BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , , ,
????????4️⃣0️⃣????????
YA ALLAH MUNA ROKON KA KABA MU IKON BAUTA MAKA BAUTA TSARKAKKEKE KA KUMA KARBA MU NA IBADUN MU, , , , ,
Lumshe idona nayi tun da muka fara tafiya ashe da haka nayi barci sai da mukai nisa sosai ni kadai a baya zaune sannan na falkafirgigi daga barcin ina kallon gaban mota inda driver keta faman sharara gudu.
Sai yamma lis muka iso makwabtan karkaranmu nan na dan fahinci ida muke don da gaba yana tafaduwa don ban fahinci komai ba.
Garin muke shiga lokacin marance yayi sosai don haka mazaje da yawa suna kofan gidan su suna dakon kiran sallah.
Kwantace hanyan gidan mu nake mai har Allah ya kawo mu lafiya na nuna mashi gidan mu ya nufi kofa yai packing a kofar gidan .
Duk hankalin mutane ya dawo kan motar suna son su ga wanda zai fito a wanan mota mai kyau haka ganin ta tsaya a kofan gidan mu ya su yaya sani tasowa da abokan shi.
Da sauri driver ya fito ya bude min mota na sagalo kafa daya dayan na a ciki na tsaya dauko hand bag dina zan fito.
Yaya sani yace ah Safiya ne fa da sauri yazo yana kokarin rike marfin motan da nake fitowa ciki daga ciki suma sauran sannu da zuwa suke man na gaishe su cikin mutunci sai na nufi cikin gida.
Nan suka fara biyo ni da kayan yar wurin mamace zata fito sai gani ta tsaya tana kallo na don bata sanni ba sai da nace da ita maimuna ina zaki sai ta dauki muryana tace Safiya ke ce nace nice maimuna.
Nan ta fara ihu lah ga Safiya ga safiya daidai lokacin da nake kutso kaina cikin gidan kenan duk hankalin su ya koma wurina suna mun kallon kurrullah.
Duk suka rufe ni suna min sannu da zuwa yayin da abokan yaya sani suke ta shigo min da kaya daga ciki ni kaina abin ya bani mamaki ko shiga daki ban yi ba bayan mun gaisa dasu mama sai na wuce dakin baba kai tsaye don in ga halin da yake ciki.
An zaunar dashi wai yai sallah amma saida ummina ta tsaya daga bayan shi na shigo dakin ina cewa sannu baba yaya jikin ?
Yadago kai zabban tausayi yace safiya kece tafe nace eh sannu baba yana fadin wai may yasa su ka fada min baida lafiya banji may yake fadi ba sai da na tambayi mama dake gefen shi take fada min.
Na juya wurin mama ina tambaya anko tafi asibitin birnin yau sai tace man wai kudin da aka samu arro baya isa don tun a daukan mota da za a tafi rabin kudin ya kara nace haba haba mama nace a kaishi ko nawa ne , gani nan tafe ai zan biya.
Na dan tsaya tsaye shiru ina kallon yadda baba yake wahala da bautar Allah sai na fita dafa daki na samu kanne na sun shiga min da kayana dakin mu .
Sai dai suna waje suna gardaman wai kwali goma ne inji yar wurin inna sai dan wurin ummi kanina yace hummumm sha biyu ne na gardama ya kaura a tsakanin su.
Inna ta kwala ma yar ta kira wai ina ruwanta ko kwali dari ne na shigo dashi tasan sanan da nake yi na samu kwalayen da na shigo dasu iyayyayena suna murna.
Kai kawai na girgiza na ce a ban buta nayi alwala daga dakin ummina ban tsaya sauraren ta ba bayan munyi sallah ne na fito na samu yaya sani nake cemai yaka mata mu tafi asibiti da baba sai yace ai maganan kudi ne da mota nace motar da na zo da ita zamu tafi.
Yace sai a bari sai da safe ina shiga dakin nace dashi yau dai zamu tafi yanzu ma zamu kama hanya dawa zamuyi tafiyan ?
Nake tambaya yaya Sani din ina dafa baba ina kai sannu yaya jiki ya gyada min kai alaman da sauki jikina ya kara yin sanyi don dai ni a yi sani na dashi ban taba ganin yayi ciwo irin haka ba.
Mama tace bari taje ta shirya don da ita za a tafi inna da ummi su zauna gida amma da inna ta samu labari sai ta tada fitina wai ita zata .
Yaya sani yace ai ba kasuwa zamu ba da kowa zaice zai tafi da mama kawai zamu sai ni da Nura yace mata.
Na fita naiwa driver magana kamar yadda Sulaiman yace in sanar dashi duk abinda nake so nasa ankai mai ruwa da maltina da abinci yana ci ne sai gani na fitinan nake fada mai tafiyan mu birni.
Sha daya na dare muka isa asibitin basu so su karbe mu ba a lokacin sai da na nuna masu kudi sannan suka fara nan nan da mu, har likita suka tayar cikin daren nan yazo ya duba baba maganin da ya rubuta.
A cikin daren nan su yaya Sani da driven nan suka fita neman magani anyi saa an samu a wani shago sai dai shi yaya sani yana ganin yawan kudin don dubu ashiri da wani abu suka kaso .
Ya dawo yana fada min nace mun yi arziki ai tunda an samu tun cikin dare akaiwa baba aluran da bashi maganin sai gashi ya samu barci sosai ranan.
Washegari nacewa driver ya wuce sai yake cewa ai sunyi waya da maigida yake cewa ya dan tsaya don zirga zirgan mu ya taimaka muna naji wani iri a raina sai dai a fili cewa driver nayi anya ayi haka bazamu takura maka ba ?
Haba madam aini a kan aiki na nake daganan har ki gama banda damuwa ko kadan Allah dai yaba baba lafiya.
Nai mashi godiya sosai yace babu damuwa hajiya ai mu aikin mu ne naga kuma oga ya damu sosai da ciwon na baba murmushi nayi kawai.
Sai na tuna ban kirashi ba tun jiya kamar yadda yace in kirshi din don ya anshi wayana yasa min nombashi da zamu wuto.
Gefe na koma saida na tattara natsuwa na wuri daya sanan nai dialing din nomban na shi ringi na uku ya daga wayan yana cewa.
Safiya yaya ai na zaci bazaki kirani ba kin ga mutanen gida kin manta da kowa.
Murmushi nayi nace wallahi ba hakana bane ya dan kwaikwayeni yace to yayane nace kawai dai jikin babane ya tsoratani jiya da na samay shi jikin ba dadi wallahi.
Amma yanzu ya samu lafiya sosai don maganin da aka rubuta mai da allurai tunda ya sha su ya samu barci jiya sosai.
Yace masha Allah haka akeso to yaya mutanen gida nace suna lafiya sai nai shiru kusan tare mukai magana ina cewa kuma har da wani dawai niya haka mai yawa.
Yace bake nai wa ba iyayyena da kanne na naiwa tsaraba ki basu godiya na fara mai yace haba na fada maki bana son haka nifa iyayyena ne yanzu koba hakana bane ?
Murmushi na danyi yake cewa yanzu dai hankalin ki ya dan kwanta ko baba ya samu lafiya sai na sauke ajiyan zuciya nace hakane amma da hankalina a tashe yake so sai.
Don mu din tallakwa ne na karshe indan baba ya kwanta wa zai dube mu shi kaga hankali na ya tashi sosai.
Yace karki manta da cewa Allah ne mai yi ba wani ba yanzu bagashi ya samu sauki cikin yardan ubangiji ba nace haka ne kuma.
Yace idan ya tashi ki gaida min shi zan shiga meeting yanzu dama don baki kirani ba ne yasa ban kiraki ba yanzu kuma naji dadi alama ya nuna na dan samu karbuwa ke nan.
Kai nace haba uncle kabar wanan magana tukun yace na bari as you wish ganin zai kashe wayan yasa nace sai kuma driver yace kace ya tsaya damu.
Yace eh haka na umurce shi don idan ya wuce ina zaku samu abin yin zirga zirga shine nace ya dan dakata har muga yadda hali yayi.
An gode na kara fadi zan shiga godiya naji ya kashe wayan shi kit na dubi wayan ina murmushu na shiga dakin da aka aje baba din har lokacin yana barci naja kujera na zauna tare da kafa mai ido.
Mama tana zaune a kasa saman tabarma tana karyawa da abincin da na sa yaya Sani ya sayo muna don bamu da kowa a garin.
Na dan dade a zaune sai ya motsa da sauri na dago ina cewa sannu baba yaya jikin ina dan gyara mashi kwaciya yace Safiya ke ce yaushe kika dawo ?
Nace a sanyayye jiya na dawo baba yaya jikin yaya jikin baba ?
Yace jiki da sauki Safiya na gyara mashi kwaciya yace baiyi sallah ba da tai makin mu nida mama muka kamashi ya kewa yayi alwala.
Bayan ya idar da sallah ne yake cewa nan ina ne mama ne ke fada mashi ai asibitin birni aka zo dashi jiya da dare da safiya ta iso.
Yace Allah sarki sannu Safiya nagode nagode ubangiji yai maki albarka yasa ki gama da duniya lafiya nace amin baba mama tace yau ga ranan diya mata mun gani a gidan.
Don badon Allah ya taimaka ba da bamu san yadda wanan alamarin zai kaya muna ba kana zaune a gida ciwo zai halaka ka babu yadda muka iya .
Gashi daga zuwan mu jiya jiya har mun ga haske gashi yau ubagiji ya nufa ka bude ido nace baba don Allah ka rage yawan tunane don likita yace tunane yai maka yawa har zuciyar ka ya kumbura.
Murmushin karfin hali yayi yace yaro yaro ne tune ne ai dole mai rai yayi shi balle ni da gidana yake batun fin karfina inda rai na kuma don may bazanyi tunane ba safiya ?
Nace baba hakkuri za a yi abar ma Allah komai ubangiji yana sane da komai da bawa ya gani yanzu dai may zaka iya ci a sawo ma ?
Yace ban jin cin komai sai barcin da nake bukatan komawa don idon nan nawa kamar asa min abu mai nauyi nake jin shi.
Nace baba ka daure kasha tea mai dan zafi ko hajin ka zai warware ka kara samun karfin jikin ka.
Yace dadai kune ne kila zan dan iya sha da sauri nida mama muke cewa ga kunu nan an sawo bari a baka yaya sani ne suka shigo shida driven nan suka shiga gaida shi.
Bai sha wani abin kirki ba ya koma barcin muka sauke ajiyan zuciya muna kallon yadda yake sauke numshi a wahale wai ma cikin yaji sauki ke nan.
Sama sama muke hira da mama ina fada mata irin zaman arzikin da muke yi da anty da yan uwanta tace Safiya haklin ki ne ya ja maki .
In dai baka dauki kan ka da fadi ba Allah yana taimakon bawan sa ta ida bai zata ba Allah ne ya kawo ta cikin rayuwan ki don ta taimaka maki.
Gashi tun yanzu muga haske badon Allah ya kawo ki ba wanan alamarin yaya zamuyi kena da haka zamuyi ta kallon shi a gida babu mai taimaka muna.
Shiyasa nake ganin haukan innar ku da bata da kalamin alheri sai na tsiya akan yayan mutane duk da wanan abin da ya cika dasu kuwa.
Murmushi nayi nace banga ranan da inna zata daina halinta ba ita haka Allah ya halicce ta da hassada don bata bar kowa ba a gidan.
Tace bata fa dainawa don dubi abinda tayi jiya Sani ne kawai mai taka mata burki don badon shi ba jiya ba karamin tashin hankali za a yi ba.
Nace niko ban ga Saadatu ba ma tace tana nan daki bata jin dadin jikin ne don duk da malam ya hana a zubar da cikin jikin ta amma bai hana uwan bata abubuwa a boye ba.
Nace na shiga uku mama karfa ta kashe ta tace in ma ta kashe ta ai ita ta sani waya ci baya ina mahaifiyar ki data rungumi kaddara ba ga abin yazo mata da sauki ba.
Mu dai fatan mu ubangiji ya baki miji ki aure ki huta da zargin cewa zaman banza kike yi a can na ce ai Allah yagani mama.
Ban yi ba da sai yanzu da lalura a jikina zanyi in cutawa mutane ko mai tace ai bata gane hakan ita don idon ta ya rufe ko.
Motsawan da baba yayi yana fadin a bashi ruwa yasa mu tashi muka ce yayi hakkuri an daura mai ruwa nace barin fita in nemo likita a fada mai.
Naje gun nurse din ward din mu na fada mashi sai yazo ya duba baban ya fita kiran likita sai gasu sun dawo tare da likitan yadan duba baba din tare da zare mai ruwan da suke kara mashi din.
Yace a barshi ya dan huta zai daina jin kishin da yake ji nan dai suka kara taruwa a kasa suna mashi gwaje gwaje irin nasu na likitoci.
Yaya Nura suka iso shi da su ummi da mama da rana nan suka samu yana barci bayan gaisawan da mukayi dasu ne mama take masu bayanin halin da baba din ke ciki yanzu.
Nan dai muka wuni dasu sai zuwa yamma sukace zasu tafi drive nan dan arziki yace in bari ya mayar dasu sukace ya bari zasu shiga motar kasuwa inna sai baza ido takeyi wirin kalle kalle a asibitin.
Ya kwashe ya wuce dasu hankalin gida zai kwanta yanzu da suka zo suka gan shi dan da basu zo ba duk wayan da muke yi dasu basu yarda a yadda muka fito dashi gida wai ya samu lafiya yanzu.
Baba yana samun kulan da ya dace sosai dashi sannu a hankali yake samun sauki na shigan shi yana dan dada murmurewa .
A kwana na uku ne driver da ya kawo ni yace zai koma gida na bashi kudi yaki karba amma sai naba yaya Sani ya bashi idan sun fita.
Ban wasa da shan maganina don dama ina dashi anty tana kaini ansa a sace bada sanin kowa ba a can lagos din don haka ban da matsala wurin amsan maganin .
A kwana na shida aka sallamay mu nan muka samu motar muka dauka ta dawo damu gida kowa na ta farin ciki yadda suka ga baba ya samu sauki.
Sai dai an bashi dokoki na ya rage tunane da abincin da ya kamata yaci don ya samu lafiya muka sayo magani wadatacce muka dawo gida dashi.
Dakin mu na shiga na cire kayan dake jikina don duk warin asibiti duke yi wanka naje nayi na shirya sai na fito zuwa dakin inna.
Saadatu na kwance duk ta kumbure nace subbahanallahi Saadatu may ke faruwa haka kina zuwa asibiti kuwa maimakon tai magana sai kuka ne yazo mata.
Zama nayi a kusa da ita nace bari kuka saadatu haka Allah ya nufa damu sai dai istigifar ga bawa nace kin je asibiti tace wa zai kaini Safiya dan jike jike dai inna ke bani ina sha.
Nace zuwa zamuyi gidan mau ta dubaki mu gani tace uhumm Safiya ai da na dauka halin innan mu yasa kin fita batuna ne dan da kika zo baki nemay ba harda kuka nayi gashi ban iya fita ko ina.
Nace haba saadatu may zai sa inyi fushi dake ke fa yar uwata ce ta jini halin inna kuma inda sabi ai na saba yanzu sai dai addua kawai.
Da taimako na ta samu ta shirya don inna na dakin baba sai fitowan mu suka gani kawai take cewa ina kuma zaku haka ?
Nace wiri mau ta duba lafiyan jikin ta don ba a barta haka ba tana wahala tace ai ita taja wa kanta ina ruwan wani saaden tace dani mutafi kin ji safiya.
Nan muka fice muka barta mashin na tare ta hau nima na hau mukaje gidan an dubata take muna bayani bata samun kulawa ne sosai an mata allurai don tace akwai maleria masu ciki a jikin ta do haka tabar bari sauro na cizon ta ta bamu magani tare da fada mata abinda ya kamata taci kuma ta dinga zuwa ana dubata akaiakai.
Bamu dawo gida ba sai da na sayo mata abin bukatun ta harda gidan sauro muka dawo gida yamma tayi a lokacin nan ina ta ke cewa .
Yanzu dai anyi kudin da bamu san asalin shi ba anzo ana muna facali a gida indai tai wari ai maji komai daren dadewa .
Ba wanda ya kulata sai dare muka samu kebewa da ummina nan muka shiga hiran yaushile rabo da ita nake fada mata duk yadda nake can.