BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,
????????3️⃣8️⃣????????
UBANGIJI ALLAH YA BA MU IKON BAUTA MASHI, BAUTA TSARKAKKEKE,
YA ALLAH KA KARBA MUNA IBADUN MU, , , ,
Tsura ma dan uwan nashi ido yayi yana sauraren bayanin shi daddy yaci gaba da cewa kamar dai yadda aure ya cika kan wanan cutar haka itama aure ne sanadin samun wanan cutan a gare ta a halin yanzu.
Innalillahi yake iya fadi acikin ranshi da fili yace wai kuna nufin wannan yarinyar ta taba aure har an cuta mata irin haka.
Yace cikin garin nan na Lagos tana zauna da miji ta sai dai auren anyi zaman ne a cikin ukuba sai kuma ga wannan cutar ya baiyyana mata.
Ya ce Ya Allah kaza ma gatan mu yanzu wanan abin da mai yai kama mutum yasan cewa yana da cuta a tare dashi amma don ha inci sai yaki fadi har sai ya lika ma dan uwansa abu ya baci adawo ana dodofar tsiya.
Sun dauki lokaci suna magana daya kafin ya mike yace zai tafi har a lokacin ranshi bai mashi dadi sam don abin yadawo mashi sabo a rayuwan shi.
Yai masu sallama anty tana tabayan shi yaushe zai bullo kuma tasa aimai girki sai yace yana dan aiki idan ya rarage zai shigo.
Daddy ya mike suka fice daga gidan tare dashi sun shiga gari tare don duban wasu aiyuka da ya bayar aimashi tun wancen lokacin.
Washegari anty da zancen nama turkey ta dole shi aka dafa mata nai miyan shi nan aka taru a falo kowa na kwasan dafuwa.
Sai da anty ta bari sunyi nisa da cin abincin ne take cewa damu aduniyan nan babu abinda nake kamar wanan namar .
Nan kowa ya shiga fadan albarkacin bakin sa akan naman bandani dana ce ban taba cin shi ba a rayuwana dariya suke min sosai saka su daddy sun shigo gidan shi da Sulaima a bayan shi.
Daddy ne ke muna kallon mamaki ganin irin dariyan da sukeyi din yake tambayan maiyai maku dadi haka irin wanan dariya.
Fatine ta iya bashi amsa da cewa wai Safiya ne ke fadin ita bata taba cin naman turkey ba shine tabamu dariya sai daddyn ya mayar da kallon shi inda nake yana zama a kusa da matar shi yace.
Kauna na kada ki damu da dariyan su watarana sai kin ci abinda duk kan su basu taba ci ba don haka kema zaki rama nan ba da dadewa ba insha Allahu.
Yanzun dai tashi kin ji ki debo muna muma mu dandana muji santin da sukeyi akai don da gani yayi dadi tunda naga Fati yau haka baje baje.
Na mike zuwa hada masu abinci daddy ya kalle matan shi da dariya ya cika yace kar kuyi mamaki zama kauye don nan da wani lokaci ta fiku bude ido .
Dariya ya ci karfinta tace ai bamu haka da Safiya yadda take juya naman a kyamace ne yaban dariya.
Sulaiman ya katse ta da cewa ai cin nama ra ayi ne idan bata so sai a saya mata wani mana taci kuma kuna kallo.
Sai gani na dawo ina ce ma daddy na hada abincin dama na hada tun basu dawo ba anty tace dani to ke kin ji uncle yace tunda mun bata maki rai zai fita dake ki zabi naman da kike son ci a sayo maki muna kallo.
Na da yi mata murmushi nace ni fa anty kin san nama bai damay ni bane kawai ba wai wanan ba.
Kowa wurin yai mamakin jin abinda uncle ya fada do cewa yayi idan baki son nama sai a sayo maki wani abin don haka dana gama zamu fita.
Da sauri na dan kalle shi sai naga ba wasa ga maganan shi sai Fati ne tace Safiya muje mu shirya dama nima ina son fita kin ga sai mu tafi tare.
Anty tace waya kasa dake a ciki babu inda zaki sarkin son yawon tsiya kawai daga jin za ayi fita sai ki ara ki yafa har kina wani muje ki shirya kedin a shirye kike.
Faiza ne tace don Allah anty ki bari mu fita muma mu lakaci arziki ta sake cewa na fada maku ba mai bin su ko ina nice nace amma da twins zamu anty?
Ke kan ana kau da wasu kina jan wasu ai gara zuwa da wa yan nanbda zuwa da wa yancan yan sa maganan.
Shine yace da ita dana ai sune gaba wa yan nan din dai da kika hana su sun hanu babu wacce zamu fita da ita sai dai suga mun dawo.
Nai mamakin jin ashe yana magana mai tsayi irin haka don ban taba jin yayi magana mai tsawo ba duk sani na dashi.
Amma yau tun shigowan su na fahinci akwai canji a tare dashi sosai kodan ganin daddy tare dashi ne oho ?
Daki na shiga ba wani dogon shiga nayi ba dogon riga ne kawai sai dankwalin shi dana yane kaina dashi.
Zama nayi ina tunane ni kadai a daki na yadda zamu fita dagani sai shi sai ga su yan biyu sun shigo da murnan su wai in fito in ji uncle mu tafi.
Sai da na dan bata lokaci na fito anty bata falon sai su Fati ba wani magana mai dadi sai harara da suka raka ni dashi.
Ina tambayan su anty sai Faiza ne ta bani amsa da cewa tashige ciki nace in ta fito ki gaya mata mun tafi tace a sayo dawisu idan anje sai musan ke yar gaban goshin tane.
Nasan magana tasa min ban kulata ba na fice kawai abin yana sosa min zuciya fati ko tsaki naji taja tana bakar magana .
A mota na samay su shida su yan biyu zaune a baya hakan ya nuna min ke nan a gaba nibzan zauna kenan.
Kafin ma in karaso ya bude min gaban mota haka na daure na shiga duk a takure dani muka fice a gidan.
Tafiya muke babu mai magana sai su yan biyu dake ta hiran su a bayan motan basu ko kula mu ba fuskan shi na kallon titi niko na mayar da fuskana gefen da nake zaune ina kallon yadda garin a kullun yake da da girma da bunkasa duk da an dauke headquater anan.
Naji yace Safiya kin san abin da madam ke shirin shiryawa a tsakanin mu ko ?
Na kalli yaran dake bayan motan naga hankalin su baya wurin mu nace a hankali nadai ji tana fadi amma bamu yi magana da ita ba tukun.
Yayi ajiyan zuciya sanan ya nisa yace ya kamata in san raayin ki kiyi hakkuri muyi magana anan don bamu da wani lokaci na sake haduwa irin haka.
Shiru na dan yi kafin in sauke ajiyan zuciya ince dashi to uncle , uncle ina anty ta fada maka matsalan da nake ciki, din haka ni naga kawai ayi hakkuri ba abu bane da zai yuyu a tsakanin mu.
Saboda gaskiya sai na kasa magana karshe dai nace uncle mudai yi hakkuri kawai ya dakatar dani da fadin saboda may zamuyi hakkuri da maganan bayan abune wanda zai yuyu.
Ko bata fada maki cewa nima a halin da nake ciki ke nan ba sai na dan kalle shi kadan yace yes nima victim ne amma sai wanda ya sani zai sanda hakan.
Idana na kallon kasa look safiya ba wai abune da zamu tsaya muna yi wa juna kwana kwana ba da maganan.
Ina son ki sani wanan abinda mutanen nan suke kokarin hadawa a tsakanin mu gani sukayi mun dace da junane.
Ina son ki sani koda wanan matsalar ko babu shi akan mu wallahi ni son ki nakeyi tsakani da Allah ina mai tabbatar maki ba zan iya hakkura dake ba a yanzu.
Ya nisa ya sake cewa wallahi ina son ki sani ban taba haduwa da macen da hankalina ya kwanta da dabiun ta ba irin ki.
Gashi dan haduwan na dake da madam ta fara min maganan nan maganar sai bibiyata takeyi na rasa sukuni a tare dani.
Sai kuma naga yayi murmushi yace sorry bazan iya ci gaba da fada maki ba amma na gaya maki gaskiyan zuciya na don ba wani lokaci nake son a dauka ba ga zancen.
Nayi shiru ina sauraren shi sai da naji abunda ya fadi a karshe nai saurin dago fuskana sai wanan lokacin muka hada ido dashi.
Take gabana ya fadi don kwarjinin sa da na ga ya fito fili a idona nace da wuri uncle yace dani yes I mean it, idan kina shakkun hakan gara ki daina ko kuma kina iya bani baki ki gani.
Nayi shiru na rasa may zance dashi yadda naga ya zare min a lokaci guda to ni may zance dashi eh ko a a .
Har ga Allah uncle ya samu karbuwa ga zuciyana don ina son shi har cikin zuciyana saboda me ne sulaiman dai namijine wanda duk wata mace ke burin mallakan shi a matsayin mijin aure mutunci addini kamala da natsuwa da gaskiya irin na nuna shi din daban ne da sauran mazan dana sani akwashi.
Amma kuma nauyi da kunya ban taba ganin wanda nake jin nauyin shi da kunya ba irin shi don haka bazan iya nuna mashi kai tsaye na amince da bukatan shi ba.
Bai kara yi min magana ba har muka isa wani shopping mall anan ya tsaya yace mu fita kowa ya dauki abinda yake so.
Kunya bai bari na dauki komai ba sai wani turare dana dauka ganin kuya bai bari na dauki wani abu sai naga ya shiga daukan duk abinda yaga ya dace yana kadawa kwado sai da basket din ya cika sosai har yana zuba ya bari.
Mukaje gurin biya ya biya akai muna packeg din su a ledojin shagon muka fito.
Bai tsaya ba sai wurin wani shagon sai da nama kala kala nan ya shiga shi kadai sai gashi ya fito da ledoji shake a hannun shi yaja mota muka tafi.
Ba magana haka muke tafiyan sai ya koma hira da yaran har muka kawo gida sun fita na bude mota har na saka kafa na daya a waje naji yace dani ina sauraren ki nan da two weeks.
Ban ce dashi komai ba sai da na fito daga motan ne nace mun gode bai bari mun dauki komai ba ya kira security daya ya taya shi shiga da kayan ciki.
Lokacin yamma yayi sosai suna falo zaune muka shigo duk idanuwan su a kan mu anty farin ciki ya kasa boyuwa a fuskanta.
Suko nasan ba komai ya zaunar dasu ba sai gulma basuyi mamaki da irin kayan da muka shigo dashi ba don sanin waye sulaiman din da sukayi.
Bai tsaya ba baya ya aje sai yace da anty zai koma sai dai da safe idan ya shigo karyawa mikewa tayi ta bishi baya suka fita gidan tare.
Sai lokacin Faiza tace yau kan kun sha dadi wallahi naso ace anty ta bari mun bi ku muma mu lakato arziki don ba a barmu mu dawo haka ba.
Wai safiya kodai wani abu na shirin faruwa ne keda uncle nace may ko ke shirin faruwa rabona ne kawai ya koka a wurin shi dariyan ku akaina yazama min sanadin samun alheri yau a gurin sa.
Tace indai yai wari maji amma ai banza baya haka da sauri fati tace balle ma may zai yi wari a nan wanda ke gogayya da mata hamshakai ne zai tsaya a nan.
Nace ako hakan in Allah ya nufa sai ki ga ya faru anan din inda ba komai tai saurin cewa ki iya lafazin bakin ki ramin kura ba wurin wasan yaro bane koda kuwa an rika masa.
Dariya na wuce dakina ina yi ga leda a gaban su babu halin budawa su gani kada anty taci masu mutunci akai dole suka zauna zaman jiran ta ta dawo.
A can waje kuma sun tsaya wuri motan shi ne yayin da ya dafa mota da hannun shi daya suna magana da anty din tace to yaya ina fatan dai kun dan fahinci juna wanan fitan da kukayi tare.
Yai murmushi cikin jin kuya yace mata wanan kaunar taki kunya yai mata yawa taki sakin jiki mu fahinci juna kamar mai tsoron kar na sayar da ita.
Tayi saurin fadin may Safiyan tayi maka kuma yace yace kiyi hakkuri zakiyi mamaki amma wallahi nidai yarinyar tayi min so sai ta tsaya min a rai.
Amma naga kamar ba za iya shawo kanta ba don tana da kunya sosai ga kurciya a tare da ita kuma.
Anty zatayi magana ya hanata yace don Allah madam ki taimaka min ki shawo kanta wallahi son safiya nake yi da zuciya daya ina son ga na taimaka wa rayuwanta .
Auren ta nake soyi na bada dadewa ba sai dai ban san yaya zaku dauki maganan ba yanzu.
Ga baki daya maganan shi ya gama kashe mata jiki da mamaki don bata taba tunanen zai afaka haka da sauri a sona ba shiru kawai tayi ma rasa may zatace dashi.
Ganin tayi shiru yace madam kina mamakina ne ko tace ina jin ka dadi ne ya kashe ni wallahi wai yau kaine kake maganan aure haka a gabana babu kunya sanan wace kake so din gata yar gida ce.
Sulaiman gaskiya ka gama kasheni da jin dadi don haka ka kwatar da hankali ka da yardan Allah kamar ka auri safiya ka gama.
Bari ma ka gani yanzu da na shiga zan tun kare ta da maganan har sai ta bani baki ayi don yarinyar na jin magana na sosai.
Don haka ka barni da ita kawai zan san yadda nayi da ita kar abin ya dauki lokaci mai tsawo iyayyen ta kuma zan san yadda na lurar dasu akan zancen.
Yaji dadi har ya kasa boyewa ya rika fadin na gode madam thanks alot Allah ya bar min ke kin zama babban yayada gaske.
Tace au dama ke nan ta karyace yace ai da madam kike yanzu ko zamu zama sarakai dake tace aban tukwaici na yace ai tukwaicin ki shine daga ke ba wata a gidan nan .
Na biyun bazan fada maki ba sai abin ya yuyu zaki sani sai suka sa dariya a tare a haka ya tafi tana shamatar shi yana cewa yaji.