ba ko ban gajiya ban samu yi maki ba .
Tace kai haba dai ai nasan yadda harkan naku yake bawani lokacin kanku kuke dashi ba sosai mu dai tunda kana lafiya ai shike nan.
Ya sake mika hannu yana daukan ruwa gami da bude roban ruwan yace wallahi lafiya nake sai dai abinda ba a rasa ba dai.
Tace bari a kawo maka abinci shima captain tunda suka tafi masallaci bai dawo ba shida twins yace ashe suna can yau ya dauki rigima .
Tace wallahi rankai dade abincin fa your fovourite akayi yau fa a gidan don nasan kaima kaman dan uwanka ne kana son cin tuwo shi Safiya ta girka mashi.
Dam gaba shi yai mugun bugawa jin ta ambaci suna na take yawan mafalkin da yake akaina ya fado mashi a rai don bai ko son ya ganni don bai son zuciyar shi yana fada mashi karya a kaina.
Ban san da shi ba a wurin don anty ta kirani na fito da dan kwalina a hannu ina kokarin daurawa akaina sai ganin su nayi tare zaune suna kwasan dariya.
Gaba yai mugun faduwa dan ban san da zuwan shiba gidan kuma ban tsamani anty ta sani ba don baji tana magana ba.
Ban yar da mun hada ido ba sai gasheshi nayi da cewa sannu da zuwa uncle, ya amsa da yauwa mun samay ku lafiya.
Tuni har anty ta lura da yadda na daburce ko sai tace safiya ga bako mun samu yau girkin ki ko saura bai ragewa don maciya biyu sun hade a gidan jeki zubo mai abincin kafin daddy ya dawo.
Sai yace ai da a bari ya dawo muci tare don tunda ya fita da su yan biyu bai nisa da gida yanzu tunda an sauko tun dazun.
Na kalli anty tace barshi kin ji bai jin yunwane sai dan uwanshi ya dawo kin san haka suke kamar tasbaha wajen zumunci.
Ya kalleta yai murmushi yace in dai an matsa muna sai mu kawo wa mutum kishi ya yanzu don na gane tako yanzu baki son zancen kishiyan nan.
Dariya suka kwashe dashi tace mu ai yanzu ba batun mu akeyi ba kai dai ne gwaro zamuwa aure don zaman nan naka haka yana bata min rai wallahi.
Ya kwar da maganan da cewa kin ga ke ne mai sin cin naman Turkey yana mota na sayo maki ki tura a kwaso maki da sauran tsaraban ki har na fara tafiya zuwa dakina don jin topic din da suka dauko.
Sai naji tana cewa kai safiya don Allah dawo kin ji ki dauko min a saka a fridge tun bai lalace ba kace gobe akwai harka a gidan nan ke nan komai bazan ci ba sai shi gobe in Allah ya kaimu .
Juyowa nayi na dawo inda suke na dan tsaya dan nisa kadan dasu tace taya ni murna maigidana ya sayo muna naman Turkey wai yana a motan shi waje.
Dan murmushi nayi kadan yasa hannu a aljihu yana ciro key din motar shi yace anya kuwa zata iya kwaso kayan ita daya ?
Tace ai shine kuma fa kodai ba ka son ta wahala ne tun yanzu yace kai madam baki da dama wallahi aidai yanzu nasan takonki in kin yi wasa sai kiji ayyururi a gidan.
Tace gaba dai ba nan ba ai anyi tun 1900 dariya yayi yana miko min key din tace nifa da gaske nakeyi wallahi ba wasa ga magana na tace kira funke ta taya ki kwaso kayan don waya nan mashiriritan nan san sun kwanta ne.
Funke na kira muka fita tare a daidai lokacin da motan daddy yake shigowa ge din gidan tun mota bai tsaya ba su yan biyu suke kwala min kira.
Sun fito suka nufo mu suna cewa daddy ya kaisu shopping da zasu dawo mosque nace kaga yan gata daddy kenan daddy ya fito muna mashi sanu da zuwa ya amsa tare da cewa motar waye anan ?
Funke ne da sauri tace uncle ne yazo aisai yaran suka kwasa da gudu ciki suna fadin uncle oyoyyo nan suka barmu muna dariya shima daddy ya bisu ba tare da ya kara fadin komai ba.
Nace a raina ko yaro yasan mai kyautata mashi ke nan muka bude buth din da kyar don dagani har ita ba wanda ya iya saida security din kofan ya taimaka muna budewa.
Mun shigo da kayan da kyat muka koma kwasowa mun samay su na ta murnan ganin juna shi da daddy sun zauna kamar abokai sun rungumay junan su.
Mun gama kwasowa muka zube su nan a inda suke zaune anty sai cewa take a a a Sulaiman duk may ka kwaso muna haka ?
Yace well yanzu dai ai ki buda ki gani don ni yarana na yowa sayayya bake ba tace aina sanj indai sin kaine akwai ku dashi ba a magana.
Nace daddy a kawo abinci ne yanzu ?
Na fada tare da dan kallon shi yace haka ya kamata yar albarka ke kan ai mijin ki ya huta wallahi.
Jeki ki bamu yunwa nake ji sosai ganin wanan ya hana in nema tun da na shigo haka dai kuke so mutum kada ya huta ko yaushe sai aiki.
Mikewa sukayu zuwa table din suna kara tattaunawa akan kasuwan cin Sulaiman din wanda ya fara yanzu a logos da Abuja wanda yake kuma son karawa a wasu jahohin kasan nan.
Cewan da nayi wanan ya isa daddy ko a kara ne nace da daddy din sai suka maida kallon su ga abincin dana zuba masu daidai anty na kawowa wurin.
Dakyau safiya inji anty ai gwauna da kika tula masu abinci yau muga iyakar son cin tuwon su suma dariya suka sake a lokaci daya.
Daddy ne yace Safiya sannu da aiki kinji Allah dai ya saka maki da alheri anty tace ya nuna muna auren ta da oga koda yake ma na fasa bada kawar tawa ai don sai mu ja maka rai muma.
Daddy ya jawo plate din shi gaban shi yana cewa a a haka kuma zaki muna kinyi niyar yin abin arziki kuma zaki zuga yarinya Safiya karki dauki maganan ta ina bayan ki kinji .
Fuska na daure ba annuri na azuba masu ruwa na juya na wuce lokacin ya jawo plate ya fara cin abincin kamar bai son ci zuciyar shi ba dadi a lokacin.
Sai mamakin su yake yi kawai sunyi nisa da cin abincin shiru yai yawa daddy ne ya kawar da shirun da cewa wanan maganan yai min dadi danaji.
Don shawara ne may kyau madam ta kawo sai a lokacin yai magana yace tare da dakatar da cin abincin da yakeyi amma sai nake ganin wanan abin kun san bamai yuyuwa bane.
Daddy ya tare shi da cewa kana ganin zamu hada abinda bai dace bane a kan ka ko zamu cuce ka ko yarinyar ?.
Gaba daya ture plate din dake gaban shi yayi daddy yace kaci abincin kamana naga abincin yayi dadi ai .
Baiki ba yasa hannu ya mayar ga abincin daddy yaci gaba da magana yace ka kwantar da hankalin ka ka saurare ni.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button