BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

Kwana goma na kara jikin baba yayi sauki sosai na fara shirin komawa don kullun su yan biyu waya suke suna tambaya na yaushe zan dawo sai ince masu gobe.
Damuwan da sukeyi yasa nace zan koma nan muka fara shirin tsaraba abin da nasan suna so shi muka saya zan je masu dashi tsaraba.
Sai da na shirya na sa ranan tafiya mu nan yaya sani ya zake dama yana damuna yaushe zamu tafi sai gashi nace mai ranan asabar mai zuwa zamu wuce.
Ranan ina zaune na dawo sallaman uwayena ta famnin ummi na ina cire kayan jikina dana sa waya na yai kara ina dauka naga yaya Saadune.
Da murna na na dauki wayan nan na zauna a bakin gadon ummi nace yaya ina kashiga nayi kiran wayan ka yafi a kirga baka dauka ba.
Yace kedai bari wasa wasa nayi tafiya zuwa ghana sai gani har togo shiyasa ba a samu na ko an kirani.
Nai mashi sannu da zuwa yake ce min yanzu ma yazo ne matar shi zata haihu shine yadawo gida yace kin san halin gwagon ki.
Idan bani nan ba komai zasu yi ba shiyasa na dawo gida don ayi komai a gabana nace Yaya ashe zamu samu karuwa kwanan nan.
Nace idan na dawo lagos zan zo inda kuke yace zakizo lagos ne nace ai yayanan nake yanzu.
Yanzuma nazo gidanane baba baida lafiya shine nazo amma ya samu lafiya yace subbahanallahi may ya samu baban ?
Nace ya samu sauki ai amma yaji jiki sosai wallahi amma yanzu yana samun lafiya yace a gaida mashi baba insha Allahu zai shigo kafin ya koma.
Yace yaya labari safiya ina fatan komai na tafiya daidai ko nayi murmushi nace yaya komai lafiya sai dai mun hadu kawai yace akwai labari kenan ?
Dariya nayi nace ya gaida matar shi yace zataji zan fada mata kin ce zaki zo nace insha Allahu zan zo.
Mukai sallama na kashe wayan ina jin dadi a raina na yaushe rabo ina fada ma ummi ya na gaishe su wai matar shi nada ciki zata haihu.
Addu a tai masu ta na Allah ya raba lafiya nace amin muka dan taba hira da ummi akan matsalolin duniya na gidan mu dana waje.
Sai ranan jumma a inna tasan da tafiyan mu duk ta rude sai ta kira yayan a daki tana ce mashi yanzu kai don kasada binta zakayi baka san mutum ba baka san sanaar shi ba.
Baka gudun aje a yanke ma kai ko a sayar dakai kaida ganin wanan mutumin kasan kudin shi ba na kai sake bane kuma gashi yaro ina zai samo kudi irin haka ?
Da sauri ya katse uwar da cewa ke inna zaki fara ko zaki fara halin ki yanzu duk halarcin da yarinyan nan tai maki baki gani ba zaki nemi wani sheri ki lakaka mata.
To ki iya bakin kin ki kada ki je ki zauna da wani kiyishi ya fita muji kunya yarinya na bin mu da arziki ke kina binta da sheri Saadatu dake zaune tace fada mata dai ko zata ji .
Yace nidai zan bita ki min addua Allah yasa karshen zaman banza ne yazo in samu abin yi acan in dawo maki da arziki sai lokacin tace to Allah ya sa hakan ne kadai kula da kan ka don Allah.
Ya fito nikan shiri nakeyi na zabi kaya cikin wanda nazo dashi naba Saadatu na raraba masu kayana wanda naje lagos dashi don yanzu ban iya sa su naba mutanen gidan mu.
Da dare driver ya iso don sammako zamuyi tun da safe zamu bar garin ranan mun raba dare da ummi muna hira sai wani lokaci muka kwanta tun da safe muka kama haya nabar su da kewan mu muma muna kewan rabuwa dasu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , ,
????????4️⃣3️⃣????????
YAN UWA BARKAN MU DA SALLAH DA FATAN MUN WUNI LAFIYA YAYA AIKI YAYA SHAN KAMSHI ALLAH YA MAIMAITA MUNA AMIN.
Mun yi nisa ga tafiya yaya Sani da driver nata hira ina naya ina karatu a wayana har muka kai wani gari driver yace zai tsaya yasai ma iyalin shi abu.
Suka fita suka barni a cikin motan nan na dago kaina ina kalle kallen garin mutane nata hada hadan su.
Nace a raina kowa yanzu wirin nan da abinda ke damun zuciyar shi atake na tuno a yadda na bar gidan mu don dai na tabbatar da inna kiran da taiwa yaya Sani jiya da dare magana ce a kaina.
Hango su nayi sun riko ledoji ga abin saya inkai tsaraba babu hali don nasan jirgi zanbi in koma kamar yadda nazo.
Suka dawo suka shiga mota muka fara hanya sai lokacin nace wa yaya Sani mutanen gida dai na tuna.
Yace ai baba ya samu lafiya yanzu baki ga har kofan gida ya rakomu ba nasan tunda yace afito mai da tabarma anan zai zauna.
Nace ni ban san lokacin da rikicin gidan mu zai kare ba kullun ace sai makwabbata sun shigo rabon fada a gidan mu.
Yace ai ba laifin kowa bane sai inna kin ga ana shigowa raba mama da ummi fada inma har matsala ya afku a tsakani su ba mai tsawo bane kowa ya bari.
Amma ita inna da kowa tana yi a gida har baba har yaran gida kin ma san abinda ta fada min ne jiya kan tafiyan nan namu ?
Sai nace inna dai nidai Allah yasa su bari yace to amin amma da wuya su bari din don ko kowa ya bari na tabbatar inna ba zata bari ba.
Sai dai yadda kuke hakkuri kuna take halinta kucigaba dayi har Allah ya kawo muna dauki ajiyan zuciya nayi nace Allah ya kyau ta.
Karfe biyu saura muka shiga Abuja nan yaya ya dinga baza ido wurin kallo nima din ba a barni a baya ba don kallon abin mamaki da aljabi nakeyi don garin yadda yake komai a tsare.
Direct gidan Sulaiman muka nufa don daddy ya koma lagos ko tun satin da mukazo dashi sulaiman din ne ya fito ciki bayan mun shiga mun zauna a wani irin yanayi.
Da ganin sa baijin dadin jikin shi sai dai yana dauriya irin na maza cikin karfin hali yana muna sannu da hanya.
Mun gaida shi a cikin ladabi da biyayya ya samu wuri shima ya zauna yana kara yiwa yaya sani yaya hanya yaya sani daketa washe baki ya amsa da lafiya.
Ya tambayi jikin baba muka amsa mai da sauki sosai tun wanan maganan naja bakina nai shiru suke hira sama sama yayin da mai aikin shi ke ta faman jera abinci wanda nasan don zuwan mu aka girka shi.
Driven da muka zo dashi ne yashigo falon yake gaishe shi ya amsa mai cikin dakiya irin na masu gida da yaran su yake tambayan shi yaya hanya ?
Ya amsa mai Alhamdullahi ya mike zai fice sai sulaiman din yace kada kai nisa don four zaka kai madam airport zata tafi lagos yau.
Sai lokacin na sauke ajiyan zuciya na dan dago na saci kallon shi ban san shima kallon nawa yake yi ba sai ya dan murmusa yace ga abinci can an shirya maku bissimillah ko.
Dagani har yaya Sani ba wanda yake da alaman motsawa sai naji yace barin dan fita na baku wuri kunji dadin sakewa sai dai ba dadewa zanyi ba zan dawo.
Ya mike ya fita ya barmu nan sai lokacin na dago na kalli yaya sani nace yaya kaci abinci gashi can saman table anjera.
Ya juyo yace kefa nace a a yaya ban jin cin komai yace may kikaci tun fa karin safe da mukayi gida ne a cikin ki nace yaya ban iya ci ne gaskiya.
Mikewa nayi shima ya tashi ya bini zama nayi ina nuna mai yadda zaici koma duk ya rude yaga abinci kamar a banza.
Ya sake jiki yaci sosai ina kara fada mai ya rike amana da gaskiya don zai yuyu gwada ka zai yi ya ga halin ka yace .
Safiya kada kiji komai akaina insha Allahu zaki samay ni kamar yadda kike son in kasance nace nagode yaya.
Yace safiya aini keda godiya ina na taba tunanen zan zo irin wanan wirin a rayuwana gashi ta dalilin ki Allah ya kawo ni.
Yace wanan mutumin waliyi ne Safiya akwai mutunci a gare sai dai muyi fatan Allah ya sanya Alheri ga alamarin.
Kamar yadda yace ba zai dade ba haka din ne kuwa ya shigo muna da sallaman shi mukai mai sanu da dawowa yaji dadi har cikin ranshi.
Ya nasa a zuciyar shi dama ace nazo kenan ba tafiya zan yi ba don yau da ya samu masu mashi sannu da zuwa agidan shi har yaji daban.
Ya samu wuri ya zauna yana cewa i hope kunci abinci sai nace mun ci yake cewa good yaya ne yace a a Safiya nayi da ita taci bataci komai ba.
Yace a wani irin cool voice why Safiya ko kina ganin zan cuta makine da bazaki ci abincin gida na ba ba fa anan aka girka ba odan shi nasa akai maku don gidana gidan gwauro ne.
Nace ba hakana bane na koshine yaya Sani yace haka take bata son cin abinci ko a gida sai yace a a baki ko kyauta min ba.
Why kike wasa da cin abinci bayan kin san halin da muke ciki don Allah ki bar wasa da cin abinci please ?
A sanyaye nace mashi tau yace good sai yayi dan shiru can ya nisa yace zaki barmin yaya Sani anan idan mun gama abinda ya kawo shi zai koma gida.
Nace an gode yada dan harare ni ya ce ban so na fada maki ko yanzu nima basu zama yan uwa na bane ?
Nace ban ce ba.
Yace barin dan shiga na fito sai ki shirya nan ya mike ya shige ya barmu a falon yaya sani ya bishi da kallo sai ya juyo ya dube ni.
Yace Safiya kin dace kin samu miji dai dai da halinki murmushi nayi nace Allah yasa yaya don ni yanzu tsoron auren nake yi don ban san halin da zan tarar ba saboda auren Ahmed ya sani tsoron maza.
Kibar wanan maganan don Allah auren Ahmed ai auren kaddarane ga kowan mu kibar tunawa don Allah.
Kuka na fara yaya sani na bani hakkuri yana cewa ki bar kuka don Allah kada mutumin nan ya fito ya samu kina kuka bamu da abinda zamu fada mai.
Jin haka yasa na dakatar da kukan nawa nace yaya dole in kuka don in ina tuna wanan auren sai inji dama mutuwa nayi.
Yace subbahanallahi safiya kibar wanan magana don Allah hakkuri zakiyi mana gashi ubangiji na son ya musaya maki da alherin sa cikin hikima irin ta ubangiji.
Kan shi ya cuta idan yayi maki ne don ki wulakanta suka ci amanar ki Allah ya tausaya maki yaba ki wanda ya fishi ta ko ina.
Shiru kowan mu yayi zuciyar mu tana tunane kala daban daban sai ji mukayi ya fito daga dakin haka yasa mu natsuwa .
Sallah yace muyi kanfin na wuce suka fita da yaya sani zuwa yin nasu sallahn suka barni nan zaune
Da yake ba sallah zanyi ba nan na zauna naci gaba da damuwa a raina ina mai jin ba dadi a zuciya ta tare da bin gidan da kallo.
Sai gashi ya dawo nan yake cewa na shirya nace eh yace na tashi mu tafi kai yadan dafe nace sannu sai ya sake yai murmushi.
Nace kamar baka da lafiya ko kallona yayi yana girgiza kai yace yaya akayi kika sani ?
Nima murmushin nai mashi nace tun shigowan mu naga hakan a tare da kai ban dai yi magana bane kawai.
Yace don baki damu dani ba komay ?
Nace bagashi na maka sannu ba yanzu?
Yace yana kokarin tashi wallahi jikin nawa ne yadan motsa min kwana biyun nan kuma laifina ne nai tafiya ban dauki magani na ba.
Nace haba dai may yasa kai ko ?
Yace da rabon insha wahala haka ne.
Yace tashi muje kada lokacin ya wuce muna nan yau na shiga uku da madam don na fada mata azo airport a dauke ki.
Mikewa nayi yana gaba ina binshi baya zuwa wurin da mota ya ke kafin mu karasa inda su ke yace kayan na nan sutura naki ne sai tsaraban mutanen gida kuma sai na zo idan naji sauki.
Nago, , , ban saki kimin godiya ba kaina nayiwa don yanzu hakkina ne na baki duk wani kula da kike so numfashi na sauke.
Don ya hanani magana ina isowa driver ya bude min mota muka na shiga shima ya shiga yaya Sani da driver a gaba.
Ko da muka isa ban dauki lokaci ba jirgin mu ya daga sai lagos shida da rabi muka sauka inda naga anty ce da kanta tazo dauka na sai faiza.
Da murna suka tare ni bayan an dauko kaya na muka muka nufi gida yaran basu gida sun fita da daddy sai fati ce kadai a kida.
Itama ba laifi ta tareni ba yabo ba fallasa don tun da tace in andawo bata sake fadin komai ba kamar bata san jiyan mahaifina naje ba.
Ban shiga da kayana ba na ware wanda nazo masu dashi da wanda ya bayar a kawo masu murna ta shigayi tana cewa .
Safiya keda kika je jiyan kika tsaya muna tsaraba haka mai yawa ta bude naman da aka soya na zabbi wanda kaunan mama ta soya muna shi yaji hadi ta fara ci.
Tace kai Safiya mai wanan naman idan da agarin yake ai kullun ina shagon shi ke kinji nama zau da dadi ta bude kayan miya taita murna ganin na hado masu kayan miya na garkajiya ta shiga yabawa kamar nakawo masu wani daula.
Tasa funke ta kwashe kayan zuwa kitchen don su faiza sun far ma naman da ci tace su bari hakana sai ta dibawa daddy na shi.
A dakina muna like da su yan biyu da suka mane min sai hira suke so in masu na kauyen mu, suna son hiran kauye sosai sai faman tambaya na suke yi ina basu amsa sai da daddy ya dawo ya kirasu.
Na fito cikin dogon riga sai hijjab dana saka a sama yar karama don bani zuwa gaida daddy hakana sai dai idan ya girshe ni a gidan ba hijjab a jikina kuma idan ya samay ni hakana bani iya sakewa dashi.
Yana gani na ya na cin naman dana zo kasu dashi anty na gefen shi zaune itama naman take ci yace a a amarya andawo.
Kunya ya kamani na soke kaina nace daddy mun samay ku lafiya yace lafiya Safiya yaya baban naki da jikin ?
Nace yaji sauki yace a gaishe ku ai mashi godiya a wurin ku sai yace ai ba komai Allah dai yaba shi lafiya.
Nace amin tare da mikewa daga tsugunnin da nayi har na juya zan wuce sai naji yace ashe sulaiman ya samu zuwa garin naku ?
Na juyo tare da dan dukar da kaina kasa saboda kunya ya sake cewa yanzu sai batun aure don bana son a dauki wani dogon lokaci ba a yi ba .
Bandai yi magana ba na juya na wuce zuwa dakina inda ma na rufo dakin don ina son in duba kayan da ya sawo min shake a troler.
Sai da nagama komai na jawo akwatin na buda idona ya fara tozali da wasu irin dogoyen riguna masu kyau da daukan ido .
Guda guda nake fitar wa saida na fitar da kala bakwai sai kuma wasu lace da aka dinka su kamar an gwadani guda ukku suma.
Ya tashi kala goma ko wani da gyalen shi da takalman shi ido na runtse tare da sauke ajiyan zuciya nace a fili Allaj miskara ziratin .
Yau ni safiya keda wanan kayan da sai a film ko a jikin wata data kai, nake ganin su yau ni safiya gani dasu a matsayin nawa ga wa yanda ya saya min kafin in tafi gida.
Na hada suka tashi sha biyar kenan nace wanan wani irin mutum ne da baya jin kyashin kashe kudin shi haka sai naji ina son kiran shi a wanan lokacin in dada mashi godiya.
Waya na mike na dauko bayan na mayar da kayan na kirashi ringing uku ya dauka yanayin shi kamar na mai barci.
Yaya jikin na yimashi yace yaji sauki yace kin sauka lafiya kin samay su lafiya ko ?
Nace suna lafiya sai dan shiru sai naji yayi murmushi nace dama dai na bugo inji yaya jikin naka yace ashe andamu dani ke nan da har za a kirani.
Murmushi nayi kamar yana gabana sai nace yallabai kuma wani hidima akaimin haka yace yes kin san yanzu matar sulaiman kike dole ne nayi maki ko kina son a ganni cikin sutura ne ke kuma azo a ganki haka ?
Nace to na gode kwarai sai naji ya kashe wayan murmushi nayi nace har kullun idan kai min alheri baki bazai gaji dama godiya ba don kacancanci hakan.
Gidan Ahmed dana zauna har nabar gidan ko kyale bai hada ni dashi ba banda tsaraban kanjamau dana samu koma wani hali yake yanzu oho ?
Muna gama wayan dashi ya tuna da cctv din da ke gidan ya jawo ya hada ya fara kallon barin mu gidan da yayi da yaya sani.
Don yaga fuskana na sai ko ya fara ganin badakal da muka yi da yaya din tun fitar shi har shigowan shi da shiga dakin shi da yayi ya bar mu.
Lumshe ido yayi yana jin wani iri a ranshi yanayin da yaji a lokacin da haka ya samay shi har yakwanta ciwo don bakin ciki gani yake a lokacin kamar zai mutu ne a take.
Kamar ba zai yi wanan rayuwan da yake yi ba yanzu har da fadawa vikin soyayyan yarinya karama da yake jin shaukin ta akoda yaushe.
Lumshe idon shi yayi yana jin wani irin yanayi a zuciyar shi a haka barci ya dauke shi da tunane barkatai a zuciyar shi.
Washe gari da ya tashi sallah yayi bai kara kwantawa ba yayi abinda zai yi ya fito yaya Sani ma ya fito yana falo zaune shi kadai.
Yana ganin ya fito yake ce mai ina kwana yaya ce yaya sani ashe ka tashi ya gaida yaya sani din nan suka zauna suna dan hira a kaina a wurin yaya sanin ne yaji labarina tsab ba ragi ko kari.
Yace in sha Allahu karku ji komai a kaina zaku samay ni da yiwa yar wanka a dalci sai dai idan wani abu ya fito daga gare ta.
Yaya Sani yaji dadi sosai har ya kasa boye farin cikin shi sun karya yace zai fita sai ya dawo akwai maganan da zasu yi da yaya sani din.
Ya kara da cewa idan yana son fita ya zaga gari yayi magana sai a fita dashi driver yana nan waje
Kwarai yaya sani yake jin dadin zama garin ko ba komai yaci mai kyau yasha mai kyau idan zai fita ga mota nan a fita dashi yana kallon gari
Gashi har yau sulaiman bai samu zama ba balle suyi maganan da yace zasuyi dashi shi kuma yana cikin fargaba don bai san maganan da zai mashi ba.
Ko yaushe muna waya da yaya sani din yana fada min daular da yake ciki a gidan na sulaiman din
Nakan yi mashi dari idan yace Safiya kin ko ga yadda na koma wani dan birni dani sati gudan man danayi a gidan ku.
Nakan ce kai yaya wai gidan gidan mu yana can kauye gidan sulaiman din dai sai yace gidan ku mana aini inna nake son tazo taga irin gidan da Allah ya nufa zaki zauna aciki.
Muga yadda zata yi ranan nasan bata da bakin magana nasha gayawa inna tun kina yarinya akan ta daina irin abinda take gwada maki don bata san abin da Allah zai mayar dake ba wata rana.
Amma sai inna tace min wai ni yaro ne bani sani komai ai yadda uwar ki take yar kauye basu da komai kuma diyan ta haka zaku taso baku da komai.
Yanzu gashi Allah ya gada masu shike da komai yayi ikon shi a kan ki wanda nasan har duniya ya nade gidan mu babu mai cin maki a ratuwan duniya.
Nace kai yaya banda sheri dai don kaga inna bata nan kai mata kaza fi yace safiya ke baki ganewa ne inna fa sam bata son kowa a gidan mu in ba mi diyan ta ba ni kuma wanan halin nata yana damu na sosai a raina.
Nakan yi mashi nasiha akan ya tuna fa inna uwa ce a gare shi sai yace ya sani shi dai halinta ne baya so sai nace sai hakkuri da iyayye yaya.