BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,
????????4️⃣9️⃣????????
NOVEL DINA NA KUDINE IDAN KI FITAR MIN BAN YAFE BA IDAN AN FITAR KI KA KARANTA INA BINKI HAKKINA A KAN KI.
Ina kwance saman gadona da waya a hannu na na mayar da hankalina sosai a kan wayan ina duban sako naji an shigo dakin.
Na dago don ganin ko wacece sai Fati na ganj tsaye a kaina tana huci idanuwan ta sun kada sunyi jawur dasu aje wayan nayi a gefe na duk da ban karasa karanta sokon ba.
Ta harde hannayen ta saman kirjinta ta wurga min kallo mai tattare da tsana zallah a cikin shi ta fara tafa hannu ta biyu tamai kara bina da wani irin kallo na tsana.
Zama nayi da kyau ina fuskanta ta don inji abinda take shirin fadi lalai Safiya kin cika rikkan yar yaudara kin kai maciyiya amana.
Ke yanzu bakiji kunya ba don Allah to ki sani in takaman ki iya asiri da kwatar maza yau kin kai karshe don baki da wayau yanzu ina ke ina uncle ko a kafa akadaura mashi ke ai ba zai iya ja ba.
Sai lokacin nayi murmushi nace da ita balle a daurin da akewa ko wace mace da mijin ta za ai muna kuma na dauke shi kamar yadda ko wata mace take dauke mijin ta.
Hannu ta daga wai ta kai min mari kafin hannun ta ya iso gare ni na kwashe ta da mari biyu masu kyau nace kin zo har dakina ki fada min abin da yai maki dadi ki wuce kice kinci bulus.
To bari kiji uncle kamar na aure shi na gama da yardan Allah ke ce wahalala da faman dakon son wanda bai masan dake ba a duniya.
Ashe Faiza na jin mu ita ta kira anty sukazo tare daidai Fati na fadin aure fa kikace kodai karuwanci waye baisan abinda ake turaki yi wurin shi ba banza kawai ana turaki gurin shi kina samo kudi don zubar da kai dama zubun ki baiyi kama da ta mutanen kwarai ba.
Muryan anty ne ya karade dakin tana cewa wake turata karuwancin nike nan kike nufi kowa fati ?
Da sauri muka juya kofan ta karasa shigowa ita da Faiza dakin tana cewa Fati nace uban wa ke turata karuwanci tambayan ki nake yi ki fada min ?
Nace anty wanan maganan da take fada min kullun ya isheni don ba yau ne farko fada min haka da takeyi ba wai kina turani wurin maza ina samo maki kudi.
Ko zuwa gida da nayi jiyar baba sai da ta fada min ha gashi kuma yau ta sake fadin wai kin turani kalaba na samo maki kudi wurin maza dama haka kike yi.
Inna lillahi anty ke nanatawa a gigice tana kallon Fati din takeyi rai bace tace kazafin da zakiyi min ke nan Fati sakkaiyan da zaki mayar min ke nan ?
Na dauko ki cikin wahala da lalace nazo dake nan don ki zama mutum ki dogara da kanki shine zaki saka min da wanan a gidana.
Tace da kike fada a kan sulaiman ya ko san da zaman maki a duniyan nan halin ki na banza ya barki ki aikata alheri ne ne fati ?
Karshe kasa karasa magana tayi nasan takaici ya rufe ta sai juyawa tayi ta fice daga dakin rai bace.
Muka dawo da kallon mu ga juna sai gata ta juyo tace ki fice daga dakin nan tun raina bai karkare baci ba Fati.
Ta kalle ni taiyi kwafa tana cewa kin ci bashin marin da kikai min don sai na rama abina ki sani nace daga baya ke nan na nuna maki ni yar kauyen gidi ne.
Ta fice fuuu anty ta mara mata baya suka fice aka barni da gani sai Faiza tace don Allah Safiya ki boye ni kada ki fadawa anty anbin da nace hannu na daga mata nace Faiza ki fice please.
Batayi musu ba ta juya ta fita daga dakin simi simi na sauke a jiyan zuciya tare da komawa saman gado na zauna ina tunane ni may ye laifina a cikin maganan da bazata samay shi da maganan ba shi da take so.
Na dade wurin zaune na rasa amsan da zan ba kaina dole nake kwance ina ci gaba da tunane a raina sai da naji yunwa na iya fitowa don neman abinda zanci don ko karyawa banyi ba ta samayni da magana.
A falo na ga Faiza zaune wuce ta nayi zuwa kitchen batare da nayi mata magana ba na hado abinda zanci na dawo zan shige sai naji tace Safiya fushi kike yi hardani ne wai ?
Nace fushi akan may aini Allah yayi min fada akan may zan tsaya bata lokacina kuma aida ban gode masa ba.
A gaban anty ta nanata da kunnen ta taji ai hali shike nuna kansa wanan ya nuna bata da alhakin ku kuke fakewa a bayan ta kuna mata sheri har na gama na wuce bata ce dani komai ba.
Ban iya cin abincin ba don raina ya na bace har lokacin twin’s na ta shigo tana ce dani maman su na kirana abinda ya sani fitowa kenan.
A falo take zaune ga Fati da Faiza a zaune suma na samu wuri na zauna in ji abinda zata ce muna.
Mun zauna shiru sai can ta nisa tace Faiza ta amsa naam Safiya nima na amsa mata da naam Fati ta amsa mata ciki ciki da naam.
Tace na koraku nan ne don in yi magana da ku baki dayan ku akan abinda ya faru dazun tsakanin Fati da Safiya a gidan nan.
Banyi mamakin jin abinda kika fada ba don nasha jin ire iren wa yan nan maganganu daga bakunan mutane dake fitowa daga bakin ku.
Amma wanan yafi min munin saurare don da kunuwa na naji ba wani ya fada min ba sai fatin tace ni may na fada anty maganan mu mukeyi kawai.
Kina rufe min bakin kin ki ko sai ranki ya baci yanzu in maki tsinanen duka anan sai ta ja bakin ta tayi shiru tare da dukar da kanta kasa tace idan da banji ba sai ince kaka tayi maki.
Ba wani ya fada min ba ni naji da kunne na abinda kika fada kenan ni ke tura ta wirin maza tana samo min kudi kike nufi.
Ta dago za tai magana ta tare ta da tsawata yana fidin tayi shiru dole ta sake kyalewa tai fada sosai a cikin bacin rai sai ta juya kan Faiza tana cewa.
Aure Safiya zatayi nan da dan wani lokaci zan iyacewa nan da dan lokaci mai zuwa bazaku ce baku san da zancen ba.
Don haka zan iya hakkurewa har lokacin da tayi aure wace taga zata iya zama dani ta zauna bazan kori kowa daga cikin ku ba don ku kuka kawo kan ku na.
Sai dai idan na sake jin wani rikici a tsakanin ku kafin wanan lokacin dukkan ku rayukan ku zai baci dani amma ke fati tun yanzu nasan matakin da zan dauka a kanki.
Gida zaki koma don ba zan yarda ki bata min suna a banza ba da abinda banji ban gani ba ki dora a kaina duk wanda yaji wanan zancen sai yace idan baki gani ba baki fadi.
To komawar ki gida shi yafi zama alheri a gare ni don haka sai ki shirya next week zan sa a kai ki gida kafin in zo muyi maganan a can.
Hakkuri ta shiga bayarwa sai ta bani tausayi ban san lokacin da nace don Allah anty kiyi hakkuri.
Ta dago kai ta kalle sai na saukar da kaina a kasa na kara fadin don Allah anty kiyi hakkuri sherin shedan ne .
Kina ji da bakin ki abinda ta fada akaina kuma kince ba yau ta fara fada maki haka ba sai fati tau sarin cewa wallahi bani na fada ba Faiza ce ta far fadi nima naji na fada.
A take Faiza tace kada kimin sheri yaushe na fada ta juya gare tana cewa wai Safiya ranan wa kiji ya fada har muka baki hakkuri akan karki bari anty taji zancen.
Murmushi nayi nace anty don Allah kiyi hakkuri da zancen in ma har suna hasashen haka ne a ransu ai Allah shiyasan gaskiya.
Haba haba kuyi min adalci mana maye laifina na ajeku a gida na danayi tare dani ?
Idan bani ba wacece zata ajeku haka a gidanta amma tunda ku kuka kawo kanku gareni na karbe ku hannu bibiyu na zauna daku may na rage ku dashi a gidan nan na jin dadin rayuwa.
Duk mukai shiru muna sauraren ta tace ke Faiza ai akwai gidan anty Ai a abuja may yasa baki je can kin zauna ke kuma akwai gidan anty mami a kaduna ai uwarku daya may yasa baki tafi wurin ta ba.
Sai nan bayan haka da halina ne hakan da ku da kuka riga Safiya zuwa nan aida daku zan fara ba Safiya da tazo daga baya ba.
Ko don ita din ta fiku kyau kuke tsamanin haka zanyi da ita toni aure na hada don raya sunnan ma,iaki SAW ba yin zina ba yadda kuke tsanmani.
Allah ne ya yanke mata wahala da zuwanta ta samu miji ku da kuka dade da zuwa aida aikinane hakan akwai maza da yawa may zai sa ban hada ku dasu ba ku samo min kudin ko ku ba mata bane yan uwanta.
Faiza tace munyi kuskure amma kiyi hakkuri ba a karawa in Allah ya yarda ta ja tsaki tare da kawar da kanta gefe.
Nan muka zauna zugun zugun damu ita dai bata sake magana ba sai duban tv da takeyi tana sauke ajiyan zuciya kawai.
Nice na fara mikewa na bar falon zuwa daki ban san lokacin da sauran suka watse ba tun wanan ranan aka rage yawan gulma a gidan.
Sai dai ban yarda na sake wa Faiza dake yawan shige min ba wai ita ala dole tana tsara yadda zamuyi buki in ya taso.
Na fito daki da safe na samu anty a falo don yau ba ranan fitanta aiki bane don haka mukan wuni da ita a gida bata fita ko ina a wanan ranan ne takanyi gyaran jikin ta.
Sai yanzi na gane hakan da nake zaune a gidan ta ina fitowa tare da gaida ita tace yauwa Safiya kin fito don Allah ki taimaka min da kan nan nawa.
Yau kitso nake so da gyaran jiki tace yan biyu ta dauko mata kayan kitson su nan na zauna muka fara banyan kai muna hira sai ga Faiza ta fito zauna nan take fada mata ai kan yayi dauda nan dai mukai ta mahara karshe dai tace zataje wankin kan.
Wayana dage gefena ne yayi kara alaman sako ya shigo min a lokacin ban dauka ba sai anty ta lura dani take cewa in diba mana ko soko ne mai muhinmanci.
Ga abinda na gani rubuce ga sakon.
Safiya badon na isa ba sai don girman Allah Safiya ki taimaka ki kashe min wutan kaunan ki dake famar kunar zuciyata har kullun, Safiya ina sonki ina kaunar ki wallahi wallahi ina son ki tsakani da Allah, Auren ki nake so don auren ki alheri ne a gareni.
Ki taimaka ki kirani a wayan ki inji muryan ki don in samu natsuwar gudanar da ayyukan dake gaba anan idan kina raayina ki kirani inji muryan ki Sulaman Habbi Bauchi.
A hankali na runtse idona bayan karanta sakon ina sauke ajiyan zuciya sai kuma gabana ya fara bugawa a hankali kamar zai tsage min.
Ganin sakon na rinkayi kamar a mafarki na shiga tambayan kaina may ya kawo wanan sakon haka har uncle ya tsaya ya rubuto min shi.
Na sake tambayan kaina may ke faruwa ne wai muryan anty naji tana cewa dani kin gama karanta sakon ki sance ma su yan biyu nasu muje a wanke muna.
Cikin dauriya na amsa mata da eh sai dai saukina kitson kan su ba wani mai yawa bane ina gamawa na shige daki don ban da kwanciyar hankali a tare dani a lokacin.