BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

* * *
Jinya yayi so sai duk ya ramay ya fita hayacin shi karshe ma sai da ya dawo gidan gwago akai jinyan shi.
Yanzu kowa yasan abinda ya samay shi don tun a karuwan shi aka san suna dauke da cutan an kaita gida ta mutu can.
Gwago kulun kuka takeyi tana fafin Ahmed baka kyauta min ba kasa na cuci diyar mutane gashi yanzu ni da garin mu amma ina kunya zuwa.
Don ko naje ban san da wani ido zan kalle su ba kasa na rabu da dan uwana mutumin arziki da sanin ya kamata.
Yarinyar nan tana da ma bidi amma don a raya zumunci ya rufe idon shi yace sai kai kuma akayi hakan.
Ahmed dake kwace saman wani tsohon katifa yace mummy kada ki bleming dina ni kadai a cikin maganan nan ai gaban ki nake dauko mata tun ina yaro na amma baki hanani ba.
Sai yanzu da abu ya baci muna ne zaki tsamay hannu ki ciki duk waja muna saboda fitinar ki baba ya bar garin nan .
Kin hana ya zauna kusa damu ya ga halin da muke ciki ya kwabe mu tun yana zuwa har ya daina zuwa yanzu ya tare a gurin sabuwar matar shi.
Tace abinda zaka fadamin ke nan ko bayan komai a kanka ne ya faru don yana ganin yarda nake sakar maka kudi yai magana nace ina ya fito.
Nan dai sukai ta sa insa da dan nata sai da sadiya ta shiga tsakanin su taja gwago din waje kar abin yai masu yawa gashi kwance ba moriya.
Zuwan yaya Saadune ya kaishi asibiti suka karbi magani har ya fara jin saukin jikin shi ya tatara ya koma gidan shi sai dai hakan bai sa yabar halin shi ba.
Yaya saadu yazo gida kamar yadda yai alkawari ya samu ana aikin gidan mu gadan gadan ya samu baba yaji sauki sosai har yana dan fita kasuwa.
Yai masu alheri ya dawo bai tsaya lagos ba don wurin matar shi dake shirin haihuwa ya wuce direct sai da ya isa ya kirani washe gari da karfe hudu.
Ban daki na bar wayan na caji sai da na shigo ne na samu miscall din shi a nan nan nai mai kira biyu bai dauka ba ga na uku matar shi ta dauka tana cewa bai nan ne.
Nace madam yaya kike yaya tsufa ta amsa min da murmushi da lafiya tace ke haka akeyi baki lekomu ba kuma kina lagos.
Nace kada ki damu idan kin haihu zan shigo sai nayi maki one week zan koma tace kamar da gaske nace bari ki gani ko yanzu shiga daki ki haihubin banzo ba .
Ta kwashe da dariya tace to Allah ya kaimu lafiya idan ya dawo zan fada mashi kin kira baki samay shi ba.
Mukai sallama na kashe wayan na koma har kokina sai dai ban faye fita irin da ba don gidan in ba anty ke nan ba kamar suna shan kanshi.
Shiya sa ban damu da shiga harkan kowa ba a cikin su sai dai ina tunanen Ita Faiza idan fati na fushi dani ne akan dalilinta na son sulaiman .
To ita akan may take fushinta dani ni dai ban san nayi mata wani abu ba kafin in wuce gida.
Abinda ban sani ba ashe baya na ashe sunyi meeting a kaina kan nazo na samay su a gida anty ta fifitani a kan su .
Bata kallon kowa da gashi a gidan sai ni su tun yaushe suke ba a nema masu miji ba sai ni da zuwa don nazo da sihirin mu na yan kauye sai ace nice ake kokarin zuwa dani wuri.
Sai suka yanke shawaran su hade mi kai ta yadda in na dawo zan rasa gane kan su sai na raina kaina a cikin su.
Wanan dalilin yasa ban gane ma kan su sai waccan tabi can wanan tabi nan sai su watse su barni ni kuma dana ga hakan sai nima na fara share su kawai.
Gashi yanzu na dawo sai shige da fita nake yi na doke sanin su sai suka shiga gulma wai kila ba gida naje ba mun hada baki ne da anty ta turani wurin maza na samo kudi.
Tun sunayin zancen a boye har na tsura su sunayi nan nai masu tas sai suka shiga rokona wai inyi masu hakuri kada anty taji nasan korar su zatayi a gidan.
Nace amma idan na karajin wani abu makamancin haka zan fada mata dan ta dauka min mataki akansu.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,

????????4️⃣5️⃣????????

YAR UWA KI TUNA NOVEL NA KUDI NE DON DARAJAN ANNABI KADA KI FITAR MIN DA NOVEL WAJE KE KUMA IDAN AN FITAR KIKA KARANTA BAKI BIYA HAKKINA A KAN KI, , , , , , ,

Bayan anty ta fita wurin aiki ita da yara na gama abinda zan iya taya funke na fannin aiki sai na koma daki na kwanta abina.
Can barci ya soma dauka na sai naji anturo kofan dakin alaman mutum ya shigo haka yasa na bude idona don ganin ko waye ya shigo din.
Faiza ce fuskanta dauke da murmushi tace ba dai kin kwanta ba ne nace na kwanta eh barci nake son in dan yi na wani lokaci.
Zama naga tayi a bakin gadona abinda ta dade batai min ba sai gashi yau tazo tana yi don haka nasan da wani manufa tazo.
Magana muke yi amma sai bin dakin nawa take yi da kallo kamar mai son ganin wani abu tace gida fa ya karbe ki safiya.
Kin ga yadda kika sauya gaba daya kamar bake ba sai nayi murmushi nace kin san gida dadi gare shi ai.
Tace sai kuma naji wani labari a bakin anty da nai mamakin jin shi wai Sulaiman zaki aura ba da dadewa ba ?
Faiza ke nan idan haka ne ai gida guda muke dake da a bakina zaki ji labari sai tace gaskiya kan ai na dauka da gaskiya ne sai in ce halan baki san abinda ke damuwan shi ba.
Da sauri nace may fa ?
Sai tai shiru tace kardai aji a bakina fadi ba a tambayeka.
Nace ai ya kamata na sani don kariya sai tace dama ji nayi ana fadin kila yana da cutane a jikin shi shiyasa bai son ai maganan aure dashi.
Haka naji a gida suna fada shiyasa nace barin fada maki don ki sani kada matar gidan nan ta cuta maki don kudi.
Baki ganin yadda take nan nan dashi ta kwace ma kowa shi idan ba itaba babu wanda yake shiri dashi a cikin yan uwan mu kaf.
Ita kadai ya yarda da ita yake mu,amula da ita itama din nasan don kudin shi ne take hurda dashi fiye da kowa.
Mamaki ya hana ince mata komai sai sauraren ta da nake yi rashin magana na baisa ta fasa magana ba.
Taci gaba da fadin kin gashi nan haka yake kamar bakin bature komai nashi a ka,idance yake yin shi.
Idan bai so ba sai ya nuna kamar bai sanka ba , babu dan uwan dake jin dadinsa sai wanda yaso.
Haka shima bai kula kowa yana takama da kudi a cikin dangin idan kinga gidan da ya kera a bauchi sai kin kama baki.
Babu kowa a ciki sai mahaifiyar shi da kaunar shi dake bangare guda amma duk girman gidan nan part din shi a rufe yake bai sa kowa a ciki ba.
Ni ina ma mamakin yadda idan na gaidashi anan yake amsa min a sake don a gida baka ko ganin shi balle ma ku gaisa dashi.
Nace aiko wanan halin bai kamance shi ba sai ka ganshi kamar babu ruwan sa ashe haka yake ?
Ta mike ta na cewa barin koma dama shiya kawo ni in fada maki in baki sani ba kada ai maki rifa rufa saboda kudi.
Nace amma ni sai banga wani kudin da zai rudi anty dashi ba don ko mijin ta ma yana dashi itama ba a zaune take ba.
Sai tace Safiya kenan.
Wa yaki kudi ko wa yaki kari a rayuwa balle ma ita ai ba abinda take so kamar kudi ta fadi tana kara nufar kofan fita daga daki sai ta juyo tace amma fa maganan nan ya tsaya dagani sai ke.
Nan ta fita ta barni da tunane fan a raina duk kokarin da boyar Allah nan take muna amma suna fakewa a bayanta suna zagin ta.
Nan dai nayi ta tunane kala kala har nagaji barci ya kwashe sai dai a cikin tunanen nawa ba abinda nake tunawa kamar abinda ta fada gamay da sulaiman din.
Sai kuma abin ya tsaya mun a raina nace kardai zan kara tsundumawa ne ga auren ukuba a rayuwa nace ni kuma haka rayuwa tazo min a bahaggon rayuwa komai zan gani sai akasin sa.
Karan wayan ummi na ne ya tayar dani daga barci na mika hannu na jawo wayan dake caji don na samata ringing din mamana mamana mai share hawayena.
Na yi sallama ta karba nan muka shiga gaisawa ina tambayan mutanen gida tana bani amsa da suna lafiya.
Tace yar nan shi kuma wanan bawan Allahn haka yasama kan shi lalura akan mu nace ummi wake nan fa ?
Tace mai neman ki mana ya turo yayan ki sani da abin arziki doya sai da aka shake bayan mota da shi da manja muna murna.
Ashe magana bai kare ba sai ga sani yace wai ya turo shi a rushe gidan mu a gyara a cikin wata daya anya yar nan kinyi bincike a kan sa kuwa.
Kwance nake bansan lokacin dana mike zaune ba nace ummi a rushe gidan mu fa kikace ?
Ta au ke baki ma sani ba ke nan ai yanzu duk bamu gidan kowa na gidan su sai inna ku ce a family house yan uwanta sunki yarda ta zauna masu a gida don sanin halinta.
Assha baiyi kyau ba tace halinta ya ja mata koda akazo da zancen gyaran gidan ai sai da tai halin nata mama ku ne kawai tai ta samaku albarka kedashi.
Taki kwashe kayan ta sai da mutane suka taru a kanta tonon asiri zallah abin ba dadin ji wallahi nace Allah ya kyauta.
Amma ummi ni abin ya bani maki don ko yau da safe mun gaisa dashi amma bai sanar dani zancen ba.
Watau yana son ya bani mamaki ko kuma baison godiya kamar yadda yace bai son yayi alheri a tsaya ana mashi godiya.
Sai naji ummi tace ikon Allah shine kyauta sahihi wanda ake so Allah zai saka ma mutum da alheri.
Nisawa nayi nace ummi nifa yanzu har tsoro nake ji bakiga kayan da ya saya min ba da zan dawo har akwati guda shake da kaya.
Ummi tace ikon Allah shi bai gajiya ne ?
Na amsa mata da kuma bai son godiya.
Tace Allah ya kyauta kuma ya saka da alheri ni abinda na fahinta shine bai son azo daurin aure a raina ma inda ya dauko mata ne shiyasa yace ai gyara a cikin wata guda kacal.
Nace ummi ai kowa yasan ni yar tallakane tun da ubana ba kowa bane da aka sani tace Allah ya sanmu ai nace shi kan.
Mun dade muna magana da ummi a waya har ta bani gwago buka gaisa nayi masu godiya tace akan may ai nan gidane ga ummi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button